Sashe 13
LUu Luu Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana biye da ita tamkar wanda ke gadin wata tsadaddar kadara,dukkan dagawa da saukar fararen tas din qafafunta masu shige da nasa akan idanunsa ne,tanason waiwayawa ne......tanason juyawa ta kalli cikin idanunsa amma tana jin wani abu me nauyi kamar ba zata iya hakan ba.
Dab da bayanta ya zura hannu sanda suka isa personal qofanta ta baya.......bata sani ba,ba kuma zatace ba taga ya fidda keya ya zura ya murza ya kuma bude sannan ya turata ta bude. Bata sake jin motsinsa ba saidai tasan yana tsaye a gurin,zuciyarta na sake zugata.
"Kidan waiwaya ko sau daya ki kalleshi.....ki juya ki gani ko shurunsa ke yake bi da kallo". A wani irin sace ta saci kallonsa ta gefan idanunta,sai taga wayarsa ya fidda a aljihu yana latsawa,alamu kuna sun nuna gajeran saqo yake turawa.
Haka kawai taji wani iri.....haka kawai taji ba dadi. Bata taba satar kallon d'a namiji ba a rayuwarta,saidai ita a saci kallonta harma ta hukunta mutum,amma a yau wai itace ke satar kallon wani?. Waninma da ba ita yake kalla ba?,kallon wayarsa yafi kallonta muhimmanci?.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Sai data shige duka sannan ta juyo a hankali,ta kuma sake wayancewa da dora hannunta saman handle tanayi kamar zata rufe qofar. Wannan karon kuma kai tsaye ta zuba masa dukka blue eyes dinta,tanason tabbatarwa da gaske wayar tasa yake kalla har yanzu?.
Tabbacin kuwa ta samu,don yadda yake typing da sauri da sauri ya gaya mata wani saqon gaggawa ne zai aike. Sosai a yanzun taji ranta ya sosu fiye da dazun,sai kawai ta zabi rufe qofar wanda tana dab da hade gap don da yayi saura qofar ta qarasa kullewa ya daga kansa daga wayar,saidai bai samu daman ganin komai ba sai gefan fuskarta da blue eyes dinta guda daya.
Murza muqullin jiki tayi tana jin zuciyarta tana mata zafi,sannan ta juya a hankali tana sake riqe cloak thobe don cikin hannuwanta tana damqeta da kyau kamar wani zai qwace mata.
"Bai kula ba....bai damu ba?" Ta tambayi kanta tana jin ranta yana sake baci,saidai qamshin nan nasa da ya sanya takejin kamar yana dab da ita ya hana bacin ran nata yaci gaba.
A parlor din da yafi kama da harabar da zaka zauna jiran neman izinin ganinta direct daga bedroom dinta ta iske birra. Ta sani koda kowa zai tafi birra zata zauna.
Ta miqe tana nufota da zummar karbar cloake thobe din saman jikinta ta kuma taimaka mata ta sauya kayan jikinta,amma daga idanun da akhnan tayi tana duban birran da gane rigar waye a jikinta ya sanya birra janyewa da baya. Ganin birran ta fahimci abinda takeson fada kafin ta fadi,saita hadiye maganarta ta juya tana wucewa ciki.
Ta jima zaune da rigar jikinta tana kallon yadda ruwa ke zuba ta glass door din data ratsa bangon,kafin a hankali ta zameta daga kafadarta ta miqe don hadata da 'yar uwarta. Wancan rigar daya bata aro wancan karon bata maida masa ba......a yanzu ga wata ta qaru,saita hadesu guri daya tana zubasu cikin wata 'yar jaka. Har yanzun koda rigar farko ma bata daina qamshin da takeyi ba bare riga ta biyu.
*H A I S A M*
Samun tabbacin ta rufe qofar ya sanyashi maida wayar aljihunsa a hankali,ya juya a nutse yana takawa zuwa sassan sultane da yake iya hangowa dab da shi.
