Sashe 36
LUu Luu Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Akanme?.....ni bazai faru dani ba bare na nemi sani,kema Allah ya baki lafiya ke kika jama kanki" Ta fada tana yamutsa fuska. A yadda taga falaak din a yamutse saboda abu qwaya daya tak ita saita bari ya faru da ita?.
"Duk fa wayon amarya sai ansha man ta.....kin manta?"
"Falaak.....ki kama kanki" Ta fada tana tsumewa
"Inacan tausayinki kamar zai hallakani,amma ke alfahari ma kike da abun?". Ta fada a qufule
"Dole nayi alfahari mana....nakai mutuncina gidan mijina,mijina na sunnah ne ya karbu budurcina abun alfahari ne yaa biftu,ina fata kema ya faru a kanki zakifi fahimta" Ta fada a ranta amma a fili sai tayi qasa da kanta tana cewa.
"Kiyi haquri na daina"
Knocking akayi aka turo ana shigowa,maleek ne,sai a sannan akhnan taga basarwar da yaketayi,sai yanzu ta fahimta
"Mugu" Ta fada qasan ranta tana jin haushinsa yana saukar mata. Wayarta ya ajiye mata a gefe yana cewa.
"Captain yace ki duba akwai saqo".
"Captain?" Ta maimaita tana daukan wayar,don sunan baqo ne a kunnuwanta,bata ma kuma gane wanene ba.
Procedures ne na yadda falaak zata samu relief a rubuce cikin wayar ya rubuta ya ajiye a notebook dinta. Kunya taji ta kamata sosai gauraye da haushi,har shima wai yasan meye ya faru ne?,kawa saita dan kai idanunta kansu maleek.
Yadda ya gwaggwafe gaban falaak din riqe da yatsunta yana murzawa,har ita dake gurin bata iyajin abinda yake gaya mata ya aza mata nauyi da yawa,kawai sai taji ba zata iya zama ba,ta miqe tsam,daidai sanda yake fadin.
"Tanti....ki zauna fita zanyi"
"No" Tace a taqaice kawai tana takawa gami da ficewa a dakin.
*_A G A D E Z_*
*_SULTANE PALACE_*
Zaune take a gabansa cikin nannauyar kwalliyar na dake cike da alfahari da kuma nuna isa,kwalliyar data qara adadin nauyinta don ta boye ramar data fara yi wadda ta bayyana kadan har a qasusuwan wuyanta.
Tun daga watannin baya,ranar da gobara ta tashi a gidan. Bacewar tamim.....bacewar yalwa,gobarar villa dama dauki daidai din da akewa hadimanta,har xuwa ranar qarshe da 'yan jarida suka dirar mata bata sake baccin kirki ba.
Kaman zatayi sanyi,kaman zatayi collapse,kaman zata saddaqar amma kuma zuciyarta ta gaya mata KI TASHI ZAITUNA!.
Wani irin salo take gani tattare da yaron da dawowarsa yafi haihuwarsa zame mata barazana a rayuwarta. AHMAD yaron data kowacce fuska baka isa ga qaryata jinin sultane bane a jikinsa.
Bai rayu dasu ba....bai rayu cikin masarautar ba......amma yasan kowanne nau'in salon sarautarsu.....lungu da saqo na cikin gidan.....adadin ma'aikata dama komai dake wanzuwa a cikin gidan. Batayi mamaki ba.....kasancewar ALSAAMIT tattare dashi zai iya zama mafi girman hatsari fiye da haka.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Wani irin takawa d'ai d'ai taga kaman morsa safiyya tanayi.....wani irin girma ta fuskanci kanta yanayi......abinda ya hanata bacci darare da yawa.....saidai kuma ta samu babban makama sanda ta soma lura da rade radin da kuma gani da tayi da idanunta SULTANE bashi da wani cikakken qwari da lafiya.
Murmushi tayi sanda ta lura da wannan
"Wataqila ina da sauran dama ne.....daman da zata zamemin ta qarshe" Ta kama damar da kyau kuwa,ta fara kusanta kanta da sultane matuqar kusantawa. Abinda ya bata mamaki yadda take samun cikakken dama da access da komai,saidai cikas kadan kadan da take samu daga ahmad din.
