Sashe 98
Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sultan ya maida idannuwansa dake dauke da yannayin kausasa ya ce" Mardiya, me kike a nan zaune tamkar wace bata da aure?"
Mardiya ta hadiyi wani yawu jin wai a tambayetan da Abih ya ce, kafin muryarta na rawa rawa karshe ta fashe da kuka ta ce" wai yaya kake na yi ne MUTAKAB, yaya kake so na yi? Bayan kana min gabar da ban san a kan me ba dan kawai na fadi gaskiyana shikenan?, ni bani da damar nuna fushina shine zaka nunan na tafi gidanmu? Da zaka ce a tambaye ni a kan me nake zaune a nan so kake na yashi na kara komawa gidan namu ka hadu da wannan kunna cin amanata?
Wannan din da ta ce da wada ta nuna ya saka da SHAHEED, da AMMI, da ABIH baki daya suka kai dubansu wajen UMMU dake zaune
Ga mamakin SHAHEED wanda ya yi jiran jin irin hukuncin da UMMU zata dauka ta hanyar ramawa sanninta da ya yo cewar bata da hakuri da daukan raini, sai ya ga ko nunawa bata yi cewar ta san zancen da ake ba, hasalima abin yanke farce ta dauna ta duka tana dan karkare karamin farcenta na yatsarta karama,
Juyowa ya yi da yannayin mamaki, lalle dunia ta yi sanyi, sannan ya yarda idan ba auren ba babu abinda zai saka ka kalli mutun da girmansa da komai ka farfada masa magangannun da sukai maka dadi dan kawai ya taba auren mijinka bayan ya girme maka nesa ba kusa ba
"Haba Mardiya, me yasa kike da saurin daukan fushi a kan lamarin duniya harma ki rufe ido ki ringa magana na neman magana ne? Me ya hada zamanta da mijinki ne? Me yasa kike ta shigota da gudu bayan tana iya yinta tana kauce maki da dukan karfinta ne?" AMMI ta karasa tana mai kallon Mardiya
Mardiya ta ce" Haba maman Sultan, tsakani da Allah karya na yi ne? Meye hadinta da mijina da zata ringa dauko masa ruwa daga ya zo? Meye zai sa ta zo nan ta tare bayan na san ba danginku bace?"
Da wani mamakin Ammi ta budi baki zata yi magana , Abih ya rigayeta yana dan murmushi ya ce" in ba Mardiya ba macen da ka haihu da ita a yi maganar meye hadinka da ita?"
Da sauri ta tare shi tana dan fido masa manyan idannuwanta ta ce" kana nufin du iyayen y'ayanka sunna iya zuwa nan su tare dan kawai aun haihu da kai?"
Mutalab ya dago idannuwansa da sukai masa ja ya kalleta, ya dauke dubansa ya kai kan UMMU, sai da ya lumshe idannuwansa kafin ya cire ya dora kan SULATAN dake bin du wanda ya dauki magana da ido yana jira su gama, dan murmushi ya yi ya dan cije lebensa ya ce" ka ga ilar rashin zama waje daya ko? , Shaheed a da ce mata na yi ta je gidansu, aman a yanzu ina so ta koma dakinta sai dai da sharadi, dan Allah Shaheed ka rokar min Nana ashuwa ta koma dakinta, ina mai roko da kokon barana uwar y'ayana ta koma dakinta"
Shaheed ya kurawa Abih ido, lokaci daya Mardiya ta zabura , baki daya jikinta ya kwashi rawa, tana mai kukan nan sama sama ta ce" walahi ba dai da ni zan yi kishi da macen da ta girmeni ba, matar da ta haifeni ne za'a hadani kishi da ita? Me yasa ake son kai a wajennan? Kowa idan ya budi baki sai dai ya goya mata baya ni kuwa a kwaye min? To walahi ba zan hada kishi da ita ba sai dai ka sake ni MUTALAB,"
UMMU ta dago daga gyaran farcenta da take ta kai dubanta kan Mardiya a karo na farko kennan, sai da ta rintse idannuwanta ta saki bakinta da ta cije da karfi tana kallonta ta nunata da abin yanke farcen nan ta ce" sannin cewar ke yarinya ce ya saka nake kawar da kaina a kanki MARDIYA! Yaya kike son sai kin kureni wajen da zan iya hukuntaki tamkar yar da na haifa da cikina ta hanyar dane ruwan cikinta na matse bakinki na zaneki da bulala?, ki kiyayi shiga sabgata, na rantse maki zan iya matse hancinki na rufe numfashinki! MARDIYA ke yarinya ce, kuma a duniyar kishi ke yar kauye ce ki je ki zauna da mace ta koya maki kishi, ki bambance MIJI da KISHIYA , ki iya yiwa MIJI magana, ki iya tafia a gaban miji kafin ki dawo ki tantance ni din abokiyar gabarki ce ko makashinki ce!"