Tun daga qofan farko amintattun hadiman me martaba suke masa iso. Shiga shiga shiga yau sai gashi har qaramin parlor dake manne da bedroom dinsa,parlor din da daga shi sai matansa sai yaransa duk iya tsanin shaquwarka dashi batakai ka iso nan ba.
Da sallama ya shiga,duk da bai sameshi zaune a gurin ba,sai yayi tsaye yana goye da hannuwansa a qirjinsa yana qarewa parlor din kallo a nutse.
Mutum har mutum......mutum ma basarake,me jagorantar dubbai kuma miliyoyin al'umma,ya sarrafa ko wane lamari da sha'ani,amma ya wayi gari cikin juyawa da kuma makircin mace qwaya daya tal. Ya kwashi shekaru cikin duhu,cikin rashin sani da makanta me tarin yawa.
"Yaya zaka tsaya muhammad?,shin ka manta a muhallin mahaifinka kake?" Muryar sultane ya katse masa dogon nazarin da yakeyi.
Wannan murmushin......wannan murmushin mai cike da tarin nutsuwa ya sakar masa. Cikin girmamawa ya furta.
"Barka da fitowa".
"Barka kade Muhammad.......zauna" Sultane ya sake masa tayin zama sanda yake zama shima saman kujerar.
Cikin mutuntawa haisam ya bashi hannu sukayi musabaha me dan tsaho,sultane yana tambayarsa batun tafiyar.
"Tafiya ta kammala.....ta kuma zo da bayanai na abubuwa masu nauyi da girma" Sosai maganar ta sauka a zuciyar sultane cikin wani gurbi na zuciyarsa,sai yaji wani abu yana lullubeshi kasalarsa tana ninkuwa.
"Allah ya tabbatar da dukkan alkhairi" Ya fada haka kawai yana jin zuciyarsa tana laushi.
"Ameen ameen"
"Dukka hadimai sunyi nisa da gurin hidimarsu......akwai duk wani nau'in abu da kake buqata kaci ko kasha daga can" Murmushi haisam yayi kadan,ko yaya mutum me karamci yake sai ya nuna karamcin nan nasa.
"Alhamdulillah,godiya nake" Ya fadi yana sake nuna girmamawarsa a gareshi,shuru ya ratsa na wani dan lokaci,sultane yana jin wani nauyi yana jin akwai abinda ya kawo haisam din,akwai abinda haisam yakesonyin magana akai amma kuma shima ya gagara tambayarsa.
Gyaran muryar haisam taja hankalinsa.
"Allah ya taimakeka.....nace ayimin afuwa,na nema ganinka a lokacin daya kamata ace kana hutawa......Musamman kwana biyun da akace bakajin dadin jikinka". Murmushi yayi mai cike da dattako.
" A duk sanda d'a keson ganin ubansa daidai ne,hakan bazai zama laifi ba sam sam".
"Haka ne.....akwai wata gaskiya ce data jima tana boye......kuma yanzu lokacin boyewarta ya wuce" Yayi maganan a hankali yana duban sultane.
Sanyaya jikinsa yayi,zuciyarsa tana rawa kadan. Fatansa kawai Allah yasa ba wani mummunan abu bane.......fatansa kawai Allah yasa koma meye bai shafi aurensa da akhnan ba.
"Ina jinka muhammad" Ya fadi yana sallamawa cikin ransa.
"Ni ba malami bane kawai kamar yadda ka sani,kamar kuma yadda kowa yake kallona.......ina da wani aiki na daban da nakeyi tun daga qasata". Yakai maganan qarshe shuru yana maye gurbin dakin.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 12*
Wani irin shuru da ya wanzu saboda idanu kawai da sultane ya zubawa haisam. Yana zaton zaiji tsoro ko wata fargaba amma game da maganar haisam da tazo ba zato ba tsammani......yana zaton zaiji wani tashin hankali ya sauko masa amma ba wani sauyi da yaji.
"Na sani......na sani muhammad,koa hankalce bakayi kama da malamin nan ba.....malamin da baida aikin yi,malamin dake komai kara zube ba,na karanceka kafin jawoka jikina.....na karanceka sosai kafin na sanyaka tsakiyar ahalina.....amma ban sani ba,na karanceka gaba daya ne ko bai karanci komai daga kai din waye ba". Yayi maganan da wani iri laushi da hope sosai a muryarsa ba.