Yaron da idan hanya ta hadasu yake mata wani irin kallo,kallon data tabbatar idan har yana da dama.....idan har zai yuwu zai iya daukan wuqa ya kaita lahira.
"Ta yaro kyau take bata qarko..... Ka daina dariya wasa yayi kyau.....wannan zaqin mulkin......wannan darajar da wannan matsayin gaba daya na 'yan kwanaki zuwa watanni ne....zaka sake bacewa bacewar da har abada ba zaka dawo ba" Haka takan fadi cikin ranta,amma a fili saita bishi da murmushi.
Kamar yanzu da take zaune gaban sultane din,tana yanka masa fruit din tana bashi yana sha,tana kuma jansa da hira a nutse.
Tun daga nesa ta hangesu,morsa safiyya ce cikin wata irin shigar kamala dake bayyanar da darajarta da wani irin Kwarjini. Ahmad yana biye da ita a baya da wani kalan girmamawa tamkar yana fadawa duniya ITADIN MAKWAFIN MAHAIFIYATA CE.
Ta zuba musu idanu da gaske,har cikin tsakiyar zuciyarta tana jin wani irin zugi a duk sanda ta gansu a haka. Dawowarsa ta sake qarawa morsa safiyya wani irin girma da martaba da bata zata ba,saboda kowa kiranta yake UWAR YARIMA ME JIRAN GADO.
Duk kuwa da yadda taso sunan ya zamana nata ne.....ko ta hana tasirin sunan,amma ko daya a ciki bata samu nasara ba.
Akwai tarin mutane masu yawan gaske dake neman kusanci da Ahmed din,wanda kusancin yana da muhimmancin da dole kowa ya buqaci wannan gurbin a kusa dashi.
A zahiri saita saki fuskarta,tana maida dubanta ga sultane da bai lura da tahowarsu ba.
"Ga magaji nan zuwa shida mamarsa". Kansa ya daga zuwa sashen,yana duban Ahmad yana jin wani abu me girma yana motsawa cikin zuciyarsa. Baisan dame zai yiwa haisam sakayya ba....duk da har yanzu baisan yadda komai ya kasa ce ba har yanzu.
Murmushi kawai yake saki har suka iso,murmushin da mammina take jinsa kamar tsiruwar allura saman naman zuciyarta.
"Barka da hutawa" Morsa safiyya ta fada tana cire takalmanta a girmame tana qarasowa gabansa.
"Bakanki uwar yarima" Murmushi ya subuce mata tayi qas da kanta,yanayin da ya masa kama sosai da safeena.
"Da kanka me martaba?"
"Sunan ya dace da wadda aka bawa ai......ga maman gimbiya....ke kuma ta yarima ce" Ya fada yana nuna mammina data qaqalo murmushin dole. Idanu morsa safiyya ta daga ta kalli mammina,cikin sa'a ita ita take kalla,sai kawai safiyyan ta ajewa mamminan murmushi tana dauke kanta. A yanzun bataga komai tattare da mammina ba sai wata kwantacciyar damuwa,damuwar da duk dare saita tsaya saman abun sallah ta kaiwa Allah sunanta. Allah ya hanawa rayuwarta sukuni muddin da haqqin safeena saman wuyanta.
"Zamankin nan a gabana.....sai naga kaman safeena ce" Ya fada zuciyarsa tana masa nauyi.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 34*
"Allah ya tsinewa safeena da kabarinta dama dukkan abinda ya fito ta tsatsonta dama ahalinta gaba daya" Mammina ta fada har bakinta yana motsawa,wani abu me masifar nauyi takeji yana sauka saman zuciyarta. Ta tsanu safeena tsana mafi girma,tsanar da ko a lahira batajin zata daina mata wato bayan an mutu an gama kwanciyar kabari an tashi,dukkansu basu kai su goge wannan tsanar ba.
