Sashe 158
LUu Luu Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sannu kawai nanay ke jera mata,kamar ta sauke ciwon daga kanta ta dawo dashi mata jikin. Ta kasa tantance cikin biyun wanne zatayi?. Jimamin wahalar da akhnan din tasha yanzu?,ko kuma murnar qara samun tabbatuwar zarginta?. Tana hango fuskar motii ne kawai,yadda zaiji da wannan albishir din. Tanaso ta zama ta farko da zata fara gaya masa wannan kafin kowa ya fadi masa.
Idanunta akan haisam,yadda hankalinsa ke a jagule sanda rumaisa ta kawo roba yana gyarawa akhnan jikinta.
Matsowa saamee tayi,cikin wannan kulawar da qarqashinta abubuwa ne masu yawa tana miqa hannu zata karba robar da aka kawowa haisam din.
"Bari na qarasa mata obbo....kaje ka gyara jikinka". Sau daya tak! Ya daga kai ya aje mata wani irin kallo,take taji dukka 'ya'yan hanjinta sun girgiza. Ta rufawa kanta asiri a hankali ta taka tana ja baya ta basu sararin gurin.
Tas ya gyara mata jikinta,ya zare tasa cloak throbe din da ita kadai ta baci ya miqawa rumaisa dukka ya tattara ta fita dasu don bawa hadimai su gyara.
Shi ya riqeta da kyau sanda take maida numfashi suna sauka zuwa parlor suna barin dining area din da tuni bayi sun fara aikin tsaftaceshi.
Nanay na biye dasu,banda jera mata sannu ba abinda takeyi,har ya zaunar da ita saman sofa,ya tsaya daga gefanta yana ware hannun jubah dinsa daya nade a dazun.
"Wata nawa ne?" Nanay dake zaune dab da akhnan din ta fada bayan ta gama qarewa faratanta da tafin hannunta kallo.
Dif sukayi ita da haisam din,sai kuma ya juya a hankali yana duban akhnan din. Itama shi take kalla,don bata fahimci komai a maganan nanay ba.
Kamar ta tamabayeta,sai kuma haka kawai taji nauyin tambayar nanay din me take tambaya?.
"La'ilaha ilallahu muhammadurrasulillahi.....muhammad nace wata nawa ne?,kada dai kacemin bakasan komai akai ba ballantana watanninsa?,yawo kawai kuka dinga yi baka kaita an duba lafiyarta ba?" Nanay ta fada tana tafa hannu sannan ta kama haba idanunta akan haisam din da yayi tsaye ya rasa ma daga inda zai debowa nanay bayanin. Kunyarta da nauyin ta kuma suna sake danneshi,uwa uba kuma shi baisan me yadda akhnan din kanta zata fahimta ba.
Idanun nasa ya janye a hankali,ya sake maidawa ga akhnan yana jin wani nauyi yana sake nutsar dashi yana jin nanay naci gaba da mita.
"Nace wata nawa ne muhammad?" Ta sake tambayarsa. Kamar ayau an cire mata duk wani shamaki tsakaninta dashi.
"Banda sakalci,ka sakata a gaba kuna yawonku abinku,baka damu da sanin lafiyarta ba?. In banda zamani ina ake haka?"
Wannan karon
dariya ce ta kusa kubucewa daga bakin haisam,saboda gaba daya wadda ake maganar a kanta ma tana zaune tana kallonsu cikin mamaki,kamar ba a kanta ita ake magana ba.
Akhnan ta waiga daga nanay zuwa Haisam,sai kuma ta saukar da kanta qasa tunaninta yana kullewa.
"Zan sake tambayarka a karo na qarshe" Ta fada fuskarta na nuna serious.
Yanzu kam dariyar gaba daya ta mutu a fuskar haisam. Ya zauna sosai cikin kujera.
Kamar dalibin da malaminsa ya tsare.
"Ban sani ba.....Allah ban sani ba nanay" Yayi maganar yana lumshe idanunsa gami da budesu lokaci guda.
Tunda yake bai taba ganin abinda nanay ta yiwa serious haka ba. Fada takeyi da gaske,har sai daya koma a hankali ya zauna.