"Baka karantani duka ba.....saidai ina me baka albishir ba zakayi nadaman sakani amana cikin ahalinka ba......ba wannan ne abu mafi muhimmanci ba sultane......aikina ya ratsa ta wani bigire.....aikina ya biyo takan wani muhimmin abu cikin rayuwarka".
"Ban damu ba muhammad.......ban damu ba,nagartarka kawai nakeso,muddin ta tabbata bani da matsalar sanin waye kai ko meye aikinka har qarshen numfashi na". Wani nauyi.....nauyi haisam yaji sosai saman zuciyarsa. Ya Allah.....wanne irin yarda da aminci ne wannan?,wacce irin qauna ce wannan?. Ya rabb,kada ya bashi ikon cutar da sultane ko sabawa zatonsa.
"Wanne abune haisam?.....sanar dani" Sultane ya fada yana gyara zamansa.
"D'anka.....d'an ahmad" Idanu sultane ya zuba masa ya kasa cewa komai.
"D'ana ahmad?,d'a kuma jinin farko na safeena da muhammad hammud?" Kai haisam ya jinjina masa yana kallon yadda wasu emotions ke tasiri a tattare dashi.
"Shi......yana raye,bai mutu ba". Wani irin abu sultane yaji ya doka tsakiyar kansa,sai ya dinga jin maganar haisam tana amsa kuwwa a kunnensa.
"Yana nan a raye,lafiya qalau" Ya sake fadi don ya bawa sultane qwarin gwiwar tambayarsa ko sau daya ne.
"Yana ina muhammad?,ahmad fa?,ba irin neman da bamu masa ba,ahmad hatta da safeena duk da zurfin haqurinta ta saddaqar ta rasashi....ahmad dai?" Ya tambaya cike da shakku.
"Ahmad yana raye.....ubangiji yaga dama ya raya abinsa". Yayi furucin a tausashe.
Zumbur yaga sultane ya miqe,ya kama hannuwan haisam sosai cikin nasa yana duban idanun haisam din da nasa idanun,idanuwan da suka cika sosai da ruwan hawayen da jarumta irin nasa ya hana musu kowanne tasiri.
"Ya girma ko?,yayi hankali haisam?,kaini na ganshi,kaini naga ahmad,inama ace safeena tana raye?"
Wani irin tausayinsa me narkar da zuciya ne ya saukarwa haisam,sai ya kama hannuwansa shima,yayi taku uku ya matsa dab da sultane din don bashi kafadar da zai jingina ya samu sassauci.
Kamar yasan me manufar haisam kuwa,sai ya rungume kafadar haisam yana sauke wani irin numfashi,wani numfashi me tsananin nauyin dake bayyana girman tsananin da zuciyarsa ke cikin tsahon shekarun.
Ya tabbatar inda gama garin namiji ne sultane din kuka zai fashe dashi. Ashe duka shekarun nan yana rayuwar kawai,yana maida komai ba komai ba?,amma akwai ciwon rashin ahmad din tattare dashi.
Yadda yaji jikinsa ya fara kyarma sai ya kamashi a nutse ya zaunar dashi,don yasan zuwa yanzu abinda ya bawa me wada ya dinga shayar dashi ya ratsa jikinsa sosai.
"Akwai shaidu ga gwajin qwayoyin halitta.....bari na gabatar maka dasu" Caraf yaji sultane din dake ajiye wani irin numfashi ya riqe hannunsa
"Ba buqata haisam.....na tabbatar yadda akhnan ba zatamin qarya ba,ba zata cutar dani ba hakazalika kaima". Maganan ya sanyashi dakatawa daga warware takardun yana duban sultane da girman yadda da amincewar da yayi masa.
*M A M M I N A*
Ji da ganin komai take kamar a mafarki,an aurar da falaak ana shagulgula dukka cikin gidan ita bata sani ba?
