Sashe 161
LUu Luu Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haka kawai cikin jikinsa yakejin idanunta,sai ya dago kai a nutse yana dubanta. Tarar da ita yayi ba ta aikin,ba kuma karatu takeyi ba. Bata komai,kawai ta tattara dukka idanunta da nutsuwarta a kansa,kallonsa kawai take yi,zara zaran eyelashes dinsa dake motsawa a hankali saman takardun suna sake sanyawa tanaji yana sake burgeta.
"Me?" Ya tambaya a hankali.
"Nothing." Ta fadi murmushi yana subuce mata a hankali
"Akhnan." Ya kirata da sautin dake nuni da kada ki sake kiyimin qarya.
"Ina tunanin..." Ta yi murmushi.
"...yadda yaranmu zasu yi." Sai ya tsaya cak,takardun da ke hannunsa suka rasa muhimmanci na dan lokaci.
Ajjiyesu yayi a hankali yana fuskantar inda maganarta ta dosa.
"Akhnan" Ya sake kiranta a tausashe.
"Kina tunanin......inda za'a bani zabin qwace komai dana mallaka.....a barmin ke da yaran da zaki haifamin.....bazan zabi zama matalauci daya mallaki kyakkyawar gimbiya da yaran da suka haifa ba?" Maganan ta sauka a zuciyarta da kunnenta da wani irin laushi daya tilasta mata lumshe idanunta gami da budesu.
"Naji tsoro....." Ya bude idanunsa duka yana dubanta.
"Naji tsoro sanda na fahimci zuciyata ta fara sonka a sanda kai ko kallo ban isheka ba. Naji tsoro sanda na fahimci na fada tarkon qaunarka. Naji tsoron rasa kimata.....darajata da martabata. Ashe abinda ban sani ba,wannan soyayyar....wannan son shine silar da zai fidda rayuwata daga duhu zuwa haske.....wannan son shine zai mallaka min LU'U LU'UN dake gabana.....LU'U LU'UN da nake shirin tattakeshi da qafata ba tare dana gane shi bane". Ta cikin idanunta kadai ya fahimci dukkanin gaskiyarta. Ta cikin idanunta kawai ya fahimci gaskiyarta kenan take fada daga zuciyarta. Sai kawai ya ture kujerarsa baya,ya miqe a hankali yana takowa.
Idanu ta fidda kadan murmushi yana subuce mata.
"Me?,ina zaka?" Ta tambaya tana sake fidda blue eyes dinnan nata da suka sake girma.
"I've missed your warmth..."
Ya furta a hankali yayin da ya yi mata rumfa da hannayensa a saman kujerar da take zaune. Idanunsa suka sauka kan nata da wani irin yanayi me sanyi.
"Let me stay here for a moment." Ya fada sanda yake mata rumfa saman kujerar da take zaune akai.
"Haisammm" Ta fada da wannan yanayin da yakeso.
"Akhnan" Shima ya furta da wata sirrintacciyar murya yana sake hade tazarar dake tsakaninsu.
"Aikin....." Bai bari ta qarasa ba,ya toshe mata bakinta da nasa.
★Watanni sun yi nisa. Cikin Akhnan ya kai girman da ko juyawa a bacci sai ta yi tunani kafin ta motsa.
Wani yanayin da ita kanta yake bata tsoro,saidai tana dannewa ne kawai saboda yadda hankalin haisam gaba daya ya tattara a kanta.
Karfe biyu na dare,gidan gaba daya ya yi shiru. Wani irin shuru me nutsuwa. Ba abinda kake ji sai sautin motsin security da suke kwana aikinsu cikin gidan kafin safiya wasu su canjesu.
A hankali ta farka. Wani irin yunwa ce ta tashe ta daga baccin daya dauketa tun dazu,batasan ma ya akayi haisam ya maidota daki ba. Wani irin nauyin bacci takeyi,ta kwanta da wayarta a hannu tana lissafa EDD dinta. Sati shida ne ya mata saura a yadda scanning da calendar yake nuna mata.
Ta yunqura tayi qoqarin tashi ba tare da ta tashi haisam ba.
