Sashe 159
LUu Luu Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kuma na taba daukar ciki" Ta fada tana murmushi,maganan ta yiwa akhnan nauyi da yawa,tayi qasa da kanta tana jin kamar zata narke. Ashe dai duk yadda ta dauki nanay a matsayin uwa....akwai wani abu da ba lallai ya sauya ba. Surukuta.....bata sauyawa,koda wannan matar zata uwa gareka.
"Uwa tana gane wasu abubuwa kafin a gaya mata."
"Mijinki....akhnan,akwai wata boyayyar soyayyar da yake miki wadda ni kaina basan da ita ba. Tunda muka zauna a nan idanunsa yana kanki sau ba adadi.....yana kula da dukka motsinki,shi kansa jikinsa ya fara sanin abin da ke tare da ke kafin hankalinsa ya gane." Kunya ta sake narkar da ita,ta sakeyin qasa da kanta sosai.
"Akhnan" Nanay ta kira sunanta a tausashe.
"Allah ya baki wata ni'ima me girma"Hawayen farin ciki suka fara taruwa a idanun Nanay.
"Zaki zama uwa idan Allah yaso"
"Ni kuma zan zama kaka" Ta qarasa fadan maganan da wani feeling sosai cikin ranta tana jin kamar ta hadiye akhnan.
A wannan karon akhnan ta sauke idanunta kan cikinta. Har yanzu tana jin abun kamar almara,kamar zuciyarta na gaya mata ba zata yarda gaba daya ba. Amma wani abu a zuciyarta ya fara canzawa. A hankali.....A hankali. Kamar tana fara fahimtar cewa rayuwarta ta shiga sabon babi ne.
Wani irin farinciki ya mamaye zuciyar haisam dake tsaye a bakin qofa yana kallonsu,yana kallon komai,sai ya sauke hannuwansa qasa a hankali yana jin shima qwalla tana cika masa idanuwa.
Baisan girman karamci irin na Allah iya adadinsa ba. Banda shi.....ba wanda zai maka haka. Ya maka baiwa ya sake qara maka da wata.
★★Wani hukunci ta yankewa kanta na koyon komai da komai a sanda duka haisam baya kusa. Cikin awannin da tasan zaije ya dawo. Ta yanke hukuncin zama cikakkiyar matar auren da zata bawa miji kulawa,ta kuma kula da yaran da zata haifa a gaba.
Ko kusa ko alama bata bari yasan da wannan shirin ba. A hankali kuma a boye take koyon komai. Saboda a yanzun....ta sani bata da komai....bata da wani abu da zata bawa haisam bayan wannan kulawar,bayan ta iya komai da yakeso yake kuma buqata.
Ta sani.....babban kuskure take aikatawa,saboda yadda haisam din idan yana gida koda daukan cup baya barinta tayi,hakanan idan zai fita sai ya tabbatar da dukka hadimanta biyar dinnan dama baba hannatou daya dauko mata ita daga Niamey tana kusa da ita.
Tunda take....ko a tarihi bata taba ji ko ganin inda ake lelen ciki irin nata ba. Ta sani tabbas banda tsaurara tsaro akan fitar maganan cikin da haisam ya yanke ya zama abune daya faru cikin sirri saboda sharrin ido da baki.....tayi imani da yanzun haka anacan ana shagali na kwana da kwanaki akan cikin.
Don gaba daya sunyo kabbara akansa. Tsakanin nanay motii dasu oga Anaani batasan waye yafi qaunar wannan d'an tayin dake kwance a mararta ba. A cire ta oga kwata kwata haisam.....nashi abun baya da misali dana kowa a cikin su,don tabbas inda yana da hali,daidai da numfashi ma cewa zaiyi zaiyi mata shi.
Batasan tana da kunya har haka ba.....sai sanda morsa safiyya ta kirata tana mata sannu da jiki. A maganganun morsa safiyya ta tabbatar nanay ba zata iya boye wannan farincikin ba....ba zata iya qin gayawa 'yar uwarta ba. Sanda sultane ya kirata zai mata sannu da jiki a wani lokaci da jikinta yayi weak,haisam ya dage lallai sai an saka mata drip saboda tafijin qwarin jikinta,kashe wayar tayi. Kunya ta dinga ji,ba zata iya magana da sultane ba,bayan ya fita sanin komai da akayi aka samu cikin.
