Sashe 163
LUu Luu Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har suka isa gida,ya zagaya ya bude mata ta fito,maimakon ta jirashi saita fara takawa ciki tana tura qatoton cikinta gaba,ita a lallai fushi takeyi.
Stairs ta nufa kai tsaye,abinda a yanzun indai ya kama zata hau din yana riqe da ita ne,hakanan idan zata sauko shike zame mata madogara.
Amma kafin ta kai matakalar farko.
"Zauna." Muryar Haisam ta dakatar da ita.
Sai ta juya,ya nuna mata kujerar falon.
"Please." Ya qarashe fada a nutse.
Ta lura da yadda ya fadi kalmar,ba umarni ba ne wannan karon.
Sai ta tsinci kanta da dawowa ta zauna a hankali.
Gabanta ya matso shima ya zauna sosai. Na wasu seconds yana kallonta ne kawai,kamar yana neman hanyar da zai fara.
Ita dince ce ta fara magana muryarta na rawa.
"Yanzu zan iya sanin me yasa ka taso ni daga wajen su Sultane kamar yarinya?" Hawayenta suka tsaya dab da idanunta.
Numfashi ya sauke a hankali.
"Saboda kina daukar kanki kamar baki da ciki." Nan take ta yi shiru,wannan ya bashi dama yaci gaba.
"Kin yi tafiya daga wata qasa." Ya daga yatsa daya.
"Kin isa gida." Sai ya daga na biyu.
"Kin qi hutawa."
Na uku.
"Kin je masarauta."
Na huɗu.
"Kuma kin zagaya rabin wurin." Akhnan ta sauke idanunta a hankali tana jin nauyinsa. Yana da wani irin kawaici,yana da wani irin haquri,amma batasan me yasa take saurin hasala haka ba. Ta sani,ba qarya yake yi ba.
Jingina yayi da kujerarsa. A karo na farko muryarsa ta yi laushi sosai fiye da kima.
"Do you know why I'm worried?"Ta girgiza kai a hankali,sai ya dan yi shiru kafin ya ce
"Because there are only ten days left." Akhnan ta dago kai da sauri.
"What?"
"Ten days."Ya maimaita.
"Kwana goma kacal." Ya sake fadi.
Ta kafe shi da idanu kamar bata fahimtar yaren French
"Kwana goma zuwa me?"Sai ya kalleta kai tsaye.
"Kwana goma zuwa ranar haihuwar yaranmu."
Wani irin shuru parlor din yayi,sai ta ji zuciyarta na bugawa
"Me?" Ta tambaya da tsoro a muryarta.
Haisam ya dan matsa kusa da ita.
"Likitoci sun riga sun tsara ranar haihuwar,saboda yanayin da suke ganin ya fi dacewa da ke da jariran" Ido ta zuba masa da tsoro sosai.
"Kuma baka gaya min ba?" Wani dan murmushi mai laushi ya bayyana a fuskarsa.
"Na yi qoqarin hakan." Sai ta tuna.....sau nawa yake son yin wata magana ya fasa. Sau nawa yake kallonta ya yi shiru.
Ya kamo hannunta,yatsunsa suka rufe nata gaba daya.
"Kin kasance kina gudun maganar cikin tun farko giiftii." Yayi dan shuru.
"Ban so na matsa miki ba." Idanunta suka cika da wani irin yanayi. Ba tsoro zalla ba.....ba fushi ba.....sai mamaki da yanzun yafi rinjaye.
Kwana goma.....kwana goma kacal?. Kwana goma sai ta zama uwa?.....
A karon farko ita ce ta matse hannun haisam,muryarta can qasa sosai.
"Haisam..."
"Mm?"
"Tsoro nake ji." Sai ya dan yi murmushi,irin murmushin da yake yi idan yana son kwantar mata da hankali.
Ya dago hannunta ya sumbaci bayan tafin,sannan ya ce a hankali
"Good."sai ta hade gira.
"Good?"
"Because I'm scared too." Akhnan ta zuba masa ido.
Da wuya Haisam ya taba yarda yana tsoron wani abu,yau gashi saboda ita taga tsoro qarara a idanunsa.