Ba wani dan adam a duniya daya taba kawo ma komai nata cikas sai ita.....ba wani wanda ta taba saka plan a gabanta ya zama silar wargajewarsa bayan baqar wahala datasha akai irinta. Daga ita sai IBRAHEEM,sauqinta daya.....IBRAHEEM har yanzu yana cin darajar taba sonshi da zuciyarta tayi,amma duk da haka shima saida ta barwa rayuwarsa tabo ta hanyar daukar rayuwa d'a na farki daya soma haifa a rayuwarsa.
Taimakonta daya sautin maganan da tayi baikai ga fita ba,saidai ahmad da idanunsa suke kanta ya tabbatar akwai wani abu data fada. Murmushi morsa ta sake.
"Allah yayi mata rahama"
"Ameen amee" Ahmad da sultane suka hada baki gurin amsawa.
"Ya qarfin jikin?" Ta sake tambayarsa
"Mun godewa Allah dai" Yadda yayi maganan sai morsa safiyya taji zuciyarta ta tsinke. Yanayin yadda safeena ke gaya mata kenan a kullum rana har ranar data bar duniya.
"Allah ya baka lafiya madawwamiya kai da sauran marasa lafiya"
"Ameen" Dukkansu suka amsa harda mammina a wannan karon wadda zuwansu gurin ya sanya taji kaman ta zama bare,kaman an wareta.
"Yarimanmu" Mammina ta fada tana murmushi. A nutse ahmad din ya juya yana dubanta,ya aje mata wani kallo da yanayin izzar data taba mammina din sosai.
"Wai duka yaushe ya iya wadannan abubuwan gaba daya?" Ta tambayi kanta da kanta.
"Idan kina fada,kaman kina qarawa zuciyarki nauyi ne,inda kin haqura da furtawar kiji da abu daya". Ya fada da yaren oromo daya tabbatar ba wanda zaiji abinda yace,don ko morsa safiyya ya fahimci ba yaren kowanne bangaren takeji ba,tsahon barinta qasar kuma yasa ta manta wasu abubuwa da yawa.
Murmushi kawai ta maida masa kaman yadda ta saba,har yau ko kalma daya bata taba furta masa ba,amma kuma shi ya sani,hakan ba yana nufin komai lafiya ba.
Gaban sultane ya qarasa cikin girmamawa ya tsugunna.
"Muna da baqi ranka ya dade cikin gidannan"
"Baqi?,wadanne iri?" Sultane ya fadi,don yadda yakejin jikinsa a yanzun bacci kawai yake da buqata.
"Eh baqi.....amma kamar ba gurinka kai tsaye sukazo ba.....daga babbar hukuma,alhaji nasiruddeen bahago" Jin sunan kawai ya sanya sultane tashi ya zauna sosai.
"Ba baqi bane ahmad....akwai sanayya me girma,duk sanda kuma kaga sunxo babban dalili ne ya kawosu,a shigo dasu" Ya fada yana duban Ahmad din. Kai ya jinjina a nutse,ya miqe wani sirrintaccen murmushi yana fita daga fuskarsa......ya taka a hankali xuwa qofa don bawa me wada umarni.
Tunda suka shigo gurin idanun mammina yake kansu. Haka kawai takejin akwai wani baqon al'amari a tattare dasu. Yadda suke dan kallonta daya bayan daya lokaci taji bata nutsu dasu ba. Bata duba yadda morsa safiyya ta kame daga gefe ba,suka gaisa cike da kima da dattako,suka kuma duba jikin sultane sannan suka mata barka da dawowar Ahmad ba tace.
"Kaman buqatar kwanciya sultane yake....don Allah idan ba matsala,ko zaku iya gama komai da wuri ya samu ya huta" Ta fada tana miqewa.
"Zaki zauna ne ai hajja zaituna,zuwan naki ne" Alhaji nasiruddeen ya fada a girmame.
Cak ta dakata tana dubansa,saidai kafin tace komai ya maida dubansa ga sultane.
"Allah ya baki yawan rai,ayimin afuwa nayi magana da iyali kai tsaye ba tare dana nema izini ba" Murmushi kadan sultane yayi,ba jiya ba yau ba,shekaru masu dama ne suka bada sanayyarsa da sabonsa da Alhaji nasiruddeen da kuma yanayin aikinsu.