Wai yaushe?,yaushe haka ta faru?,yaushe tayi wannan baccin?,yaushe tayi sake haka..yaushe al'amura suka fara mata sako sako?.
Dab da bayanta ya zura hannu sanda suka isa personal qofanta ta baya.......bata sani ba,ba kuma zatace ba taga ya fidda keya ya zura ya murza ya kuma bude sannan ya turata ta bude. Bata sake jin motsinsa ba saidai tasan yana tsaye a gurin,zuciyarta na sake zugata.
"Kidan waiwaya ko sau daya ki kalleshi.....ki juya ki gani ko shurunsa ke yake bi da kallo". A wani irin sace ta saci kallonsa ta gefan idanunta,sai taga wayarsa ya fidda a aljihu yana latsawa,alamu kuna sun nuna gajeran saqo yake turawa.
Haka kawai taji wani iri.....haka kawai taji ba dadi. Bata taba satar kallon d'a namiji ba a rayuwarta,saidai ita a saci kallonta harma ta hukunta mutum,amma a yau wai itace ke satar kallon wani?. Waninma da ba ita yake kalla ba?,kallon wayarsa yafi kallonta muhimmanci?.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Sai data shige duka sannan ta juyo a hankali,ta kuma sake wayancewa da dora hannunta saman handle tanayi kamar zata rufe qofar. Wannan karon kuma kai tsaye ta zuba masa dukka blue eyes dinta,tanason tabbatarwa da gaske wayar tasa yake kalla har yanzu?.
Tabbacin kuwa ta samu,don yadda yake typing da sauri da sauri ya gaya mata wani saqon gaggawa ne zai aike. Sosai a yanzun taji ranta ya sosu fiye da dazun,sai kawai ta zabi rufe qofar wanda tana dab da hade gap don da yayi saura qofar ta qarasa kullewa ya daga kansa daga wayar,saidai bai samu daman ganin komai ba sai gefan fuskarta da blue eyes dinta guda daya.
Murza muqullin jiki tayi tana jin zuciyarta tana mata zafi,sannan ta juya a hankali tana sake riqe cloak thobe don cikin hannuwanta tana damqeta da kyau kamar wani zai qwace mata.
"Bai kula ba....bai damu ba?" Ta tambayi kanta tana jin ranta yana sake baci,saidai qamshin nan nasa da ya sanya takejin kamar yana dab da ita ya hana bacin ran nata yaci gaba.
A parlor din da yafi kama da harabar da zaka zauna jiran neman izinin ganinta direct daga bedroom dinta ta iske birra. Ta sani koda kowa zai tafi birra zata zauna.
Ta miqe tana nufota da zummar karbar cloake thobe din saman jikinta ta kuma taimaka mata ta sauya kayan jikinta,amma daga idanun da akhnan tayi tana duban birran da gane rigar waye a jikinta ya sanya birra janyewa da baya. Ganin birran ta fahimci abinda takeson fada kafin ta fadi,saita hadiye maganarta ta juya tana wucewa ciki.
Ta jima zaune da rigar jikinta tana kallon yadda ruwa ke zuba ta glass door din data ratsa bangon,kafin a hankali ta zameta daga kafadarta ta miqe don hadata da 'yar uwarta. Wancan rigar daya bata aro wancan karon bata maida masa ba......a yanzu ga wata ta qaru,saita hadesu guri daya tana zubasu cikin wata 'yar jaka. Har yanzun koda rigar farko ma bata daina qamshin da takeyi ba bare riga ta biyu.
*H A I S A M*
Samun tabbacin ta rufe qofar ya sanyashi maida wayar aljihunsa a hankali,ya juya a nutse yana takawa zuwa sassan sultane da yake iya hangowa dab da shi.
Tun daga qofan farko amintattun hadiman me martaba suke masa iso. Shiga shiga shiga yau sai gashi har qaramin parlor dake manne da bedroom dinsa,parlor din da daga shi sai matansa sai yaransa duk iya tsanin shaquwarka dashi batakai ka iso nan ba.