Kallonsa ya sauka kan cikinta,sannan ya dawo kanta.
"But we'll do it together......in sha Allah".
A wannan karon,akhnan ba ta sake tunanin masarauta ba dama kowa da kowa,sai kwanaki goma da suka rage kafin rayuwarsu ta canza har abada.
*_To masu tafiya suna saiku shirya,ku bada list kafin a gama diban adadin 'yan tafiya_*🤒🤒
Nidai na gama nade kayana zanyi gaba,saikun iso.💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 150*
*_The Day Three Princes Arrived_*
*A Kingdom Reborn*
Cikin wani irin yanayi aka kammala dukka bakukuwan. Wani irin biki daya barwa akhnan wani kebantaccen nishadi duk da irin yanayin da take ciki. Ya kuma taimaka wajen dauke mata hankali dan kadan daga tunanin kwanaki goman da suke tunkarota.
Tare suka wuce da amare,shehnaz da aisa,wadanda daga kowacce tabi mijinta inda zasu zauna,daga can kuma kowacce zasu wuce guraren da sukafi yawan zama guraren ayyukansu a qasashe da garuruwa daban daban.
★★Safiyar ranar ta zama ta daban kuma ta musamman a gurin dukkanin ahalin motii ibraheem aba jifar,da kuma ahalin sultane muhammad hammud. Safiya ce da dukkanin ahalin biyu ke sanya ran yin idanu biyu da jikokin farko na masarautun.....wadanda zasu sama cikakkun jikoki zalla na jikin motii da sultane.
Daga cikin lafiyayyen amenity na asibitin. Giiftii khadeeja muhammad hammud ce,zaune gefan gadon asibitin da aka gyarashi da kyau tun da sassafe da wani irin lallausan fari qal din duvet. Sanye take da silk white robe,wadda tabi jikinta ta kuma fidda dogon cikinta dake gaba wanda sai data tallafeshi da pillow saboda yada take jin yana rinjayarta. Dogon gashinta a nannade a cure a qeyarta da yanayin daya sanya tsayinsa dukka ya bace gaba daya saboda gammo da akayi mata dashi. Hatta da dakin ya sani,yau din wani abu ne na musamman ke shirin faruwa. Saboda kebantaccen daki ne da iyalan motii aba jifar kawai ke kwanciya a cikinsa. Ba dakin kawai ba.....ward ne musamman dan madaidaici da aka ware saboda royal blood na gidan motii aba jifar.
Tun daren jiya hannunta yake saman cikinta. Cikin daya kasance tare da ita tsahon wata takwas da kwanaki,cikin da ya canza rayuwarta..... A yau zasu rabu,ba rabuwar baqinciki ba,tana sanya ran zama ta alkhairi da farinciki. Yadda aka jarrabi haisam da son cikin ya sanya take ganin tata qwalamar akan son yaran batakai ko ina ba.
Ranar asibitin ya cika da tsaro gaba daya,kamar shugaban qasa ke kwance a ciki. Ranan komai na asibitin ya shaida masu abu da abinsu ne suke cikinsa. Dukkan floor din maternity wing an killaceshi.
A hankali qofar bathroom ta bude,haisam ne ke takowa a hankali,gashin kansa dana girarsa,harma da gargasar hannunsa duka jiqe da ruwa.
Batasan sau nawa yayi alwala yayi sallah ba daga daren jiya zuwa yanzu. Ta maida idanunta a nutse cikin nasa idanun. Wadannan manyan idanun masu haske,amma a yau sun canza launi kadan,sun kuma rusuna sosai,alamun dake sake bata tabbacin baiyi cikakken bacci ba jiya,bayan ita ya tilasta mata yin baccin duk da bata shirya hakan ba. Dauke idanunsa yayi,ta tabbatar yana son boye mata rashin baccinsa dama karayar da tunda take dashi bata taba ganinta cikin qwayar idanunsa ba irin yau. Tun daren jiya bai zauna ba......batasan ya fita damuwa ba sai yanzu. A kwana taran baya kallon kanta take tana sake mamakin yadda take tsoro take karaya.....amma haisam nan da nan yake maida mata wannan energy din. Batasan ya boye komai bane ya kuma danne sai yanzu,yanzun da mintuna kadan suka rage a shiga da ita Cs din.