A hankali ta zame daga jikinsa,bataso ta farkar dashi,bataso ta hanashi baccinsa,saboda yini yake yana ayyuka biyu. Tata hidimar,da kuma hidimar kamfani. Duk da wani lokaci yana rikida ya koma dan binciken sirri boyayyen aikinsa da duniya batasan dashi ba.
Saidai amma kafin qafarta ta taba qasa,muryarsa ta fito daga dim light din dakin.
"Ina za ki?" Tadan firgita kadan,saboda yadda tayi takatsantsan gurin tashi batayi zaton zai ji barinta jikinsa haka da wuri ba. Ta yi rolling eyes dinta tana sauke numfashi a hankali.
"Ina jin yunwa." Maganan ta sanya ya bude idanunsa gaba daya a hankali. Sai yaji kaman shine sila. A dazun sai data tabbatar ta gama kaishi duniyar da yakeso kafin su koma parlor inda a nan bacci ya dauketa,sai shine ya dauketa cancakat ita da cikin,yana takawa da takatsantsan saboda yadda ta ninka nauyinta. Sai a sannan ya sake kallonta da kyau,tausayinta yana ratsashi a hankali. Cikin bai mata muni ba.....amma kuma komai na halittarta ya canza. Ya sani,tana jin jiki koda bata fada ba,tsabar juriya ce irin tata da bai taba zata tana da ita ba,musamman idan ya tuna first night dinsu,sai gashi tana shirin bashi mamaki.
Wannan ya sanya yayi booking medical team qasa uku,duk inda ta fada kota kama zasuje. Bai gaya mata Cs bane,saboda bayaso hankalinta ya daga kafin lokacin. Baya so hankalinta ya tashi ko kadan,ko a jiya da sukayi waya da likitocin yana jiran date ne kawai na randa zasu cire mata cikin. Yanaso ya ganta ta huta hakanan,yanaso ta koma akhnan dinnan daya sani.💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 148*
Bude idanunsa yayi gaba daya a wannan karon.
"Yanzu kika fara jin yunwar?"
"Eh." Ta amsa masa a shagwabe.
"Karfe biyu na dare,me yasa baki tasheni ba?" Ya fada yana miqewa zaune sanye da fari qal din wandon pyjamas
"Ni ba agogo ya tashe ni ba." Ta fada tana narai narai da idanu ta cikin hasken fitilar daya kunna ta gefan gado. Sai ya yi dariya kadan,ya kama kumatunta ya danja a tausashe
"Me kike so acici?" Ya tambayeta
"Ban sani ba." Ta fada qwallar nason gangaro mata.
"Wonderful." Ya fadi yana sanya yatsansa ya dauke mata qwallar kafin takai ga zubowa. Lips dinsa ya dora saman goshinta,yayi kissing nata softly,sai yaci gaba da barin lips din nasa saman nan yana sauke mata lallausan numfashinsa a nutse saman goshinta.
Wani irin nutsuwa hakan ya saukar mata,bai janye ba sai daya tabbatar zuciyarta ta sassauta.
"I'm sorry.....kiyi haquri,Allah yana tare dake,kowacce rana qwaya daya tal tarin lada kike samu,double lada saboda yara biyu ne a jikinki.....ke din 'yar aljanna ce in sha Allah". Maganan ya sake sanyawa zuciyarta tayi wani irin taushi,ya miqe ya kama hannunta a nutse yana sauko da ita daga saman gadon.
Minti goma bayan haka,akhnan na zaune a kitchen island. Blanket ne a kafadunta wanda haisam ya lulluba mata don taji dadin zaman,da kuma sanyi sanyin daren da akayi ruwa a cikinsa dake ratso kitchen din.
Haisam kuwa,wanda manyan kamfanoni ke jiransa safe,yana tsaye yana binciken fridge. Kai ba zaka ce shine wannan zakin ba.....wannan malamin.....wannan attajirin.....wannan yariman da number dinsa ke kadawa cikin manyan diyan jinin sarauta da duniya ke alfahari dasu.
"Fruit?" Ya waiwayo yana tambayarta gami da d'age girarsa sama.
"A'a." Ta fadi da shagwaba tana bubbuga qafafunta a qasa. Sai ya maida kansa ga fridge din yana ci gaba da bincikawa.
Sake waiwayowa yayi yana dubanta da fararen idanunsa.