Da sallama ya shiga,duk da bai sameshi zaune a gurin ba,sai yayi tsaye yana goye da hannuwansa a qirjinsa yana qarewa parlor din kallo a nutse.
Mutum har mutum......mutum ma basarake,me jagorantar dubbai kuma miliyoyin al'umma,ya sarrafa ko wane lamari da sha'ani,amma ya wayi gari cikin juyawa da kuma makircin mace qwaya daya tal. Ya kwashi shekaru cikin duhu,cikin rashin sani da makanta me tarin yawa.
"Yaya zaka tsaya muhammad?,shin ka manta a muhallin mahaifinka kake?" Muryar sultane ya katse masa dogon nazarin da yakeyi.
Wannan murmushin......wannan murmushin mai cike da tarin nutsuwa ya sakar masa. Cikin girmamawa ya furta.
"Barka da fitowa".
"Barka kade Muhammad.......zauna" Sultane ya sake masa tayin zama sanda yake zama shima saman kujerar.
Cikin mutuntawa haisam ya bashi hannu sukayi musabaha me dan tsaho,sultane yana tambayarsa batun tafiyar.
"Tafiya ta kammala.....ta kuma zo da bayanai na abubuwa masu nauyi da girma" Sosai maganar ta sauka a zuciyar sultane cikin wani gurbi na zuciyarsa,sai yaji wani abu yana lullubeshi kasalarsa tana ninkuwa.
"Allah ya tabbatar da dukkan alkhairi" Ya fada haka kawai yana jin zuciyarsa tana laushi.
"Ameen ameen"
"Dukka hadimai sunyi nisa da gurin hidimarsu......akwai duk wani nau'in abu da kake buqata kaci ko kasha daga can" Murmushi haisam yayi kadan,ko yaya mutum me karamci yake sai ya nuna karamcin nan nasa.
"Alhamdulillah,godiya nake" Ya fadi yana sake nuna girmamawarsa a gareshi,shuru ya ratsa na wani dan lokaci,sultane yana jin wani nauyi yana jin akwai abinda ya kawo haisam din,akwai abinda haisam yakesonyin magana akai amma kuma shima ya gagara tambayarsa.
Gyaran muryar haisam taja hankalinsa.
"Allah ya taimakeka.....nace ayimin afuwa,na nema ganinka a lokacin daya kamata ace kana hutawa......Musamman kwana biyun da akace bakajin dadin jikinka". Murmushi yayi mai cike da dattako.
" A duk sanda d'a keson ganin ubansa daidai ne,hakan bazai zama laifi ba sam sam".
"Haka ne.....akwai wata gaskiya ce data jima tana boye......kuma yanzu lokacin boyewarta ya wuce" Yayi maganan a hankali yana duban sultane.
Sanyaya jikinsa yayi,zuciyarsa tana rawa kadan. Fatansa kawai Allah yasa ba wani mummunan abu bane.......fatansa kawai Allah yasa koma meye bai shafi aurensa da akhnan ba.
"Ina jinka muhammad" Ya fadi yana sallamawa cikin ransa.
"Ni ba malami bane kawai kamar yadda ka sani,kamar kuma yadda kowa yake kallona.......ina da wani aiki na daban da nakeyi tun daga qasata". Yakai maganan qarshe shuru yana maye gurbin dakin.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 12*
Wani irin shuru da ya wanzu saboda idanu kawai da sultane ya zubawa haisam. Yana zaton zaiji tsoro ko wata fargaba amma game da maganar haisam da tazo ba zato ba tsammani......yana zaton zaiji wani tashin hankali ya sauko masa amma ba wani sauyi da yaji.
"Na sani......na sani muhammad,koa hankalce bakayi kama da malamin nan ba.....malamin da baida aikin yi,malamin dake komai kara zube ba,na karanceka kafin jawoka jikina.....na karanceka sosai kafin na sanyaka tsakiyar ahalina.....amma ban sani ba,na karanceka gaba daya ne ko bai karanci komai daga kai din waye ba". Yayi maganan da wani iri laushi da hope sosai a muryarsa ba.