"Haisam." Ta kirashi da yanayin da tasan yafi so. Sai ya waigo kamar yana jiran kiranta.
"Ka zauna." Ta fada tana jin tausayinsa yana narkar da zuciyarta. Iya wannan kawai ya sanyata dagewa da addu'an Allah yabar masa ita da yaran duka a raye.
"Ina zaune tun dazun ai"
"A'a." Ta girgiza kai tana sakar masa murmushi.
"Kana sintiri dai yarima na" Karon farko a ranar dan murmushi ya bayyana a fuskarsa.
"You're enjoying this." Ya tambaya yana dage mata girarsa duka biyun.
"A little." Ta fada tana kashe masa ido daya still da murmushi a fuskarta.
"Good." Ya fada yana warware hannun shirt dinsa daya nade saboda alwala. Ta dan bishi da kallo,yau shigarsa ma,irin shigar da ba kasafai ya fiya fita da iya bane. Farar t-shirt ce qal da baqin trouser daya haska har saman dogayen yatsun qafafunsa. Ya mata wani irin kyau,sai takejin kamar a qara mata lokaci tare dashi tayita kallonsa.
Qarasowa yayi ya durqusa a gabanta. Ya dora hannunsa kan cikinta. A hankali ya motsa labbansa,bayan ya matso dasu kusa da tsinin cikin.
"Behave yourselves today." Wata tattausar dariya ta saki
"Wa kake wa magana?" Ta fada idanunta a bude tana kallon wannan calm face din nashi.
"My sons." Ya bata amsa da calmness dinsa da baya taba barin jikinsa komai girman tashin hankali.
"Who said they're boys?" Ta fadi tana bata fuska,don ita har ga Allah baby girls tafi sha'awa. Tunda ta dora idanunta akan baby falaak da taci sunan morsa safiyya suke kiranta da sultana,taji duk duniya baby girl takeso.
"Ku bani ita don Allah" Tace da maleek a daren sunan daya samu shigowa ganinsu. Murmushin nan nasa me harba jinin sarauta a jikinsa yayi,ya kalli falaak kawai.
"Idan ta baki nima na bayar" Saita falaak ta fidda ido waje tana dariya.
"Zai hadamu fada ne kawai giiftii". Haisam da yake can gefe yana amsa waya ya jisu,bai amsa mata ba sai da suke tattaki suna komawa sashensu.
"Abinnan fa da kikace zaki kira sultane ki gaya masa anyi shi akayi aka samu yarinyar nan....banda anyi hakan da falaak din taki tana nan zaune ita daya ba sultana din.......amma yanzu duk bayan kince zaa kashe miki sisinki kuma an mata gata da baby kice su baki?" Kunya ta kamata,wata irin kunya me nauyi data tuna wautarta a wancan ranar. Allah ya taimaketa daya taka mata birki,da da wanne ido zata dinga kallon sultane a yanzu?.
"Eh....amma har yanzu abinnan dai kasan abun jin kunya ne ko?"
"Eh.....duk da hakan kuma baki fasa tashi na jiya kince saina miki ba ko" Qaramin ihun kunya ta saki tana cusa kanta a qirjinsa data tuna da dabarun da aka samu akayi saboda yadda tsaho da tudun cikinta ke hana komai.
"Allah ya tabbatarmin dake a haka ko kin haihu" Taji yana fada qasa qasa cikin nishadi.
"They are." Amsar haisam ta maido da tunaninta kansa.
"And if they're not?" Ta fada tana turo baki gaba.
"They are." Ya sake maimaitawa kyawawan idanunsa suna lumshewa gami da budewa.
Kukan shagwaba ta sakar masa,ya miqe yana sakin siririn murmushi gami da fara cire mata dan kunnen dake kunnenta.
"Fadata ai ba fadan Allah bane ko?" Sai daya fadi hakan sannan ya samu sauqi.
Shi ya shiryata tsaf cikin kayan daya kamata ta kasance a cikinsa.
Wani irin shiru ne ya mamaye private wing din asibitin. Ba shiru irin na rashin mutane ba.