Ta dora idanunta akan haisam dake zaune a gefanta yana yanka mata fruit,sai ya dage mata girarsa dukka biyun,daya daga cikin alamun tsokanarsa kenan idan yaso.
"Bakaji kunya ba?" Ta tambaya da muryarta da tayi laushi saboda wahalar da tasha jiya.
"Name?" Ya fadi yana kashe mata ido daya.
"Haisammm mana" Ta fada a karye.
"Wash Allah na" Ya fadi shima yana lumshe idanunsa gami da dora tafin hannunsa a qirjinsa.
"Har yau.....ba abinda ya canza....har yau ina bala'in son naji sunana abakinki" Yana sauke maganan yana jifansa da pillow. Saurin fushinta ya motsa,wani abu ya tsaye mata a wuya. Haisam ya rainata,ta lura kallon yarinya qarama cancan yake mata. Idan tana magana serious shikam bai taba bata muhimmanci ba.
"Bakajin kunyar bappi na.....kasan me kayimin na samu ciki,amma har zaka iya gaya masa ina da cikin?" Ta fada hawaye na silmiyo mata.
Dariya taso qwace masa,amma yasan bai isa yinta a wannan lokacin ba. Maganan gaskiya ya rasa wanne kalan sakalci yake damun akhnan din.
Ita ba 'yar fari ba....ita ba auta ba. Duk da wani bangaren ana iya kiranta da auta din,tunda itace ta qarshe a wajen mamminta. Komai ya ajiye ya isa inda take,ya tsugunna saman qafafunsa yahau aikin lallashi da share mata hawaye. Saboda ya sani......indai nanay tazo ta samesu a hakan....bame qwatarsa sai Allah. Laifin duniya duka nasa ne.
Nanay.....ba wai tana son akhnan bane kawai. A'a....yanzu tana kallonta ne da idanun uwa.....suruka....kuma mahaifiyar babban jikanta na farko.
Akhnan ta fara jin kamar Nanay tana zaune ne a gidansu,saboda kullum sai ta kira. Safe.....rana....dare.
"Kinci abinci?"
"Me kika ci?"
"Me yake damunki?"
"Me kikeso yanzu?"
"Ina fata haisam bai takuraki ba"
"Akwai abinda kike buqata?"
"Me kikeyi yanzu?"
"Qarfe nawa kikayi bacci?"
"Basu katse miki bacci ba ko?"
Wadannan tambayoyin dama tarin wasu ya sanya haisam ke kame kansa kafin sunanshi ya shigo list na 'yan tuhuma.
Shi kansa bai tsira ba,wani lokaci shi take kira ba akhnan ba. Akwai randa yayi wani mistake ranar ya gane a yanzun baida wata faada a gurin nanay. Akhnan da abinda ke cikinta sun karbe gurbin.
"Muhammad" Yana tsaka da aiki a sannan a office dinsa dake jimma.
"Na'am nanay"
"Taci?"
"Me taci?" Ya tambaya saboda kanshi ya buga da tarin gyare gyare da sukeyi a kamfani,da kuma settling ayyukan akhnan na sahel couture dana maison akhnan daya hadawa kansa gaba daya.
"Dama na sani....baka tambayeta ba....anya muhammad kana kula da ita yadda ya dace kuwa?"
"Nanay...." Ya kirata don bada uzuri amma ta katseshi.
"Ka kirani idan ka isa gida" Sai ta katse wayar abinta.
"...I failed an inspection." Ya fadi a fili yana dafe kanshi.
Bayan kwana biyu kuma sai ga motoci sun iso gidan cike da kayan abinci.
Fresh fruits,honey da traditional foods da yawanci masu juna biyu suke ci. Komai carefully selected,kana kalla kasan da takatsantsan aka shirya komai.
Da kanta ta sauko ta duba cartons din cikin mamaki.
"Waye ya turo wannan?"
Birra tayi murmushi tana dubanta.