"Nanay" Ya kira sunanta a tausahe. Harara ta balla masa.
"Me?" Kaman zaiyi dariya amma ya danne,zaiso yaga yadda zata ganar da akhnan abinda yake tare da ita.
"Ba laifi na bane...."
"To na waye?" Ta tari numfashinsa hannunta cikin na akhnan din. Ya zare hannunsa daga kan hannuwansu dake harde,ta riqeta sosai kamar wanda ya yiwa akhnan din wani mummunan abu.
"Itace...."
"Ni?" Akhnan ta tambaya cike da mamaki tana fidda idanu. Me tayi yau haka da haisam ya zabi bayyana laifinta da kuskurenta qarara?. Kaman ba shine ke bata kariya a dukkan muhalli ko gurbi ba?.
"Eh ke..taqi yarda.....taqi fahimtar abinda ke faruwa da jikinta". Idanu sosai akhnan ta sake fiddawa,kafin kuma a hankali su koma daidai saboda ruwan hawayen da suka tara na karyewar zuciya.
Shuru ya ratsa dakin,kowa da abinda yake kai kawo cikin ransa.
A hankali nanay ta sauke kallonta kan akhnan. Ba mamaki bane.....kowacce mace takan tafka nata kalan shirmen da quruciyar yayin cikin fari. Wani abune da kusan yake shammatar kowacce mace,don haka nata kalan shirmen cikin fari kenan. Yadda tayi tsuru tsuru kama me laifi ya sanya nanay kusan sakin murmushi,amma saita maze,ta maida dubanta ga haisam.
"Bamu guri.....zamuyi magana" Tsam ya miqe ba tare daya musa ba. Hakan ya masa,qilan tunda nanay ce ta tsaya ta saurara ta kuma fahimta. Shima ta rage masa aiki,amma yadda yasan ta koyi rikici da rigima a kwanakin nan tabbas yau saidai ya shiryawa tarar kowanne rikici nata.
Yana sanya qafarsa waje ya tuna abinda saamee tayi dazu,take dan annurin fuskarsa ya bace,ya kuma sauya akalarsa daga sitting room da yayi niyyar zama ya jirasu,ya nufi hanyar dakunan baccinsu.
Da farko sanda saqon kiran ya iski saame ta tsorata,ta fara hasashen girman laifin abinda tayi da hukuncinta. Sanannen abu ba,ba wanda zai taso cikin gidan yace baya gane umarni daga gurin yarima haisam,da idanu kawai ba tare da aiki ko magana ba. Ya mata maganan.....amma son gane komai ya sanyata batayi aiki da ita ba,wanda wannan kawai laifi ne me zaman kansa.
To amma a hankali sai taji tsoron yana gushewa sanda aka gaya mata shi daya ne,a wani qaramin guri da sukan zauna susha iska.
Samun kanta tayi da matsawa ta qara turare,ta sauya hijabin jikinta da mayafi yalwatacce. Ko ba komai.....koda fada zaiyi mata,zataso ya ganta da kyawun nan nata.
Duk wani confidence data dauko ya kwaranye sanda ta soma hangen bayansa. Yana tsaye ya bada baya,amma gaba daya kwarjininsa ya cika gurin,kamar yadda qamshinsa ke sauya yanayin gurin da wani irin yanayi me dadin gaske.
Ta qarasa bayansa ta tsaya tana sallama kanta a qasa. Kamar baiji ba,sai daya dauki wasu sakanni sannan ya amsa qasa qasa,ya taka ba tare daya waiwayo ba ya isa ga wata kujera dake gabansa kadan ya zauna.
Idanunsa ya sauke a kanta a hankali. Karon farko yana jin haushin sonshi da takeyi gaba daya. Besan me yasa ta gaza ganewa ba,baisan me yasa bata fahimci yafi son ya farauci zuciyar da ba ita ta kawo kanta ba.
"Saamee" Ya kirata,sunan da muryar suka tsarga mata.
"Na'am"
"Kinsan hukuncin watsar da umarnin cikin gidan nan....." Ya fada kai tsaye kaman me bata amsar tambayarta bame tambaya ba.