A'a.....shirun da ke zuwa kafin wani babban al'amari.
Stairs ta nufa kai tsaye,abinda a yanzun indai ya kama zata hau din yana riqe da ita ne,hakanan idan zata sauko shike zame mata madogara.
Amma kafin ta kai matakalar farko.
"Zauna." Muryar Haisam ta dakatar da ita.
Sai ta juya,ya nuna mata kujerar falon.
"Please." Ya qarashe fada a nutse.
Ta lura da yadda ya fadi kalmar,ba umarni ba ne wannan karon.
Sai ta tsinci kanta da dawowa ta zauna a hankali.
Gabanta ya matso shima ya zauna sosai. Na wasu seconds yana kallonta ne kawai,kamar yana neman hanyar da zai fara.
Ita dince ce ta fara magana muryarta na rawa.
"Yanzu zan iya sanin me yasa ka taso ni daga wajen su Sultane kamar yarinya?" Hawayenta suka tsaya dab da idanunta.
Numfashi ya sauke a hankali.
"Saboda kina daukar kanki kamar baki da ciki." Nan take ta yi shiru,wannan ya bashi dama yaci gaba.
"Kin yi tafiya daga wata qasa." Ya daga yatsa daya.
"Kin isa gida." Sai ya daga na biyu.
"Kin qi hutawa."
Na uku.
"Kin je masarauta."
Na huɗu.
"Kuma kin zagaya rabin wurin." Akhnan ta sauke idanunta a hankali tana jin nauyinsa. Yana da wani irin kawaici,yana da wani irin haquri,amma batasan me yasa take saurin hasala haka ba. Ta sani,ba qarya yake yi ba.
Jingina yayi da kujerarsa. A karo na farko muryarsa ta yi laushi sosai fiye da kima.
"Do you know why I'm worried?"Ta girgiza kai a hankali,sai ya dan yi shiru kafin ya ce
"Because there are only ten days left." Akhnan ta dago kai da sauri.
"What?"
"Ten days."Ya maimaita.
"Kwana goma kacal." Ya sake fadi.
Ta kafe shi da idanu kamar bata fahimtar yaren French
"Kwana goma zuwa me?"Sai ya kalleta kai tsaye.
"Kwana goma zuwa ranar haihuwar yaranmu."
Wani irin shuru parlor din yayi,sai ta ji zuciyarta na bugawa
"Me?" Ta tambaya da tsoro a muryarta.
Haisam ya dan matsa kusa da ita.
"Likitoci sun riga sun tsara ranar haihuwar,saboda yanayin da suke ganin ya fi dacewa da ke da jariran" Ido ta zuba masa da tsoro sosai.
"Kuma baka gaya min ba?" Wani dan murmushi mai laushi ya bayyana a fuskarsa.
"Na yi qoqarin hakan." Sai ta tuna.....sau nawa yake son yin wata magana ya fasa. Sau nawa yake kallonta ya yi shiru.
Ya kamo hannunta,yatsunsa suka rufe nata gaba daya.
"Kin kasance kina gudun maganar cikin tun farko giiftii." Yayi dan shuru.
"Ban so na matsa miki ba." Idanunta suka cika da wani irin yanayi. Ba tsoro zalla ba.....ba fushi ba.....sai mamaki da yanzun yafi rinjaye.
Kwana goma.....kwana goma kacal?. Kwana goma sai ta zama uwa?.....
A karon farko ita ce ta matse hannun haisam,muryarta can qasa sosai.
"Haisam..."
"Mm?"
"Tsoro nake ji." Sai ya dan yi murmushi,irin murmushin da yake yi idan yana son kwantar mata da hankali.
Ya dago hannunta ya sumbaci bayan tafin,sannan ya ce a hankali
"Good."sai ta hade gira.
"Good?"
"Because I'm scared too." Akhnan ta zuba masa ido.
Da wuya Haisam ya taba yarda yana tsoron wani abu,yau gashi saboda ita taga tsoro qarara a idanunsa.
Kallonsa ya sauka kan cikinta,sannan ya dawo kanta.
"But we'll do it together......in sha Allah".