"Yogurt?"
"A'a." Ta sake amsa masa tana maqale kafadarta.
"Soup?" Ya sake tambaya bayan ya sake bincikawa.
"A'a."
"Akhnan." Ya fada yana miqewa tsaye daga tsugunnon da yayi yana waiwayowa dukka gareta. Dariya ta fara yi,wata boyayyar dariyar da haisam yake iya ganeta nan da nan duk da boyetan da take qoqarin yi.
"Ban sani ba ne." Ta fada tana langabar da kai cikin yin kalar abun tausayi.
"Two babies woke me up for this." Ya fada da muryar tausayi shima,sai ya ci gaba da bincike cikin fridge din.
A qarshe ya fahimci ta shirya wahalar dashi ne,don haka bai sake tambaya ba ya shiga hada mata wasu abubuwa.
"Bismillah" Ya fada yana dora mata saman island din,sannan yaja kujera ya zauna opposite nata.
Yatsina fuska kadan tayi,ta saka spoon cikin bowl din.
Ta saka na farko a bakinta,ta tauna,sai ta tsaya.
"Hmm."
Ya daga kansa yana dubanta sosai.
"What?"
"This." Ta nuna plate din.
"This is exactly what I wanted." Sai ya tsaya kawai yana kallonta.
"You just said you didn't know what you wanted."
"Ban sani ba sai da na gani." Ta fada tana sake kai loma bakinta hankali kwance tana lumshe idanunta.
Ya kalli ceiling kamar yana neman taimakon Allah. Sai wata irin dariya ta subuce mata,ta dara sosai har fararen jerarrun haqoranta suna fitowa reras.
Kai kawai ya girgiza,yaci gaba da kallonta tana cin abinta hankali kwance har ta kammala. Ta gyara zamanta sosai cikin dabara kaman yadda ta saba tana kallonsa.
"Sorry." Ta fada tana kama kunnuwanta.
"For what?" Ya tambaya yana dage dukka girarsa biyun.
"For waking you." Sai ya kalleta,sannan ya sauke idanunsa kan cikinta.
"If you wake me ten times a night..." Ya tsaya da wannan nutsuwar tasa.
"...and it means you and my children are okay..." Ya girgiza kai
"I'll get up all ten times." Shuru tayi,zuciyarta na narkewa,sai ya matsa kusa da ita,ya gyara mata blanket din da ke kafadarta.
"Now finish that."
"Na koshi."
"Akhnan." Ya kirata da wannan yanayin me nauyi.
"Haisam." Itama ta kirashi,kamar kowannensu iyayensa sun saka musu wannan sunan ne saboda dan uwansa. Ba gurin wanda suke jin dadin sunayen sai a bakin daya daga cikinsu.
"One more bite." Ya fada yana daga yatsansa guda daya
Sai ta yi dariya. Saboda yanzu ta gane wani abu.
Tun da cikin ya girma......ba nanay kadai suke takurawa ba....haisam ma ya shiga qungiyar kula da ita da cikakken lokacinsa.
Tana motsawa saqo yana shigowa wayarta,haisam yabi wayar da kallo sanda take dauka. Kaman zai hanata sai kuma ya qyaleya,taci abinci,yanzun nan idan 'yan rigimar suka motsa saita narke masa hannun agogo ya koma baya.
Idanunta dukka ta fidda waje tana kallon haisam bayan ta janye idanunta daga kan wayar. Tana jin kamar tayi ihu ne,amma kuma tasan dare ne.
"Falaak my prince.....falaak ta sauka......ta samu baby girl.....maleek ya zama daddy before you" Ba haihuwar bace ta burgeshi. Yadda take maganan idanunta da suka sake girma da haske a waje. Yadda excitement dinta ya nuna,sai yaji kawai yana dokin zuwan ranar da zata riqe nata babies din.
"Next week sunan falaak.....next week bikin shehnaz......aisa....rumaisa da Aanani. Yaa muhammad.....ya ahmad......the whole next week is for us".
Shikam kallonta yake kawai yana zaune,ya nannade hannunsa a qirjinsa.
Mamakinta kawai yake,bata ko jin nauyin abinda ke jikinta take tunanin bukukuwa da suna. Yana jinta tun jiya take lissafa events events,wanda bayajin ko daya zai barta. Bazaima yarda da zamanta ciki wannan hayaniyar bikin ba sam sam.