"B....ban..." Ta fara yunqurin yin magana.
"Banyi tunanin....." Ta sake yunqurin fada amma sai ta kasa qarasawa sanda ta tuna ba'ayi masa qarya.
"To ki fara tunani daga yau" Ya furta da wannan nutsuwar tasa da kwarjinin nan dake bugarta.
Tadan daga kanta sannan ta sauke,ta san muryar nan. Muryar da haisam ke amfani da ita idan haqurinsa ya qare.
"Akwai abu daya da nakeso ki fahimta" Ya fada yana dakatawa.
"Kin taso a gidan nan."
"Nanay ta raina ki."
"An ba ki mutunci." Sai ya tsaya.
"Kuma saboda mutuncin nan ne nake magana da ke cikin girmamawa." Zuciyarta taji ta buga da kalmar girmamawar daya ambata. Amma kalmar da ta biyo baya...ita ce ta karya duk wani fata da ya rage mata.
"Daga yau." Ya fada a sarari.
"Idan ni da matata muna wani wuri..."
"Ki bamu guri"
"Me yake nufi?" Ta tambayi kanta da wani irin nauyi da tashin hankali daya saukar mata. Kaman yasan abinda take tambayar kanta din yace.
"Ina nufin....duk inda muka zauna,kibar wajen". Idanunta ta lumshe tana jin tashin hankali. Ta fahimci abinda yakeyi,yana rufe qofa ne. Don wajibi ne dole ne akan kowa cikin masarautar biyayya ga umarninsa muddin yana son ci gaba da zama. Ya rufe ya kulle mata duka sauran wata qofa da take da fata a kanta.
"Kada ki sake shiga tsakanin zamanmu.....kada ki sake kawo wani abu a zamanmu.....kada ki kula da komai daya shafemu a irin wannan zaman...musamman ita,ni zan kula da ita"
Hawaye ne suka zubowa saamee masu wani irin dumi. Ba saboda an yi mata ihu ba. Ba saboda an wulaqanta ta ba. A'ah....saboda ta fahimci saqon sosai sama da yadda take tunanin ma zata fahimta din.
Ya koreta ta ruwan sanyi daga gurin da take da fata,ya koreta daga rayuwar gidan gaba daya a fakaice.
Sai Haisam ya qarasa da kalma daya cikin nutsuwa. Amma mai nauyin da ya isa ya rufe kowace qofa.💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 145*
"Ki girmama iyakar da ke tsakanin ki da matata."
"Saboda ba zan sake maimaita wannan maganar ba."
"In sha Allah" Ta fada muryarta tana rawa,sannan ta juya cikin tashin hankali tana komawa ciki.
A wannan karon ta fara zargin kanta. Ta yaya ta bari idanunta suka kulle har take neman zubdawa kanta mutunci da kimarta na diya mace?. Anya wannan hanyar zata bulle mata kuwa?,anya ba zata koma da baya ta maida akalar hankalinta da tunaninta inda ake nemanta ido rufe da dukkan qauna ba?.
(Nidai nace oho....nacin soyayya dai bana diya mace bane wadda tasan ciwon kanta).
*A K H N A N*
"Ciki?...nanay ni?" Ta fada da wani tsoro a muryarta tana fidda idanunta waje tana nuna kanta da yatsanta.
Murmushi me qarfi ya qwacewa nanay,ta danyi qasa da kanta tana karantar tsoron cikin sosai daga idanunta. Sake matsowa kusa da ita tayi ta kuma sake kamo hannayenta tana karantar yadda take buqatar a nutsar mata da zuciya da bayanin da zata gamsu.
"Eh....ke din".
"Amma nanay.....banji ciwo ba" Tayi maganan da yanayin dake nuna sakalcinta a fili.
"Duk wanda yake da ciki sai yaji wani ciwo ne na daban?....sannan baki lura da yadda kikejin gajiya ba.....zaben abinci?,rashin son wani qamshi ko wari da sauransu?,duka wannan ba ciwo bane?" Nanay tayi maganan tana duban tsakiyar qwayar idanunta. Shuru akhnan din tayi,wani irin shuru da ya nuna zurfin nazarinta sosai.