A wannan karon,akhnan ba ta sake tunanin masarauta ba dama kowa da kowa,sai kwanaki goma da suka rage kafin rayuwarsu ta canza har abada.
*_To masu tafiya suna saiku shirya,ku bada list kafin a gama diban adadin 'yan tafiya_*🤒🤒
Nidai na gama nade kayana zanyi gaba,saikun iso.💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 150*
*_The Day Three Princes Arrived_*
*A Kingdom Reborn*
Cikin wani irin yanayi aka kammala dukka bakukuwan. Wani irin biki daya barwa akhnan wani kebantaccen nishadi duk da irin yanayin da take ciki. Ya kuma taimaka wajen dauke mata hankali dan kadan daga tunanin kwanaki goman da suke tunkarota.
Tare suka wuce da amare,shehnaz da aisa,wadanda daga kowacce tabi mijinta inda zasu zauna,daga can kuma kowacce zasu wuce guraren da sukafi yawan zama guraren ayyukansu a qasashe da garuruwa daban daban.
★★Safiyar ranar ta zama ta daban kuma ta musamman a gurin dukkanin ahalin motii ibraheem aba jifar,da kuma ahalin sultane muhammad hammud. Safiya ce da dukkanin ahalin biyu ke sanya ran yin idanu biyu da jikokin farko na masarautun.....wadanda zasu sama cikakkun jikoki zalla na jikin motii da sultane.
Daga cikin lafiyayyen amenity na asibitin. Giiftii khadeeja muhammad hammud ce,zaune gefan gadon asibitin da aka gyarashi da kyau tun da sassafe da wani irin lallausan fari qal din duvet. Sanye take da silk white robe,wadda tabi jikinta ta kuma fidda dogon cikinta dake gaba wanda sai data tallafeshi da pillow saboda yada take jin yana rinjayarta. Dogon gashinta a nannade a cure a qeyarta da yanayin daya sanya tsayinsa dukka ya bace gaba daya saboda gammo da akayi mata dashi. Hatta da dakin ya sani,yau din wani abu ne na musamman ke shirin faruwa. Saboda kebantaccen daki ne da iyalan motii aba jifar kawai ke kwanciya a cikinsa. Ba dakin kawai ba.....ward ne musamman dan madaidaici da aka ware saboda royal blood na gidan motii aba jifar.
Tun daren jiya hannunta yake saman cikinta. Cikin daya kasance tare da ita tsahon wata takwas da kwanaki,cikin da ya canza rayuwarta..... A yau zasu rabu,ba rabuwar baqinciki ba,tana sanya ran zama ta alkhairi da farinciki. Yadda aka jarrabi haisam da son cikin ya sanya take ganin tata qwalamar akan son yaran batakai ko ina ba.
Ranar asibitin ya cika da tsaro gaba daya,kamar shugaban qasa ke kwance a ciki. Ranan komai na asibitin ya shaida masu abu da abinsu ne suke cikinsa. Dukkan floor din maternity wing an killaceshi.
A hankali qofar bathroom ta bude,haisam ne ke takowa a hankali,gashin kansa dana girarsa,harma da gargasar hannunsa duka jiqe da ruwa.
Batasan sau nawa yayi alwala yayi sallah ba daga daren jiya zuwa yanzu. Ta maida idanunta a nutse cikin nasa idanun. Wadannan manyan idanun masu haske,amma a yau sun canza launi kadan,sun kuma rusuna sosai,alamun dake sake bata tabbacin baiyi cikakken bacci ba jiya,bayan ita ya tilasta mata yin baccin duk da bata shirya hakan ba. Dauke idanunsa yayi,ta tabbatar yana son boye mata rashin baccinsa dama karayar da tunda take dashi bata taba ganinta cikin qwayar idanunsa ba irin yau. Tun daren jiya bai zauna ba......batasan ya fita damuwa ba sai yanzu. A kwana taran baya kallon kanta take tana sake mamakin yadda take tsoro take karaya.....amma haisam nan da nan yake maida mata wannan energy din. Batasan ya boye komai bane ya kuma danne sai yanzu,yanzun da mintuna kadan suka rage a shiga da ita Cs din.