"Nanay." Sai Akhnan ta dafe goshinta tana dariya.
Jiya suka gama wannan case din da haisam. Yanata complain. Duk kulawar da yake bata shi ya lura ma kamar nanay ta rainata. Kamar ma baya yin komai,yau ga aiken kayan abinci da fruit bayan duka stores dinsu na gidan ba wanda ba ajiyayyen kayan abincin da zai shekara biyu su da dukka hadiman gidan suna amfani dashi komai yawansu.
"Allah ya barmin nanay na" Ta fada tana murmushi,ta sake matsawa tana kuma buda kwalayen.
Har ma da notes,small notes a takaddan da handwriting din nanay dake nuna rubutunta ne.
"Ki ci wannan da safe."
"Kar ki bari yunwa ta same ki."
"Ki huta sosai.". Saita dauki takardar a hannunta tana komawa ciki da ita.💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 146*
★Da wani yammaci.....daya daga cikin yammacin da haisam yake addis ababa. Yaje can headquarter dinsu zaiyi supervision na wani aiki da aka tura wasu daga nan office dinsu under na'urorin da suke communicating.
Yawanci idan zaije addis ababa din ta private jet yake tafiya ya kuma dawo,baya ma shiga kuma sai idan wani abu ya taso,don haka duka duka awanni uku zuwa hudu yakeyi.
Yaso yaje da akhnan din.....amma baisan ya akayi yayi subutar baki yana sallama da nanay din tace kul kada ya soma daukar mata diya,shi din dai sai ya dawo.
Hakanan ya haqura din,amma duk bayan wasu mintuna sai taga kiranshi ko tex dinsa.
Tashinta a bacci kenan da yammacin,tayi sallah ta sake watsa ruwa saboda yanzun wani irin jin zafi ne da ita. Ta shirya cikin wata cotton gown data sauke har qasa ta rufe mata qafafunta. Wani material ne olive green me taushi da rashin nauyi. Ta kame gashinta da wani band,hakan ya bawa gashin nata daman sauka a gadon bayan ta yana lilo. Dan matashin cikinta daya soma bayyana tun a wata uku ya dago rigar kadan. Tayi wani irin kyau irin na masu farkon shigar ciki.
Ta sauko downstairs da wayarta a hannu tana murmushi bayan ta gama duba saqon haisam.
"Giiftii.....my princess.....bana gane aikin nan sam....anya bazan musu shirme ba?,the silent one bazai samu suspension ba kuwa?,nanay taqi fahimta.....ke aljihuna ce....na gaba gaba" Maganan ya sakata dariya da nishadi sosai,da wannan a fuskarta ta qarasa saukowa.
Buhaina da bushira ne kawai a parlour din,suna turareshi da sassanyan qamshin nan na shuwa incense and more,daya daga cikin qamshin da har yanzu bata daina so ba.....basa damunta kuma (+234 704 229 3387 tasted and trusted,zaki godemin sosai).
Da girmamawar nan da qauna dake tsakaninsu da uwar dakin nasu suke mata barka da saukowa. Ta amsa musu itama da kulawa. A ranta tana jin kamar lokaci yayi da suma ya dace ta aurar dasu,koda kuwa zasuci gaba da rayuwa da ita ne.
"Nanay tazo" Buhaina ta fada da murmushi,don suna matuqar son zuwan matar gidan. Badai mutunci da karamci ba. Da dan mamaki ta daga idanunta daga amsar da take kan bawa haisam din idanunta a waje.
"Yaushe?,tana ina?"
"Yanzu ne,bata jima na,tana kitchen"
"Kitchen kuma?" Ta tambaya da mamaki,sai kawai ta fara takawa da kanta zuwa kitchen din ba tare data jirasu ba.
Tun daga nesa ta hangota cikin cook ma gidan tana duba abinda ake dafawa.
"Me yasa suka saka spice haka?" Ta fadi tana d'an d'ana wani fried chicken da suka kammala.
Cook din ta tsaya cak tana rusunawa.