Murmushi nanay tayi,ta miqa hannu ta shafi gefan fuskar akhnan din a nutse.
"Nima na taba zama sabuwar amarya"
Idanunta akan haisam,yadda hankalinsa ke a jagule sanda rumaisa ta kawo roba yana gyarawa akhnan jikinta.
Matsowa saamee tayi,cikin wannan kulawar da qarqashinta abubuwa ne masu yawa tana miqa hannu zata karba robar da aka kawowa haisam din.
"Bari na qarasa mata obbo....kaje ka gyara jikinka". Sau daya tak! Ya daga kai ya aje mata wani irin kallo,take taji dukka 'ya'yan hanjinta sun girgiza. Ta rufawa kanta asiri a hankali ta taka tana ja baya ta basu sararin gurin.
Tas ya gyara mata jikinta,ya zare tasa cloak throbe din da ita kadai ta baci ya miqawa rumaisa dukka ya tattara ta fita dasu don bawa hadimai su gyara.
Shi ya riqeta da kyau sanda take maida numfashi suna sauka zuwa parlor suna barin dining area din da tuni bayi sun fara aikin tsaftaceshi.
Nanay na biye dasu,banda jera mata sannu ba abinda takeyi,har ya zaunar da ita saman sofa,ya tsaya daga gefanta yana ware hannun jubah dinsa daya nade a dazun.
"Wata nawa ne?" Nanay dake zaune dab da akhnan din ta fada bayan ta gama qarewa faratanta da tafin hannunta kallo.
Dif sukayi ita da haisam din,sai kuma ya juya a hankali yana duban akhnan din. Itama shi take kalla,don bata fahimci komai a maganan nanay ba.
Kamar ta tamabayeta,sai kuma haka kawai taji nauyin tambayar nanay din me take tambaya?.
"La'ilaha ilallahu muhammadurrasulillahi.....muhammad nace wata nawa ne?,kada dai kacemin bakasan komai akai ba ballantana watanninsa?,yawo kawai kuka dinga yi baka kaita an duba lafiyarta ba?" Nanay ta fada tana tafa hannu sannan ta kama haba idanunta akan haisam din da yayi tsaye ya rasa ma daga inda zai debowa nanay bayanin. Kunyarta da nauyin ta kuma suna sake danneshi,uwa uba kuma shi baisan me yadda akhnan din kanta zata fahimta ba.
Idanun nasa ya janye a hankali,ya sake maidawa ga akhnan yana jin wani nauyi yana sake nutsar dashi yana jin nanay naci gaba da mita.
"Nace wata nawa ne muhammad?" Ta sake tambayarsa. Kamar ayau an cire mata duk wani shamaki tsakaninta dashi.
"Banda sakalci,ka sakata a gaba kuna yawonku abinku,baka damu da sanin lafiyarta ba?. In banda zamani ina ake haka?"
Wannan karon
dariya ce ta kusa kubucewa daga bakin haisam,saboda gaba daya wadda ake maganar a kanta ma tana zaune tana kallonsu cikin mamaki,kamar ba a kanta ita ake magana ba.
Akhnan ta waiga daga nanay zuwa Haisam,sai kuma ta saukar da kanta qasa tunaninta yana kullewa.
"Zan sake tambayarka a karo na qarshe" Ta fada fuskarta na nuna serious.
Yanzu kam dariyar gaba daya ta mutu a fuskar haisam. Ya zauna sosai cikin kujera.
Kamar dalibin da malaminsa ya tsare.
"Ban sani ba.....Allah ban sani ba nanay" Yayi maganar yana lumshe idanunsa gami da budesu lokaci guda.
Tunda yake bai taba ganin abinda nanay ta yiwa serious haka ba. Fada takeyi da gaske,har sai daya koma a hankali ya zauna.
"Nanay" Ya kira sunanta a tausahe. Harara ta balla masa.
"Me?" Kaman zaiyi dariya amma ya danne,zaiso yaga yadda zata ganar da akhnan abinda yake tare da ita.