"Ba komai......zaituna....zauna" Ya fadi yana dubanta.
"Duk fa wayon amarya sai ansha man ta.....kin manta?"
"Falaak.....ki kama kanki" Ta fada tana tsumewa
"Inacan tausayinki kamar zai hallakani,amma ke alfahari ma kike da abun?". Ta fada a qufule
"Dole nayi alfahari mana....nakai mutuncina gidan mijina,mijina na sunnah ne ya karbu budurcina abun alfahari ne yaa biftu,ina fata kema ya faru a kanki zakifi fahimta" Ta fada a ranta amma a fili sai tayi qasa da kanta tana cewa.
"Kiyi haquri na daina"
Knocking akayi aka turo ana shigowa,maleek ne,sai a sannan akhnan taga basarwar da yaketayi,sai yanzu ta fahimta
"Mugu" Ta fada qasan ranta tana jin haushinsa yana saukar mata. Wayarta ya ajiye mata a gefe yana cewa.
"Captain yace ki duba akwai saqo".
"Captain?" Ta maimaita tana daukan wayar,don sunan baqo ne a kunnuwanta,bata ma kuma gane wanene ba.
Procedures ne na yadda falaak zata samu relief a rubuce cikin wayar ya rubuta ya ajiye a notebook dinta. Kunya taji ta kamata sosai gauraye da haushi,har shima wai yasan meye ya faru ne?,kawa saita dan kai idanunta kansu maleek.
Yadda ya gwaggwafe gaban falaak din riqe da yatsunta yana murzawa,har ita dake gurin bata iyajin abinda yake gaya mata ya aza mata nauyi da yawa,kawai sai taji ba zata iya zama ba,ta miqe tsam,daidai sanda yake fadin.
"Tanti....ki zauna fita zanyi"
"No" Tace a taqaice kawai tana takawa gami da ficewa a dakin.
*_A G A D E Z_*
*_SULTANE PALACE_*
Zaune take a gabansa cikin nannauyar kwalliyar na dake cike da alfahari da kuma nuna isa,kwalliyar data qara adadin nauyinta don ta boye ramar data fara yi wadda ta bayyana kadan har a qasusuwan wuyanta.
Tun daga watannin baya,ranar da gobara ta tashi a gidan. Bacewar tamim.....bacewar yalwa,gobarar villa dama dauki daidai din da akewa hadimanta,har xuwa ranar qarshe da 'yan jarida suka dirar mata bata sake baccin kirki ba.
Kaman zatayi sanyi,kaman zatayi collapse,kaman zata saddaqar amma kuma zuciyarta ta gaya mata KI TASHI ZAITUNA!.
Wani irin salo take gani tattare da yaron da dawowarsa yafi haihuwarsa zame mata barazana a rayuwarta. AHMAD yaron data kowacce fuska baka isa ga qaryata jinin sultane bane a jikinsa.
Bai rayu dasu ba....bai rayu cikin masarautar ba......amma yasan kowanne nau'in salon sarautarsu.....lungu da saqo na cikin gidan.....adadin ma'aikata dama komai dake wanzuwa a cikin gidan. Batayi mamaki ba.....kasancewar ALSAAMIT tattare dashi zai iya zama mafi girman hatsari fiye da haka.
(Don samun littafin lu'u lu'u 08187255862)
Wani irin takawa d'ai d'ai taga kaman morsa safiyya tanayi.....wani irin girma ta fuskanci kanta yanayi......abinda ya hanata bacci darare da yawa.....saidai kuma ta samu babban makama sanda ta soma lura da rade radin da kuma gani da tayi da idanunta SULTANE bashi da wani cikakken qwari da lafiya.
Murmushi tayi sanda ta lura da wannan
"Wataqila ina da sauran dama ne.....daman da zata zamemin ta qarshe" Ta kama damar da kyau kuwa,ta fara kusanta kanta da sultane matuqar kusantawa. Abinda ya bata mamaki yadda take samun cikakken dama da access da komai,saidai cikas kadan kadan da take samu daga ahmad din.
