Sashe 176
LUu Luu Part 3 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Sai ta jingina da bakin qofar parlour tana kallonsu. Ba tare da ta ce komai ba......haisam ne ya fara lura da ita. Murmushi ya bayyana a gefen bakinsa.
"Why are you standing there?" Ya fada da muryar nan da ko yaushe take taushi idan zai magana da ita. Kusan narkewa take idan taji muryar,akwai randa ta riqeshi gam suna cikin yara,Allah yasa sun juya suna ficewa.
"Haisammm manaaa" Ta fada a shagwabe,shi da ita duka idan suna abu kaman basu ajiye yara haka ba.
"Akhnaaaannn.....me kuma?"
"Kana sani ina narkewa......don Allah abbeee....wannan muryann....hmmmmnnnn". Murmushi ya saki,ya kamata a nutse ya zaunar da ita,sannan ya zauna kusa da ita.
" Bazan iya daga miki murya ba my princess....bazan iya ba,kada ma Allah ya kawo ranan....manzon Allah ne yace rifqaan bilqawarir,ma'ana kuyi hankali da abun qarau dinnan,kaman abu na glass....kinsan me yake nufi?" Saita girgiza kai tana murmushi. Ta karanta ta sani ta gani,amma a bakinsa kawai takeso taji. Kota karanta nassi ko tarihi,tafiso taji ta a bakinsa,yana wani irin shigarta ne da zauna mata a kai.
"Manzo S A W ya kwatanta zuciyar diya mace da tangaran ko glass saboda rauninku,yaya zan iya miki magana da irin muryar da nake magana da kowa?....kamar ke din bata musamman bace?" Wani lallausan murmushi ne ya subuce mata,ta boye fuskarta saman kafadarsa tana dariya.
"Kai kam ko....Allah ya maka baiwar iya koyarwa....kai din malami ne na haqiqa".
"Karatu kawai na iya na takarda....ko harda wancan daya karatun?" Ya tambayeta muryarsa can qasa da wani yanayi daya sanya duka tsigar jikinta zubawa.
Ruqunqumeshi tayi tana qyalqyala dariya,don da iya maganar kawai ya tsumata gaba daya. Dama haka yakeso.....irin cikin su ashraf ne.....kai tsaye ya dauketa suka wuce can matattarar sirrinsu.
Kama yatsunta da yayi ya dawo da ita daga tunanin,sai ta girgiza kai a hankali.
"Nothing." Ta amsa tambayarsa,amma murmushinta ya qara fadada.
Ashraf ne ya karaso kusa da ita.
"Ammiee."
"Hmm?"
"How was it?" Ta san abinda yake nufi,kowace rana idan ya ja sallah.
Sai ya tambayeta.
Sai ta kamo fuskarsa da hannunta,kamar yadda take yi tun yana qarami.
"It was beautiful ashraf......barakallahu feek" Idanunsa suka yi haske da wani farincikin yabo daga mamar tasa. Uwar da sukewa wata irin tarin qauna tun suna qananunsu har zuwa yanzu da suka qara hankali.
"Every time I hear your voice..." Sai ta dan yi shiru
"...I remember the little boy who used to sleep on my chest." Su asif suka fara dariya.
"Not again." Ahsan ya fada.
"Mama always says that."ajmal yace shima.
"Because it's true." Ashraf ya fada yana gyada kai cike da qaunar ammiee din tasa
Tsaiwa kawai haisam yayi yana kallonsu,idanunsa cike da wani irin natsuwa.
Akhnan ta waigo ta hada ido da shi,na dan lokaci babu wanda ya yi magana. Sboda babu buqatar magana,magana ce yawancin lokuta sukeyi tsakanin zukatansu.
Shekaru da yawa sun shude. Sun sha gwagwarmaya. Sun sha hawaye. Sun sha farin ciki. Amma a wannan lokacin...da yaransu suna kewaye da su. Da sautin Al-Qur'ani har yanzu yana yawo a kunnuwansu. Da Ramadan ya sake hada su a teburin sahur. Akhnan ta ji kamar Allah Ya amsa addu'ar abinda ta fi so a rayuwa.
Sai ta matsa kusa da Haisam.....ta sauke kanta a kafadarsa.