"Ba laifi na bane...."
"To na waye?" Ta tari numfashinsa hannunta cikin na akhnan din. Ya zare hannunsa daga kan hannuwansu dake harde,ta riqeta sosai kamar wanda ya yiwa akhnan din wani mummunan abu.
"Itace...."
"Ni?" Akhnan ta tambaya cike da mamaki tana fidda idanu. Me tayi yau haka da haisam ya zabi bayyana laifinta da kuskurenta qarara?. Kaman ba shine ke bata kariya a dukkan muhalli ko gurbi ba?.
"Eh ke..taqi yarda.....taqi fahimtar abinda ke faruwa da jikinta". Idanu sosai akhnan ta sake fiddawa,kafin kuma a hankali su koma daidai saboda ruwan hawayen da suka tara na karyewar zuciya.
Shuru ya ratsa dakin,kowa da abinda yake kai kawo cikin ransa.
A hankali nanay ta sauke kallonta kan akhnan. Ba mamaki bane.....kowacce mace takan tafka nata kalan shirmen da quruciyar yayin cikin fari. Wani abune da kusan yake shammatar kowacce mace,don haka nata kalan shirmen cikin fari kenan. Yadda tayi tsuru tsuru kama me laifi ya sanya nanay kusan sakin murmushi,amma saita maze,ta maida dubanta ga haisam.
"Bamu guri.....zamuyi magana" Tsam ya miqe ba tare daya musa ba. Hakan ya masa,qilan tunda nanay ce ta tsaya ta saurara ta kuma fahimta. Shima ta rage masa aiki,amma yadda yasan ta koyi rikici da rigima a kwanakin nan tabbas yau saidai ya shiryawa tarar kowanne rikici nata.
Yana sanya qafarsa waje ya tuna abinda saamee tayi dazu,take dan annurin fuskarsa ya bace,ya kuma sauya akalarsa daga sitting room da yayi niyyar zama ya jirasu,ya nufi hanyar dakunan baccinsu.
Da farko sanda saqon kiran ya iski saame ta tsorata,ta fara hasashen girman laifin abinda tayi da hukuncinta. Sanannen abu ba,ba wanda zai taso cikin gidan yace baya gane umarni daga gurin yarima haisam,da idanu kawai ba tare da aiki ko magana ba. Ya mata maganan.....amma son gane komai ya sanyata batayi aiki da ita ba,wanda wannan kawai laifi ne me zaman kansa.
To amma a hankali sai taji tsoron yana gushewa sanda aka gaya mata shi daya ne,a wani qaramin guri da sukan zauna susha iska.
Samun kanta tayi da matsawa ta qara turare,ta sauya hijabin jikinta da mayafi yalwatacce. Ko ba komai.....koda fada zaiyi mata,zataso ya ganta da kyawun nan nata.
Duk wani confidence data dauko ya kwaranye sanda ta soma hangen bayansa. Yana tsaye ya bada baya,amma gaba daya kwarjininsa ya cika gurin,kamar yadda qamshinsa ke sauya yanayin gurin da wani irin yanayi me dadin gaske.
Ta qarasa bayansa ta tsaya tana sallama kanta a qasa. Kamar baiji ba,sai daya dauki wasu sakanni sannan ya amsa qasa qasa,ya taka ba tare daya waiwayo ba ya isa ga wata kujera dake gabansa kadan ya zauna.
Idanunsa ya sauke a kanta a hankali. Karon farko yana jin haushin sonshi da takeyi gaba daya. Besan me yasa ta gaza ganewa ba,baisan me yasa bata fahimci yafi son ya farauci zuciyar da ba ita ta kawo kanta ba.
"Saamee" Ya kirata,sunan da muryar suka tsarga mata.
"Na'am"
"Kinsan hukuncin watsar da umarnin cikin gidan nan....." Ya fada kai tsaye kaman me bata amsar tambayarta bame tambaya ba.
"B....ban..." Ta fara yunqurin yin magana.
"Banyi tunanin....." Ta sake yunqurin fada amma sai ta kasa qarasawa sanda ta tuna ba'ayi masa qarya.