Yaron da idan hanya ta hadasu yake mata wani irin kallo,kallon data tabbatar idan har yana da dama.....idan har zai yuwu zai iya daukan wuqa ya kaita lahira.
"Ta yaro kyau take bata qarko..... Ka daina dariya wasa yayi kyau.....wannan zaqin mulkin......wannan darajar da wannan matsayin gaba daya na 'yan kwanaki zuwa watanni ne....zaka sake bacewa bacewar da har abada ba zaka dawo ba" Haka takan fadi cikin ranta,amma a fili saita bishi da murmushi.
Kamar yanzu da take zaune gaban sultane din,tana yanka masa fruit din tana bashi yana sha,tana kuma jansa da hira a nutse.
Tun daga nesa ta hangesu,morsa safiyya ce cikin wata irin shigar kamala dake bayyanar da darajarta da wani irin Kwarjini. Ahmad yana biye da ita a baya da wani kalan girmamawa tamkar yana fadawa duniya ITADIN MAKWAFIN MAHAIFIYATA CE.
Ta zuba musu idanu da gaske,har cikin tsakiyar zuciyarta tana jin wani irin zugi a duk sanda ta gansu a haka. Dawowarsa ta sake qarawa morsa safiyya wani irin girma da martaba da bata zata ba,saboda kowa kiranta yake UWAR YARIMA ME JIRAN GADO.
Duk kuwa da yadda taso sunan ya zamana nata ne.....ko ta hana tasirin sunan,amma ko daya a ciki bata samu nasara ba.
Akwai tarin mutane masu yawan gaske dake neman kusanci da Ahmed din,wanda kusancin yana da muhimmancin da dole kowa ya buqaci wannan gurbin a kusa dashi.
A zahiri saita saki fuskarta,tana maida dubanta ga sultane da bai lura da tahowarsu ba.
"Ga magaji nan zuwa shida mamarsa". Kansa ya daga zuwa sashen,yana duban Ahmad yana jin wani abu me girma yana motsawa cikin zuciyarsa. Baisan dame zai yiwa haisam sakayya ba....duk da har yanzu baisan yadda komai ya kasa ce ba har yanzu.
Murmushi kawai yake saki har suka iso,murmushin da mammina take jinsa kamar tsiruwar allura saman naman zuciyarta.
"Barka da hutawa" Morsa safiyya ta fada tana cire takalmanta a girmame tana qarasowa gabansa.
"Bakanki uwar yarima" Murmushi ya subuce mata tayi qas da kanta,yanayin da ya masa kama sosai da safeena.
"Da kanka me martaba?"
"Sunan ya dace da wadda aka bawa ai......ga maman gimbiya....ke kuma ta yarima ce" Ya fada yana nuna mammina data qaqalo murmushin dole. Idanu morsa safiyya ta daga ta kalli mammina,cikin sa'a ita ita take kalla,sai kawai safiyyan ta ajewa mamminan murmushi tana dauke kanta. A yanzun bataga komai tattare da mammina ba sai wata kwantacciyar damuwa,damuwar da duk dare saita tsaya saman abun sallah ta kaiwa Allah sunanta. Allah ya hanawa rayuwarta sukuni muddin da haqqin safeena saman wuyanta.
"Zamankin nan a gabana.....sai naga kaman safeena ce" Ya fada zuciyarsa tana masa nauyi.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 34*
"Allah ya tsinewa safeena da kabarinta dama dukkan abinda ya fito ta tsatsonta dama ahalinta gaba daya" Mammina ta fada har bakinta yana motsawa,wani abu me masifar nauyi takeji yana sauka saman zuciyarta. Ta tsanu safeena tsana mafi girma,tsanar da ko a lahira batajin zata daina mata wato bayan an mutu an gama kwanciyar kabari an tashi,dukkansu basu kai su goge wannan tsanar ba.
Ba wani dan adam a duniya daya taba kawo ma komai nata cikas sai ita.....ba wani wanda ta taba saka plan a gabanta ya zama silar wargajewarsa bayan baqar wahala datasha akai irinta. Daga ita sai IBRAHEEM,sauqinta daya.....IBRAHEEM har yanzu yana cin darajar taba sonshi da zuciyarta tayi,amma duk da haka shima saida ta barwa rayuwarsa tabo ta hanyar daukar rayuwa d'a na farki daya soma haifa a rayuwarsa.