"Alhamdulillah."
Sai ya sumbaci goshinta a hankali.
"Alhamdulillah." Kuma a karon nan...
ba ta fadeta ne saboda dukiya.
Ko sarauta.
Ko nasara.
Ta fada ne saboda tana kallon mijinta da yaranta.....ta san cewa wannan shi ne mafi kyawun arzikin da Allah ya taba ba ta.
*Alhamdulillah!*🎉🤍
🌹*SAƘON GODIYA*🌹
*_Assalamu Alaikum wa Rahmatullah_*
*Da farko* *_Alhamdulillah da yardar Allah da taimakonsa muka kawo qarshen Lu'u Lu'u._*
*_Kalaman godiya ba za su isa su bayyana irin farin cikina da jin daɗin da nake yi ba saboda qauna_* *_addu'o'i, sharhi, gyara, da goyon bayan da kuka nuna min tun daga farkon wannan tafiya har zuwa yau._*
*_Ga duk wanda ya karanta, ya yi comment,ya yi addu'a, ko ya kasance cikin masu jiran sabon page da doki, ina muku godiya daga zurfin zuciyata. Kun kasance wani babban bangare na nasarar wannan littafi._*
*_A wasu lokutan nakan gaji, nakan rasa qwarin gwiwa, amma kalamanku masu dadi da qarfafawa sukan sa ni ci gaba da rubutu. Wannan littafi ba nawa kadai ba ne, na ku ne tare da ni._*
*_Ina roqon Allah Ya saka muku da alkhairi, Ya sanya abin da kuka karanta ya zama sanadin farin ciki da albarka a gare ku, Ya kuma hada mu a cikin alkhairi a ayyuka masu zuwa._*
*_Ku yafe min duk wani kuskure da kuka gani a cikin rubutun, domin kamala ta Allah ce kadai._*
*_Da fatan za ku ci gaba da kasancewa tare da ni a dukkan tafitar rubuce rubuce na na gaba._*
*_Na gode. Na yaba. Ina Qaunar ku saboda Allah._* 🤍🌹
*FI AMANILLAH*🙌🏽🙌🏽
✍️ *Safiyya HUGUMA*
08187255862
"Why are you standing there?" Ya fada da muryar nan da ko yaushe take taushi idan zai magana da ita. Kusan narkewa take idan taji muryar,akwai randa ta riqeshi gam suna cikin yara,Allah yasa sun juya suna ficewa.
"Haisammm manaaa" Ta fada a shagwabe,shi da ita duka idan suna abu kaman basu ajiye yara haka ba.
"Akhnaaaannn.....me kuma?"
"Kana sani ina narkewa......don Allah abbeee....wannan muryann....hmmmmnnnn". Murmushi ya saki,ya kamata a nutse ya zaunar da ita,sannan ya zauna kusa da ita.
" Bazan iya daga miki murya ba my princess....bazan iya ba,kada ma Allah ya kawo ranan....manzon Allah ne yace rifqaan bilqawarir,ma'ana kuyi hankali da abun qarau dinnan,kaman abu na glass....kinsan me yake nufi?" Saita girgiza kai tana murmushi. Ta karanta ta sani ta gani,amma a bakinsa kawai takeso taji. Kota karanta nassi ko tarihi,tafiso taji ta a bakinsa,yana wani irin shigarta ne da zauna mata a kai.
"Manzo S A W ya kwatanta zuciyar diya mace da tangaran ko glass saboda rauninku,yaya zan iya miki magana da irin muryar da nake magana da kowa?....kamar ke din bata musamman bace?" Wani lallausan murmushi ne ya subuce mata,ta boye fuskarta saman kafadarsa tana dariya.
"Kai kam ko....Allah ya maka baiwar iya koyarwa....kai din malami ne na haqiqa".
"Karatu kawai na iya na takarda....ko harda wancan daya karatun?" Ya tambayeta muryarsa can qasa da wani yanayi daya sanya duka tsigar jikinta zubawa.
Ruqunqumeshi tayi tana qyalqyala dariya,don da iya maganar kawai ya tsumata gaba daya. Dama haka yakeso.....irin cikin su ashraf ne.....kai tsaye ya dauketa suka wuce can matattarar sirrinsu.