Abin yankan Farcen ta ajiye da karfi saman table din glass din wanda hakan ya saka wajen yin kara ta mike tsaye, sannan ta dan duka ta dafa hannayenta bibiyu saman table din tana kallonta da idannuwanta dake nuna tsantsar bacin rai ta ce" zama da tsoho ai ya kare tunda kika auri tsoho da yarintarki dan son zuciya kika zauna, shirme ai ya kare a macen dake tunanin zata ci galaba a wajen namiji bayan tana kin y'ayansa, ke kam wawuya ce tunda har kike yiwa mijinki hauka a gaban kowa, ke din sakarai ce tunda har kike tunanin ihunki zai hanna wani abun rayuwa! Mazan nan da biyayarkima yaya kika gama da su? Bale ke tsagera karamar kwari?, shin mahaifiyarki ta rasu da kika rasa magaya ne ko me?"
Baki Mardiya ta daga zata yi magana da yannayin tsoron da ya darsun mata na yannayin UMMU, sai dai kafin ta yi UMMU ta zabura ta idasa matsawa kusa da ita sosai ta ce" dis, idan bakinki ya furta min A ba cikin kalmar da zaki hada dan gaishe ni ina maki rantsuwa da wanda raina ke hannunsa sai na sauke maki hakori irin yanda zan hukunta dan cikina, domin ke din y'ar cikina ce!"
Wuki wuki ta shiga yi da idannuwanta
Ummu ta juya ta fara tafia ranta a matukar bace, sai kuma ta tsaya ta juyo ta kalli MUTALAB da MARDIYA ta dan daga muryarta ta ce" me zan yi da aurensa? Bana so, ki kwontar da hankalinki in dan wannan kike hauka!"
Wannan kalmar ita ta fi batawa Abih rai, ya muke da sauri ya taka yana biye da UMMU wace ta kara saurinta zata shige dakin su NAJEEBA ya ce" NANA nine bakya so? Nine bakya so Nana? Sai me dan bakya so na, idan baki aureni ba mutuwa zan yi yo? Aman walahi ba wanda zaki aura in dai ina raye , mu zuba ni da ke"
UMMU ta juyo ta zazaro idannuwanta ta ce" mu zuba MUTALAB, idan an zo daura aurena ka hanna! "
Tana kokarin rufe bakinta sukai ido hudu da NAJEEBA wace yar hayaniyar ta fitar da ita, irin kallon da take mata ya saka jin kafafuwanta sun yi mata nauyi,
A hankali ta furta" NAJEEBA"
NAJEEBA ta lumshe idannuwanta zafafan hawaye suka zubo a kurmin idannuwanta, itama a hankali sannan a sanyaye ta furta" *sai kin aure shi MAMA, idan kuwa ba haka ba mu zuba*"
Tana gama fada ta juya da sauri ta yi dakin kannenta da aka kora su da niyar labarta masu abinda UMMU ke yiwa Abihnsu
Wani irin farin ciki ne ya saka UMMU jin saukar hawaye mai dumi a gurbin idannuwanta,
Ba na komai bane sai na wannan kalma da take ji daga bakunnan y'ayanta goma sha shida banda dayar, a yau ta fito daga bakinta cike da rigima ta hanyar turo dan bakinta mai kyau ta ce *MAMA* ,
Ajiyar zuciya ta sauke ta daga kafarta da sauri ta bi bayansu dan a yi komai a gabanta
Murmushi Abih ya yi ya juya da sauro da takamarsa ya zo wucewa ya jiyo ihun kulan Mardiya da ta yi dakinta da gudu tana maimaita ba zata yi zaman kishi da UMMU ba ya mikawa SHAHEED da ya talabe kuncinsa yana kallon ikon Allah hannu ya ce" a tayamu da adu'a su kara rikice mata har ta aminta sai ka daura mana aurenmu"
Shi kam Shaheed sai ya samu kansa shima da yin murmushin ya mika masa hannun suka gaisa ya juya ya yi ficewarsa
Dubansa ya maida Kan AMMI dake ta kalle kalle ya sakar mata murmushi ya mike ya karasa kusa da ita
Hannunta ya dauka na dama ya manawa bayan hannun nata kiss a hankali ya ce" AMMI, i lv u"
Murmushi AMMI ta yi tana kallonsa cike da kaunarsa,
Ya ce" zan je, Ammi zan dawo idan har ban samu gamsuwa da irin hukuncin Umani ba"
Ita dai tana mai binsa da murmushin har ya tafi
Kamar yanda ya fada masu hakan ne ya kasance, a zaunen ya tarar da matansa biyu su duka sun sha kwaliyarsu sai kamshin turare dake tashi, aunna zaune a kujeru masu nesa da junna ba wada ke yiwa yar uwarta magana
Da mamakin ganninsa ba rawani, da shiga irin ta jaruman maza du suka bi shi da kallo
Sunna jira ya zauna ya hakimce su kai gaisuwa sai suka ga ya ja ya tsaya a tsakiya,
Muryarsa a dake ya ce" shin daga baya kika fasa ko menene dalili?"