"Baka karantani duka ba.....saidai ina me baka albishir ba zakayi nadaman sakani amana cikin ahalinka ba......ba wannan ne abu mafi muhimmanci ba sultane......aikina ya ratsa ta wani bigire.....aikina ya biyo takan wani muhimmin abu cikin rayuwarka".
"Ban damu ba muhammad.......ban damu ba,nagartarka kawai nakeso,muddin ta tabbata bani da matsalar sanin waye kai ko meye aikinka har qarshen numfashi na". Wani nauyi.....nauyi haisam yaji sosai saman zuciyarsa. Ya Allah.....wanne irin yarda da aminci ne wannan?,wacce irin qauna ce wannan?. Ya rabb,kada ya bashi ikon cutar da sultane ko sabawa zatonsa.
"Wanne abune haisam?.....sanar dani" Sultane ya fada yana gyara zamansa.
"D'anka.....d'an ahmad" Idanu sultane ya zuba masa ya kasa cewa komai.
"D'ana ahmad?,d'a kuma jinin farko na safeena da muhammad hammud?" Kai haisam ya jinjina masa yana kallon yadda wasu emotions ke tasiri a tattare dashi.
"Shi......yana raye,bai mutu ba". Wani irin abu sultane yaji ya doka tsakiyar kansa,sai ya dinga jin maganar haisam tana amsa kuwwa a kunnensa.
"Yana nan a raye,lafiya qalau" Ya sake fadi don ya bawa sultane qwarin gwiwar tambayarsa ko sau daya ne.
"Yana ina muhammad?,ahmad fa?,ba irin neman da bamu masa ba,ahmad hatta da safeena duk da zurfin haqurinta ta saddaqar ta rasashi....ahmad dai?" Ya tambaya cike da shakku.
"Ahmad yana raye.....ubangiji yaga dama ya raya abinsa". Yayi furucin a tausashe.
Zumbur yaga sultane ya miqe,ya kama hannuwan haisam sosai cikin nasa yana duban idanun haisam din da nasa idanun,idanuwan da suka cika sosai da ruwan hawayen da jarumta irin nasa ya hana musu kowanne tasiri.
"Ya girma ko?,yayi hankali haisam?,kaini na ganshi,kaini naga ahmad,inama ace safeena tana raye?"
Wani irin tausayinsa me narkar da zuciya ne ya saukarwa haisam,sai ya kama hannuwansa shima,yayi taku uku ya matsa dab da sultane din don bashi kafadar da zai jingina ya samu sassauci.
Kamar yasan me manufar haisam kuwa,sai ya rungume kafadar haisam yana sauke wani irin numfashi,wani numfashi me tsananin nauyin dake bayyana girman tsananin da zuciyarsa ke cikin tsahon shekarun.
Ya tabbatar inda gama garin namiji ne sultane din kuka zai fashe dashi. Ashe duka shekarun nan yana rayuwar kawai,yana maida komai ba komai ba?,amma akwai ciwon rashin ahmad din tattare dashi.
Yadda yaji jikinsa ya fara kyarma sai ya kamashi a nutse ya zaunar dashi,don yasan zuwa yanzu abinda ya bawa me wada ya dinga shayar dashi ya ratsa jikinsa sosai.
"Akwai shaidu ga gwajin qwayoyin halitta.....bari na gabatar maka dasu" Caraf yaji sultane din dake ajiye wani irin numfashi ya riqe hannunsa
"Ba buqata haisam.....na tabbatar yadda akhnan ba zatamin qarya ba,ba zata cutar dani ba hakazalika kaima". Maganan ya sanyashi dakatawa daga warware takardun yana duban sultane da girman yadda da amincewar da yayi masa.
*M A M M I N A*
Ji da ganin komai take kamar a mafarki,an aurar da falaak ana shagulgula dukka cikin gidan ita bata sani ba?
Wai yaushe?,yaushe haka ta faru?,yaushe tayi wannan baccin?,yaushe tayi sake haka..yaushe al'amura suka fara mata sako sako?.