Kama yatsunta da yayi ya dawo da ita daga tunanin,sai ta girgiza kai a hankali.
"Nothing." Ta amsa tambayarsa,amma murmushinta ya qara fadada.
Ashraf ne ya karaso kusa da ita.
"Ammiee."
"Hmm?"
"How was it?" Ta san abinda yake nufi,kowace rana idan ya ja sallah.
Sai ya tambayeta.
Sai ta kamo fuskarsa da hannunta,kamar yadda take yi tun yana qarami.
"It was beautiful ashraf......barakallahu feek" Idanunsa suka yi haske da wani farincikin yabo daga mamar tasa. Uwar da sukewa wata irin tarin qauna tun suna qananunsu har zuwa yanzu da suka qara hankali.
"Every time I hear your voice..." Sai ta dan yi shiru
"...I remember the little boy who used to sleep on my chest." Su asif suka fara dariya.
"Not again." Ahsan ya fada.
"Mama always says that."ajmal yace shima.
"Because it's true." Ashraf ya fada yana gyada kai cike da qaunar ammiee din tasa
Tsaiwa kawai haisam yayi yana kallonsu,idanunsa cike da wani irin natsuwa.
Akhnan ta waigo ta hada ido da shi,na dan lokaci babu wanda ya yi magana. Sboda babu buqatar magana,magana ce yawancin lokuta sukeyi tsakanin zukatansu.
Shekaru da yawa sun shude. Sun sha gwagwarmaya. Sun sha hawaye. Sun sha farin ciki. Amma a wannan lokacin...da yaransu suna kewaye da su. Da sautin Al-Qur'ani har yanzu yana yawo a kunnuwansu. Da Ramadan ya sake hada su a teburin sahur. Akhnan ta ji kamar Allah Ya amsa addu'ar abinda ta fi so a rayuwa.
Sai ta matsa kusa da Haisam.....ta sauke kanta a kafadarsa.
"Alhamdulillah."
Sai ya sumbaci goshinta a hankali.
"Alhamdulillah." Kuma a karon nan...
ba ta fadeta ne saboda dukiya.
Ko sarauta.
Ko nasara.
Ta fada ne saboda tana kallon mijinta da yaranta.....ta san cewa wannan shi ne mafi kyawun arzikin da Allah ya taba ba ta.
*Alhamdulillah!*🎉🤍
🌹*SAƘON GODIYA*🌹
*_Assalamu Alaikum wa Rahmatullah_*
*Da farko* *_Alhamdulillah da yardar Allah da taimakonsa muka kawo qarshen Lu'u Lu'u._*
*_Kalaman godiya ba za su isa su bayyana irin farin cikina da jin daɗin da nake yi ba saboda qauna_* *_addu'o'i, sharhi, gyara, da goyon bayan da kuka nuna min tun daga farkon wannan tafiya har zuwa yau._*
*_Ga duk wanda ya karanta, ya yi comment,ya yi addu'a, ko ya kasance cikin masu jiran sabon page da doki, ina muku godiya daga zurfin zuciyata. Kun kasance wani babban bangare na nasarar wannan littafi._*
*_A wasu lokutan nakan gaji, nakan rasa qwarin gwiwa, amma kalamanku masu dadi da qarfafawa sukan sa ni ci gaba da rubutu. Wannan littafi ba nawa kadai ba ne, na ku ne tare da ni._*
*_Ina roqon Allah Ya saka muku da alkhairi, Ya sanya abin da kuka karanta ya zama sanadin farin ciki da albarka a gare ku, Ya kuma hada mu a cikin alkhairi a ayyuka masu zuwa._*
*_Ku yafe min duk wani kuskure da kuka gani a cikin rubutun, domin kamala ta Allah ce kadai._*
*_Da fatan za ku ci gaba da kasancewa tare da ni a dukkan tafitar rubuce rubuce na na gaba._*
*_Na gode. Na yaba. Ina Qaunar ku saboda Allah._* 🤍🌹
*FI AMANILLAH*🙌🏽🙌🏽
✍️ *Safiyya HUGUMA*
08187255862