Taimakonta daya sautin maganan da tayi baikai ga fita ba,saidai ahmad da idanunsa suke kanta ya tabbatar akwai wani abu data fada. Murmushi morsa ta sake.
"Allah yayi mata rahama"
"Ameen amee" Ahmad da sultane suka hada baki gurin amsawa.
"Ya qarfin jikin?" Ta sake tambayarsa
"Mun godewa Allah dai" Yadda yayi maganan sai morsa safiyya taji zuciyarta ta tsinke. Yanayin yadda safeena ke gaya mata kenan a kullum rana har ranar data bar duniya.
"Allah ya baka lafiya madawwamiya kai da sauran marasa lafiya"
"Ameen" Dukkansu suka amsa harda mammina a wannan karon wadda zuwansu gurin ya sanya taji kaman ta zama bare,kaman an wareta.
"Yarimanmu" Mammina ta fada tana murmushi. A nutse ahmad din ya juya yana dubanta,ya aje mata wani kallo da yanayin izzar data taba mammina din sosai.
"Wai duka yaushe ya iya wadannan abubuwan gaba daya?" Ta tambayi kanta da kanta.
"Idan kina fada,kaman kina qarawa zuciyarki nauyi ne,inda kin haqura da furtawar kiji da abu daya". Ya fada da yaren oromo daya tabbatar ba wanda zaiji abinda yace,don ko morsa safiyya ya fahimci ba yaren kowanne bangaren takeji ba,tsahon barinta qasar kuma yasa ta manta wasu abubuwa da yawa.
Murmushi kawai ta maida masa kaman yadda ta saba,har yau ko kalma daya bata taba furta masa ba,amma kuma shi ya sani,hakan ba yana nufin komai lafiya ba.
Gaban sultane ya qarasa cikin girmamawa ya tsugunna.
"Muna da baqi ranka ya dade cikin gidannan"
"Baqi?,wadanne iri?" Sultane ya fadi,don yadda yakejin jikinsa a yanzun bacci kawai yake da buqata.
"Eh baqi.....amma kamar ba gurinka kai tsaye sukazo ba.....daga babbar hukuma,alhaji nasiruddeen bahago" Jin sunan kawai ya sanya sultane tashi ya zauna sosai.
"Ba baqi bane ahmad....akwai sanayya me girma,duk sanda kuma kaga sunxo babban dalili ne ya kawosu,a shigo dasu" Ya fada yana duban Ahmad din. Kai ya jinjina a nutse,ya miqe wani sirrintaccen murmushi yana fita daga fuskarsa......ya taka a hankali xuwa qofa don bawa me wada umarni.
Tunda suka shigo gurin idanun mammina yake kansu. Haka kawai takejin akwai wani baqon al'amari a tattare dasu. Yadda suke dan kallonta daya bayan daya lokaci taji bata nutsu dasu ba. Bata duba yadda morsa safiyya ta kame daga gefe ba,suka gaisa cike da kima da dattako,suka kuma duba jikin sultane sannan suka mata barka da dawowar Ahmad ba tace.
"Kaman buqatar kwanciya sultane yake....don Allah idan ba matsala,ko zaku iya gama komai da wuri ya samu ya huta" Ta fada tana miqewa.
"Zaki zauna ne ai hajja zaituna,zuwan naki ne" Alhaji nasiruddeen ya fada a girmame.
Cak ta dakata tana dubansa,saidai kafin tace komai ya maida dubansa ga sultane.
"Allah ya baki yawan rai,ayimin afuwa nayi magana da iyali kai tsaye ba tare dana nema izini ba" Murmushi kadan sultane yayi,ba jiya ba yau ba,shekaru masu dama ne suka bada sanayyarsa da sabonsa da Alhaji nasiruddeen da kuma yanayin aikinsu.
"Ba komai......zaituna....zauna" Ya fadi yana dubanta.