"Ban dauka ba'a buqatarsa ba ranki ya dade" Kai nanay ta girgiza
"Kunsan ba ita kadai bace.....ba za ku dafa kamar yadda kuka saba ba,a daina using nashi kwata kwata,yayi strong da yawa" Ta qarasa maganan cikin jikinta kamar tana jin isowar akhnan ta maida idanunta can.
"Uwa tana gane wasu abubuwa kafin a gaya mata."
"Mijinki....akhnan,akwai wata boyayyar soyayyar da yake miki wadda ni kaina basan da ita ba. Tunda muka zauna a nan idanunsa yana kanki sau ba adadi.....yana kula da dukka motsinki,shi kansa jikinsa ya fara sanin abin da ke tare da ke kafin hankalinsa ya gane." Kunya ta sake narkar da ita,ta sakeyin qasa da kanta sosai.
"Akhnan" Nanay ta kira sunanta a tausashe.
"Allah ya baki wata ni'ima me girma"Hawayen farin ciki suka fara taruwa a idanun Nanay.
"Zaki zama uwa idan Allah yaso"
"Ni kuma zan zama kaka" Ta qarasa fadan maganan da wani feeling sosai cikin ranta tana jin kamar ta hadiye akhnan.
A wannan karon akhnan ta sauke idanunta kan cikinta. Har yanzu tana jin abun kamar almara,kamar zuciyarta na gaya mata ba zata yarda gaba daya ba. Amma wani abu a zuciyarta ya fara canzawa. A hankali.....A hankali. Kamar tana fara fahimtar cewa rayuwarta ta shiga sabon babi ne.
Wani irin farinciki ya mamaye zuciyar haisam dake tsaye a bakin qofa yana kallonsu,yana kallon komai,sai ya sauke hannuwansa qasa a hankali yana jin shima qwalla tana cika masa idanuwa.
Baisan girman karamci irin na Allah iya adadinsa ba. Banda shi.....ba wanda zai maka haka. Ya maka baiwa ya sake qara maka da wata.
★★Wani hukunci ta yankewa kanta na koyon komai da komai a sanda duka haisam baya kusa. Cikin awannin da tasan zaije ya dawo. Ta yanke hukuncin zama cikakkiyar matar auren da zata bawa miji kulawa,ta kuma kula da yaran da zata haifa a gaba.
Ko kusa ko alama bata bari yasan da wannan shirin ba. A hankali kuma a boye take koyon komai. Saboda a yanzun....ta sani bata da komai....bata da wani abu da zata bawa haisam bayan wannan kulawar,bayan ta iya komai da yakeso yake kuma buqata.
Ta sani.....babban kuskure take aikatawa,saboda yadda haisam din idan yana gida koda daukan cup baya barinta tayi,hakanan idan zai fita sai ya tabbatar da dukka hadimanta biyar dinnan dama baba hannatou daya dauko mata ita daga Niamey tana kusa da ita.
Tunda take....ko a tarihi bata taba ji ko ganin inda ake lelen ciki irin nata ba. Ta sani tabbas banda tsaurara tsaro akan fitar maganan cikin da haisam ya yanke ya zama abune daya faru cikin sirri saboda sharrin ido da baki.....tayi imani da yanzun haka anacan ana shagali na kwana da kwanaki akan cikin.
Don gaba daya sunyo kabbara akansa. Tsakanin nanay motii dasu oga Anaani batasan waye yafi qaunar wannan d'an tayin dake kwance a mararta ba. A cire ta oga kwata kwata haisam.....nashi abun baya da misali dana kowa a cikin su,don tabbas inda yana da hali,daidai da numfashi ma cewa zaiyi zaiyi mata shi.
Batasan tana da kunya har haka ba.....sai sanda morsa safiyya ta kirata tana mata sannu da jiki. A maganganun morsa safiyya ta tabbatar nanay ba zata iya boye wannan farincikin ba....ba zata iya qin gayawa 'yar uwarta ba. Sanda sultane ya kirata zai mata sannu da jiki a wani lokaci da jikinta yayi weak,haisam ya dage lallai sai an saka mata drip saboda tafijin qwarin jikinta,kashe wayar tayi. Kunya ta dinga ji,ba zata iya magana da sultane ba,bayan ya fita sanin komai da akayi aka samu cikin.