"Haisam." Ta kirashi da yanayin da tasan yafi so. Sai ya waigo kamar yana jiran kiranta.
"Ka zauna." Ta fada tana jin tausayinsa yana narkar da zuciyarta. Iya wannan kawai ya sanyata dagewa da addu'an Allah yabar masa ita da yaran duka a raye.
"Ina zaune tun dazun ai"
"A'a." Ta girgiza kai tana sakar masa murmushi.
"Kana sintiri dai yarima na" Karon farko a ranar dan murmushi ya bayyana a fuskarsa.
"You're enjoying this." Ya tambaya yana dage mata girarsa duka biyun.
"A little." Ta fada tana kashe masa ido daya still da murmushi a fuskarta.
"Good." Ya fada yana warware hannun shirt dinsa daya nade saboda alwala. Ta dan bishi da kallo,yau shigarsa ma,irin shigar da ba kasafai ya fiya fita da iya bane. Farar t-shirt ce qal da baqin trouser daya haska har saman dogayen yatsun qafafunsa. Ya mata wani irin kyau,sai takejin kamar a qara mata lokaci tare dashi tayita kallonsa.
Qarasowa yayi ya durqusa a gabanta. Ya dora hannunsa kan cikinta. A hankali ya motsa labbansa,bayan ya matso dasu kusa da tsinin cikin.
"Behave yourselves today." Wata tattausar dariya ta saki
"Wa kake wa magana?" Ta fada idanunta a bude tana kallon wannan calm face din nashi.
"My sons." Ya bata amsa da calmness dinsa da baya taba barin jikinsa komai girman tashin hankali.
"Who said they're boys?" Ta fadi tana bata fuska,don ita har ga Allah baby girls tafi sha'awa. Tunda ta dora idanunta akan baby falaak da taci sunan morsa safiyya suke kiranta da sultana,taji duk duniya baby girl takeso.
"Ku bani ita don Allah" Tace da maleek a daren sunan daya samu shigowa ganinsu. Murmushin nan nasa me harba jinin sarauta a jikinsa yayi,ya kalli falaak kawai.
"Idan ta baki nima na bayar" Saita falaak ta fidda ido waje tana dariya.
"Zai hadamu fada ne kawai giiftii". Haisam da yake can gefe yana amsa waya ya jisu,bai amsa mata ba sai da suke tattaki suna komawa sashensu.
"Abinnan fa da kikace zaki kira sultane ki gaya masa anyi shi akayi aka samu yarinyar nan....banda anyi hakan da falaak din taki tana nan zaune ita daya ba sultana din.......amma yanzu duk bayan kince zaa kashe miki sisinki kuma an mata gata da baby kice su baki?" Kunya ta kamata,wata irin kunya me nauyi data tuna wautarta a wancan ranar. Allah ya taimaketa daya taka mata birki,da da wanne ido zata dinga kallon sultane a yanzu?.
"Eh....amma har yanzu abinnan dai kasan abun jin kunya ne ko?"
"Eh.....duk da hakan kuma baki fasa tashi na jiya kince saina miki ba ko" Qaramin ihun kunya ta saki tana cusa kanta a qirjinsa data tuna da dabarun da aka samu akayi saboda yadda tsaho da tudun cikinta ke hana komai.
"Allah ya tabbatarmin dake a haka ko kin haihu" Taji yana fada qasa qasa cikin nishadi.
"They are." Amsar haisam ta maido da tunaninta kansa.
"And if they're not?" Ta fada tana turo baki gaba.
"They are." Ya sake maimaitawa kyawawan idanunsa suna lumshewa gami da budewa.
Kukan shagwaba ta sakar masa,ya miqe yana sakin siririn murmushi gami da fara cire mata dan kunnen dake kunnenta.
"Fadata ai ba fadan Allah bane ko?" Sai daya fadi hakan sannan ya samu sauqi.
Shi ya shiryata tsaf cikin kayan daya kamata ta kasance a cikinsa.
Wani irin shiru ne ya mamaye private wing din asibitin. Ba shiru irin na rashin mutane ba.
A'a.....shirun da ke zuwa kafin wani babban al'amari.