Zinaria dake kallonsa gannin maganar da ita yake ta kara buda kunnayenta dan jin a kan abinda yake magana,
Sai kuma ta ga ya juya wajen NADIA itama a kausashen ya furta" Daga baya kika fasa ko tunda kika zo baki san wannan shine abu na farko a cikin layin abinda zaki yi dan samun dorewar zama da ni tare da kwonciyar hankali da nutsuwa ba? Shin baki san shine dalilin da ya saka na yi dogayen hanyoyin da zasu kai kowacenku wajen ba tare da ta fito ta bi cikin baban gida ba?"
Kara sada kanta ta yi itama cikin rudu, aman ta kasa furta komai domin a ganninta Zinaria itace baba itace ta san kan mai gidan gannin bata ce komai ba sai itama ta yi shirun ta kara sada kanta sosai
SULTAN ya ajiye wayarsa saman table a hankali ya ce" ku kiyaye"
Gannin yana niyar shigewa ciki ya saka ZINARIA kara saukowa ta rage muryarta sosai ta ce" Allah ya taimake ka, shin a kan me kake magana?"
Mardiya ta hadiyi wani yawu jin wai a tambayetan da Abih ya ce, kafin muryarta na rawa rawa karshe ta fashe da kuka ta ce" wai yaya kake na yi ne MUTAKAB, yaya kake so na yi? Bayan kana min gabar da ban san a kan me ba dan kawai na fadi gaskiyana shikenan?, ni bani da damar nuna fushina shine zaka nunan na tafi gidanmu? Da zaka ce a tambaye ni a kan me nake zaune a nan so kake na yashi na kara komawa gidan namu ka hadu da wannan kunna cin amanata?
Wannan din da ta ce da wada ta nuna ya saka da SHAHEED, da AMMI, da ABIH baki daya suka kai dubansu wajen UMMU dake zaune
Ga mamakin SHAHEED wanda ya yi jiran jin irin hukuncin da UMMU zata dauka ta hanyar ramawa sanninta da ya yo cewar bata da hakuri da daukan raini, sai ya ga ko nunawa bata yi cewar ta san zancen da ake ba, hasalima abin yanke farce ta dauna ta duka tana dan karkare karamin farcenta na yatsarta karama,
Juyowa ya yi da yannayin mamaki, lalle dunia ta yi sanyi, sannan ya yarda idan ba auren ba babu abinda zai saka ka kalli mutun da girmansa da komai ka farfada masa magangannun da sukai maka dadi dan kawai ya taba auren mijinka bayan ya girme maka nesa ba kusa ba
"Haba Mardiya, me yasa kike da saurin daukan fushi a kan lamarin duniya harma ki rufe ido ki ringa magana na neman magana ne? Me ya hada zamanta da mijinki ne? Me yasa kike ta shigota da gudu bayan tana iya yinta tana kauce maki da dukan karfinta ne?" AMMI ta karasa tana mai kallon Mardiya
Mardiya ta ce" Haba maman Sultan, tsakani da Allah karya na yi ne? Meye hadinta da mijina da zata ringa dauko masa ruwa daga ya zo? Meye zai sa ta zo nan ta tare bayan na san ba danginku bace?"
Da wani mamakin Ammi ta budi baki zata yi magana , Abih ya rigayeta yana dan murmushi ya ce" in ba Mardiya ba macen da ka haihu da ita a yi maganar meye hadinka da ita?"