Ta dora idanunta akan haisam dake zaune a gefanta yana yanka mata fruit,sai ya dage mata girarsa dukka biyun,daya daga cikin alamun tsokanarsa kenan idan yaso.
"Bakaji kunya ba?" Ta tambaya da muryarta da tayi laushi saboda wahalar da tasha jiya.
"Name?" Ya fadi yana kashe mata ido daya.
"Haisammm mana" Ta fada a karye.
"Wash Allah na" Ya fadi shima yana lumshe idanunsa gami da dora tafin hannunsa a qirjinsa.
"Har yau.....ba abinda ya canza....har yau ina bala'in son naji sunana abakinki" Yana sauke maganan yana jifansa da pillow. Saurin fushinta ya motsa,wani abu ya tsaye mata a wuya. Haisam ya rainata,ta lura kallon yarinya qarama cancan yake mata. Idan tana magana serious shikam bai taba bata muhimmanci ba.
"Bakajin kunyar bappi na.....kasan me kayimin na samu ciki,amma har zaka iya gaya masa ina da cikin?" Ta fada hawaye na silmiyo mata.
Dariya taso qwace masa,amma yasan bai isa yinta a wannan lokacin ba. Maganan gaskiya ya rasa wanne kalan sakalci yake damun akhnan din.
Ita ba 'yar fari ba....ita ba auta ba. Duk da wani bangaren ana iya kiranta da auta din,tunda itace ta qarshe a wajen mamminta. Komai ya ajiye ya isa inda take,ya tsugunna saman qafafunsa yahau aikin lallashi da share mata hawaye. Saboda ya sani......indai nanay tazo ta samesu a hakan....bame qwatarsa sai Allah. Laifin duniya duka nasa ne.
Nanay.....ba wai tana son akhnan bane kawai. A'a....yanzu tana kallonta ne da idanun uwa.....suruka....kuma mahaifiyar babban jikanta na farko.
Akhnan ta fara jin kamar Nanay tana zaune ne a gidansu,saboda kullum sai ta kira. Safe.....rana....dare.
"Kinci abinci?"
"Me kika ci?"
"Me yake damunki?"
"Me kikeso yanzu?"
"Ina fata haisam bai takuraki ba"
"Akwai abinda kike buqata?"
"Me kikeyi yanzu?"
"Qarfe nawa kikayi bacci?"
"Basu katse miki bacci ba ko?"
Wadannan tambayoyin dama tarin wasu ya sanya haisam ke kame kansa kafin sunanshi ya shigo list na 'yan tuhuma.
Shi kansa bai tsira ba,wani lokaci shi take kira ba akhnan ba. Akwai randa yayi wani mistake ranar ya gane a yanzun baida wata faada a gurin nanay. Akhnan da abinda ke cikinta sun karbe gurbin.
"Muhammad" Yana tsaka da aiki a sannan a office dinsa dake jimma.
"Na'am nanay"
"Taci?"
"Me taci?" Ya tambaya saboda kanshi ya buga da tarin gyare gyare da sukeyi a kamfani,da kuma settling ayyukan akhnan na sahel couture dana maison akhnan daya hadawa kansa gaba daya.
"Dama na sani....baka tambayeta ba....anya muhammad kana kula da ita yadda ya dace kuwa?"
"Nanay...." Ya kirata don bada uzuri amma ta katseshi.
"Ka kirani idan ka isa gida" Sai ta katse wayar abinta.
"...I failed an inspection." Ya fadi a fili yana dafe kanshi.
Bayan kwana biyu kuma sai ga motoci sun iso gidan cike da kayan abinci.
Fresh fruits,honey da traditional foods da yawanci masu juna biyu suke ci. Komai carefully selected,kana kalla kasan da takatsantsan aka shirya komai.
Da kanta ta sauko ta duba cartons din cikin mamaki.
"Waye ya turo wannan?"
Birra tayi murmushi tana dubanta.
"Nanay." Sai Akhnan ta dafe goshinta tana dariya.