"Come,let's go to bed my princess" Sai taji ya dagata cak tana tsaka da surutunta.
"Me?" Ya tambaya a hankali.
"Nothing." Ta fadi murmushi yana subuce mata a hankali
"Akhnan." Ya kirata da sautin dake nuni da kada ki sake kiyimin qarya.
"Ina tunanin..." Ta yi murmushi.
"...yadda yaranmu zasu yi." Sai ya tsaya cak,takardun da ke hannunsa suka rasa muhimmanci na dan lokaci.
Ajjiyesu yayi a hankali yana fuskantar inda maganarta ta dosa.
"Akhnan" Ya sake kiranta a tausashe.
"Kina tunanin......inda za'a bani zabin qwace komai dana mallaka.....a barmin ke da yaran da zaki haifamin.....bazan zabi zama matalauci daya mallaki kyakkyawar gimbiya da yaran da suka haifa ba?" Maganan ta sauka a zuciyarta da kunnenta da wani irin laushi daya tilasta mata lumshe idanunta gami da budesu.
"Naji tsoro....." Ya bude idanunsa duka yana dubanta.
"Naji tsoro sanda na fahimci zuciyata ta fara sonka a sanda kai ko kallo ban isheka ba. Naji tsoro sanda na fahimci na fada tarkon qaunarka. Naji tsoron rasa kimata.....darajata da martabata. Ashe abinda ban sani ba,wannan soyayyar....wannan son shine silar da zai fidda rayuwata daga duhu zuwa haske.....wannan son shine zai mallaka min LU'U LU'UN dake gabana.....LU'U LU'UN da nake shirin tattakeshi da qafata ba tare dana gane shi bane". Ta cikin idanunta kadai ya fahimci dukkanin gaskiyarta. Ta cikin idanunta kawai ya fahimci gaskiyarta kenan take fada daga zuciyarta. Sai kawai ya ture kujerarsa baya,ya miqe a hankali yana takowa.
Idanu ta fidda kadan murmushi yana subuce mata.
"Me?,ina zaka?" Ta tambaya tana sake fidda blue eyes dinnan nata da suka sake girma.
"I've missed your warmth..."
Ya furta a hankali yayin da ya yi mata rumfa da hannayensa a saman kujerar da take zaune. Idanunsa suka sauka kan nata da wani irin yanayi me sanyi.
"Let me stay here for a moment." Ya fada sanda yake mata rumfa saman kujerar da take zaune akai.
"Haisammm" Ta fada da wannan yanayin da yakeso.
"Akhnan" Shima ya furta da wata sirrintacciyar murya yana sake hade tazarar dake tsakaninsu.
"Aikin....." Bai bari ta qarasa ba,ya toshe mata bakinta da nasa.
★Watanni sun yi nisa. Cikin Akhnan ya kai girman da ko juyawa a bacci sai ta yi tunani kafin ta motsa.
Wani yanayin da ita kanta yake bata tsoro,saidai tana dannewa ne kawai saboda yadda hankalin haisam gaba daya ya tattara a kanta.
Karfe biyu na dare,gidan gaba daya ya yi shiru. Wani irin shuru me nutsuwa. Ba abinda kake ji sai sautin motsin security da suke kwana aikinsu cikin gidan kafin safiya wasu su canjesu.
A hankali ta farka. Wani irin yunwa ce ta tashe ta daga baccin daya dauketa tun dazu,batasan ma ya akayi haisam ya maidota daki ba. Wani irin nauyin bacci takeyi,ta kwanta da wayarta a hannu tana lissafa EDD dinta. Sati shida ne ya mata saura a yadda scanning da calendar yake nuna mata.
Ta yunqura tayi qoqarin tashi ba tare da ta tashi haisam ba.
A hankali ta zame daga jikinsa,bataso ta farkar dashi,bataso ta hanashi baccinsa,saboda yini yake yana ayyuka biyu. Tata hidimar,da kuma hidimar kamfani. Duk da wani lokaci yana rikida ya koma dan binciken sirri boyayyen aikinsa da duniya batasan dashi ba.