"To ki fara tunani daga yau" Ya furta da wannan nutsuwar tasa da kwarjinin nan dake bugarta.
Tadan daga kanta sannan ta sauke,ta san muryar nan. Muryar da haisam ke amfani da ita idan haqurinsa ya qare.
"Akwai abu daya da nakeso ki fahimta" Ya fada yana dakatawa.
"Kin taso a gidan nan."
"Nanay ta raina ki."
"An ba ki mutunci." Sai ya tsaya.
"Kuma saboda mutuncin nan ne nake magana da ke cikin girmamawa." Zuciyarta taji ta buga da kalmar girmamawar daya ambata. Amma kalmar da ta biyo baya...ita ce ta karya duk wani fata da ya rage mata.
"Daga yau." Ya fada a sarari.
"Idan ni da matata muna wani wuri..."
"Ki bamu guri"
"Me yake nufi?" Ta tambayi kanta da wani irin nauyi da tashin hankali daya saukar mata. Kaman yasan abinda take tambayar kanta din yace.
"Ina nufin....duk inda muka zauna,kibar wajen". Idanunta ta lumshe tana jin tashin hankali. Ta fahimci abinda yakeyi,yana rufe qofa ne. Don wajibi ne dole ne akan kowa cikin masarautar biyayya ga umarninsa muddin yana son ci gaba da zama. Ya rufe ya kulle mata duka sauran wata qofa da take da fata a kanta.
"Kada ki sake shiga tsakanin zamanmu.....kada ki sake kawo wani abu a zamanmu.....kada ki kula da komai daya shafemu a irin wannan zaman...musamman ita,ni zan kula da ita"
Hawaye ne suka zubowa saamee masu wani irin dumi. Ba saboda an yi mata ihu ba. Ba saboda an wulaqanta ta ba. A'ah....saboda ta fahimci saqon sosai sama da yadda take tunanin ma zata fahimta din.
Ya koreta ta ruwan sanyi daga gurin da take da fata,ya koreta daga rayuwar gidan gaba daya a fakaice.
Sai Haisam ya qarasa da kalma daya cikin nutsuwa. Amma mai nauyin da ya isa ya rufe kowace qofa.💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 145*
"Ki girmama iyakar da ke tsakanin ki da matata."
"Saboda ba zan sake maimaita wannan maganar ba."
"In sha Allah" Ta fada muryarta tana rawa,sannan ta juya cikin tashin hankali tana komawa ciki.
A wannan karon ta fara zargin kanta. Ta yaya ta bari idanunta suka kulle har take neman zubdawa kanta mutunci da kimarta na diya mace?. Anya wannan hanyar zata bulle mata kuwa?,anya ba zata koma da baya ta maida akalar hankalinta da tunaninta inda ake nemanta ido rufe da dukkan qauna ba?.
(Nidai nace oho....nacin soyayya dai bana diya mace bane wadda tasan ciwon kanta).
*A K H N A N*
"Ciki?...nanay ni?" Ta fada da wani tsoro a muryarta tana fidda idanunta waje tana nuna kanta da yatsanta.
Murmushi me qarfi ya qwacewa nanay,ta danyi qasa da kanta tana karantar tsoron cikin sosai daga idanunta. Sake matsowa kusa da ita tayi ta kuma sake kamo hannayenta tana karantar yadda take buqatar a nutsar mata da zuciya da bayanin da zata gamsu.
"Eh....ke din".
"Amma nanay.....banji ciwo ba" Tayi maganan da yanayin dake nuna sakalcinta a fili.
"Duk wanda yake da ciki sai yaji wani ciwo ne na daban?....sannan baki lura da yadda kikejin gajiya ba.....zaben abinci?,rashin son wani qamshi ko wari da sauransu?,duka wannan ba ciwo bane?" Nanay tayi maganan tana duban tsakiyar qwayar idanunta. Shuru akhnan din tayi,wani irin shuru da ya nuna zurfin nazarinta sosai.
Murmushi nanay tayi,ta miqa hannu ta shafi gefan fuskar akhnan din a nutse.
"Nima na taba zama sabuwar amarya"