Jiya suka gama wannan case din da haisam. Yanata complain. Duk kulawar da yake bata shi ya lura ma kamar nanay ta rainata. Kamar ma baya yin komai,yau ga aiken kayan abinci da fruit bayan duka stores dinsu na gidan ba wanda ba ajiyayyen kayan abincin da zai shekara biyu su da dukka hadiman gidan suna amfani dashi komai yawansu.
"Allah ya barmin nanay na" Ta fada tana murmushi,ta sake matsawa tana kuma buda kwalayen.
Har ma da notes,small notes a takaddan da handwriting din nanay dake nuna rubutunta ne.
"Ki ci wannan da safe."
"Kar ki bari yunwa ta same ki."
"Ki huta sosai.". Saita dauki takardar a hannunta tana komawa ciki da ita.💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 146*
★Da wani yammaci.....daya daga cikin yammacin da haisam yake addis ababa. Yaje can headquarter dinsu zaiyi supervision na wani aiki da aka tura wasu daga nan office dinsu under na'urorin da suke communicating.
Yawanci idan zaije addis ababa din ta private jet yake tafiya ya kuma dawo,baya ma shiga kuma sai idan wani abu ya taso,don haka duka duka awanni uku zuwa hudu yakeyi.
Yaso yaje da akhnan din.....amma baisan ya akayi yayi subutar baki yana sallama da nanay din tace kul kada ya soma daukar mata diya,shi din dai sai ya dawo.
Hakanan ya haqura din,amma duk bayan wasu mintuna sai taga kiranshi ko tex dinsa.
Tashinta a bacci kenan da yammacin,tayi sallah ta sake watsa ruwa saboda yanzun wani irin jin zafi ne da ita. Ta shirya cikin wata cotton gown data sauke har qasa ta rufe mata qafafunta. Wani material ne olive green me taushi da rashin nauyi. Ta kame gashinta da wani band,hakan ya bawa gashin nata daman sauka a gadon bayan ta yana lilo. Dan matashin cikinta daya soma bayyana tun a wata uku ya dago rigar kadan. Tayi wani irin kyau irin na masu farkon shigar ciki.
Ta sauko downstairs da wayarta a hannu tana murmushi bayan ta gama duba saqon haisam.
"Giiftii.....my princess.....bana gane aikin nan sam....anya bazan musu shirme ba?,the silent one bazai samu suspension ba kuwa?,nanay taqi fahimta.....ke aljihuna ce....na gaba gaba" Maganan ya sakata dariya da nishadi sosai,da wannan a fuskarta ta qarasa saukowa.
Buhaina da bushira ne kawai a parlour din,suna turareshi da sassanyan qamshin nan na shuwa incense and more,daya daga cikin qamshin da har yanzu bata daina so ba.....basa damunta kuma (+234 704 229 3387 tasted and trusted,zaki godemin sosai).
Da girmamawar nan da qauna dake tsakaninsu da uwar dakin nasu suke mata barka da saukowa. Ta amsa musu itama da kulawa. A ranta tana jin kamar lokaci yayi da suma ya dace ta aurar dasu,koda kuwa zasuci gaba da rayuwa da ita ne.
"Nanay tazo" Buhaina ta fada da murmushi,don suna matuqar son zuwan matar gidan. Badai mutunci da karamci ba. Da dan mamaki ta daga idanunta daga amsar da take kan bawa haisam din idanunta a waje.
"Yaushe?,tana ina?"
"Yanzu ne,bata jima na,tana kitchen"
"Kitchen kuma?" Ta tambaya da mamaki,sai kawai ta fara takawa da kanta zuwa kitchen din ba tare data jirasu ba.
Tun daga nesa ta hangota cikin cook ma gidan tana duba abinda ake dafawa.
"Me yasa suka saka spice haka?" Ta fadi tana d'an d'ana wani fried chicken da suka kammala.
Cook din ta tsaya cak tana rusunawa.
"Ban dauka ba'a buqatarsa ba ranki ya dade" Kai nanay ta girgiza
"Kunsan ba ita kadai bace.....ba za ku dafa kamar yadda kuka saba ba,a daina using nashi kwata kwata,yayi strong da yawa" Ta qarasa maganan cikin jikinta kamar tana jin isowar akhnan ta maida idanunta can.