Saidai amma kafin qafarta ta taba qasa,muryarsa ta fito daga dim light din dakin.
"Ina za ki?" Tadan firgita kadan,saboda yadda tayi takatsantsan gurin tashi batayi zaton zai ji barinta jikinsa haka da wuri ba. Ta yi rolling eyes dinta tana sauke numfashi a hankali.
"Ina jin yunwa." Maganan ta sanya ya bude idanunsa gaba daya a hankali. Sai yaji kaman shine sila. A dazun sai data tabbatar ta gama kaishi duniyar da yakeso kafin su koma parlor inda a nan bacci ya dauketa,sai shine ya dauketa cancakat ita da cikin,yana takawa da takatsantsan saboda yadda ta ninka nauyinta. Sai a sannan ya sake kallonta da kyau,tausayinta yana ratsashi a hankali. Cikin bai mata muni ba.....amma kuma komai na halittarta ya canza. Ya sani,tana jin jiki koda bata fada ba,tsabar juriya ce irin tata da bai taba zata tana da ita ba,musamman idan ya tuna first night dinsu,sai gashi tana shirin bashi mamaki.
Wannan ya sanya yayi booking medical team qasa uku,duk inda ta fada kota kama zasuje. Bai gaya mata Cs bane,saboda bayaso hankalinta ya daga kafin lokacin. Baya so hankalinta ya tashi ko kadan,ko a jiya da sukayi waya da likitocin yana jiran date ne kawai na randa zasu cire mata cikin. Yanaso ya ganta ta huta hakanan,yanaso ta koma akhnan dinnan daya sani.💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 148*
Bude idanunsa yayi gaba daya a wannan karon.
"Yanzu kika fara jin yunwar?"
"Eh." Ta amsa masa a shagwabe.
"Karfe biyu na dare,me yasa baki tasheni ba?" Ya fada yana miqewa zaune sanye da fari qal din wandon pyjamas
"Ni ba agogo ya tashe ni ba." Ta fada tana narai narai da idanu ta cikin hasken fitilar daya kunna ta gefan gado. Sai ya yi dariya kadan,ya kama kumatunta ya danja a tausashe
"Me kike so acici?" Ya tambayeta
"Ban sani ba." Ta fada qwallar nason gangaro mata.
"Wonderful." Ya fadi yana sanya yatsansa ya dauke mata qwallar kafin takai ga zubowa. Lips dinsa ya dora saman goshinta,yayi kissing nata softly,sai yaci gaba da barin lips din nasa saman nan yana sauke mata lallausan numfashinsa a nutse saman goshinta.
Wani irin nutsuwa hakan ya saukar mata,bai janye ba sai daya tabbatar zuciyarta ta sassauta.
"I'm sorry.....kiyi haquri,Allah yana tare dake,kowacce rana qwaya daya tal tarin lada kike samu,double lada saboda yara biyu ne a jikinki.....ke din 'yar aljanna ce in sha Allah". Maganan ya sake sanyawa zuciyarta tayi wani irin taushi,ya miqe ya kama hannunta a nutse yana sauko da ita daga saman gadon.
Minti goma bayan haka,akhnan na zaune a kitchen island. Blanket ne a kafadunta wanda haisam ya lulluba mata don taji dadin zaman,da kuma sanyi sanyin daren da akayi ruwa a cikinsa dake ratso kitchen din.
Haisam kuwa,wanda manyan kamfanoni ke jiransa safe,yana tsaye yana binciken fridge. Kai ba zaka ce shine wannan zakin ba.....wannan malamin.....wannan attajirin.....wannan yariman da number dinsa ke kadawa cikin manyan diyan jinin sarauta da duniya ke alfahari dasu.
"Fruit?" Ya waiwayo yana tambayarta gami da d'age girarsa sama.
"A'a." Ta fadi da shagwaba tana bubbuga qafafunta a qasa. Sai ya maida kansa ga fridge din yana ci gaba da bincikawa.
Sake waiwayowa yayi yana dubanta da fararen idanunsa.
"Yogurt?"
"A'a." Ta sake amsa masa tana maqale kafadarta.
"Soup?" Ya sake tambaya bayan ya sake bincikawa.
"A'a."
"Akhnan." Ya fada yana miqewa tsaye daga tsugunnon da yayi yana waiwayowa dukka gareta. Dariya ta fara yi,wata boyayyar dariyar da haisam yake iya ganeta nan da nan duk da boyetan da take qoqarin yi.
"Ban sani ba ne." Ta fada tana langabar da kai cikin yin kalar abun tausayi.
"Two babies woke me up for this." Ya fada da muryar tausayi shima,sai ya ci gaba da bincike cikin fridge din.
A qarshe ya fahimci ta shirya wahalar dashi ne,don haka bai sake tambaya ba ya shiga hada mata wasu abubuwa.
"Bismillah" Ya fada yana dora mata saman island din,sannan yaja kujera ya zauna opposite nata.
Yatsina fuska kadan tayi,ta saka spoon cikin bowl din.
Ta saka na farko a bakinta,ta tauna,sai ta tsaya.
"Hmm."
Ya daga kansa yana dubanta sosai.
"What?"
"This." Ta nuna plate din.
"This is exactly what I wanted." Sai ya tsaya kawai yana kallonta.
"You just said you didn't know what you wanted."
"Ban sani ba sai da na gani." Ta fada tana sake kai loma bakinta hankali kwance tana lumshe idanunta.
Ya kalli ceiling kamar yana neman taimakon Allah. Sai wata irin dariya ta subuce mata,ta dara sosai har fararen jerarrun haqoranta suna fitowa reras.
Kai kawai ya girgiza,yaci gaba da kallonta tana cin abinta hankali kwance har ta kammala. Ta gyara zamanta sosai cikin dabara kaman yadda ta saba tana kallonsa.
"Sorry." Ta fada tana kama kunnuwanta.
"For what?" Ya tambaya yana dage dukka girarsa biyun.
"For waking you." Sai ya kalleta,sannan ya sauke idanunsa kan cikinta.
"If you wake me ten times a night..." Ya tsaya da wannan nutsuwar tasa.
"...and it means you and my children are okay..." Ya girgiza kai
"I'll get up all ten times." Shuru tayi,zuciyarta na narkewa,sai ya matsa kusa da ita,ya gyara mata blanket din da ke kafadarta.
"Now finish that."
"Na koshi."
"Akhnan." Ya kirata da wannan yanayin me nauyi.
"Haisam." Itama ta kirashi,kamar kowannensu iyayensa sun saka musu wannan sunan ne saboda dan uwansa. Ba gurin wanda suke jin dadin sunayen sai a bakin daya daga cikinsu.
"One more bite." Ya fada yana daga yatsansa guda daya
Sai ta yi dariya. Saboda yanzu ta gane wani abu.
Tun da cikin ya girma......ba nanay kadai suke takurawa ba....haisam ma ya shiga qungiyar kula da ita da cikakken lokacinsa.
Tana motsawa saqo yana shigowa wayarta,haisam yabi wayar da kallo sanda take dauka. Kaman zai hanata sai kuma ya qyaleya,taci abinci,yanzun nan idan 'yan rigimar suka motsa saita narke masa hannun agogo ya koma baya.
Idanunta dukka ta fidda waje tana kallon haisam bayan ta janye idanunta daga kan wayar. Tana jin kamar tayi ihu ne,amma kuma tasan dare ne.
"Falaak my prince.....falaak ta sauka......ta samu baby girl.....maleek ya zama daddy before you" Ba haihuwar bace ta burgeshi. Yadda take maganan idanunta da suka sake girma da haske a waje. Yadda excitement dinta ya nuna,sai yaji kawai yana dokin zuwan ranar da zata riqe nata babies din.
"Next week sunan falaak.....next week bikin shehnaz......aisa....rumaisa da Aanani. Yaa muhammad.....ya ahmad......the whole next week is for us".
Shikam kallonta yake kawai yana zaune,ya nannade hannunsa a qirjinsa.
Mamakinta kawai yake,bata ko jin nauyin abinda ke jikinta take tunanin bukukuwa da suna. Yana jinta tun jiya take lissafa events events,wanda bayajin ko daya zai barta. Bazaima yarda da zamanta ciki wannan hayaniyar bikin ba sam sam.
"Come,let's go to bed my princess" Sai taji ya dagata cak tana tsaka da surutunta.