Da sauri ta tare shi tana dan fido masa manyan idannuwanta ta ce" kana nufin du iyayen y'ayanka sunna iya zuwa nan su tare dan kawai aun haihu da kai?"
Mutalab ya dago idannuwansa da sukai masa ja ya kalleta, ya dauke dubansa ya kai kan UMMU, sai da ya lumshe idannuwansa kafin ya cire ya dora kan SULATAN dake bin du wanda ya dauki magana da ido yana jira su gama, dan murmushi ya yi ya dan cije lebensa ya ce" ka ga ilar rashin zama waje daya ko? , Shaheed a da ce mata na yi ta je gidansu, aman a yanzu ina so ta koma dakinta sai dai da sharadi, dan Allah Shaheed ka rokar min Nana ashuwa ta koma dakinta, ina mai roko da kokon barana uwar y'ayana ta koma dakinta"
Shaheed ya kurawa Abih ido, lokaci daya Mardiya ta zabura , baki daya jikinta ya kwashi rawa, tana mai kukan nan sama sama ta ce" walahi ba dai da ni zan yi kishi da macen da ta girmeni ba, matar da ta haifeni ne za'a hadani kishi da ita? Me yasa ake son kai a wajennan? Kowa idan ya budi baki sai dai ya goya mata baya ni kuwa a kwaye min? To walahi ba zan hada kishi da ita ba sai dai ka sake ni MUTALAB,"
UMMU ta dago daga gyaran farcenta da take ta kai dubanta kan Mardiya a karo na farko kennan, sai da ta rintse idannuwanta ta saki bakinta da ta cije da karfi tana kallonta ta nunata da abin yanke farcen nan ta ce" sannin cewar ke yarinya ce ya saka nake kawar da kaina a kanki MARDIYA! Yaya kike son sai kin kureni wajen da zan iya hukuntaki tamkar yar da na haifa da cikina ta hanyar dane ruwan cikinta na matse bakinki na zaneki da bulala?, ki kiyayi shiga sabgata, na rantse maki zan iya matse hancinki na rufe numfashinki! MARDIYA ke yarinya ce, kuma a duniyar kishi ke yar kauye ce ki je ki zauna da mace ta koya maki kishi, ki bambance MIJI da KISHIYA , ki iya yiwa MIJI magana, ki iya tafia a gaban miji kafin ki dawo ki tantance ni din abokiyar gabarki ce ko makashinki ce!"
Abin yankan Farcen ta ajiye da karfi saman table din glass din wanda hakan ya saka wajen yin kara ta mike tsaye, sannan ta dan duka ta dafa hannayenta bibiyu saman table din tana kallonta da idannuwanta dake nuna tsantsar bacin rai ta ce" zama da tsoho ai ya kare tunda kika auri tsoho da yarintarki dan son zuciya kika zauna, shirme ai ya kare a macen dake tunanin zata ci galaba a wajen namiji bayan tana kin y'ayansa, ke kam wawuya ce tunda har kike yiwa mijinki hauka a gaban kowa, ke din sakarai ce tunda har kike tunanin ihunki zai hanna wani abun rayuwa! Mazan nan da biyayarkima yaya kika gama da su? Bale ke tsagera karamar kwari?, shin mahaifiyarki ta rasu da kika rasa magaya ne ko me?"
Baki Mardiya ta daga zata yi magana da yannayin tsoron da ya darsun mata na yannayin UMMU, sai dai kafin ta yi UMMU ta zabura ta idasa matsawa kusa da ita sosai ta ce" dis, idan bakinki ya furta min A ba cikin kalmar da zaki hada dan gaishe ni ina maki rantsuwa da wanda raina ke hannunsa sai na sauke maki hakori irin yanda zan hukunta dan cikina, domin ke din y'ar cikina ce!"
Wuki wuki ta shiga yi da idannuwanta
Ummu ta juya ta fara tafia ranta a matukar bace, sai kuma ta tsaya ta juyo ta kalli MUTALAB da MARDIYA ta dan daga muryarta ta ce" me zan yi da aurensa? Bana so, ki kwontar da hankalinki in dan wannan kike hauka!"
Wannan kalmar ita ta fi batawa Abih rai, ya muke da sauri ya taka yana biye da UMMU wace ta kara saurinta zata shige dakin su NAJEEBA ya ce" NANA nine bakya so? Nine bakya so Nana? Sai me dan bakya so na, idan baki aureni ba mutuwa zan yi yo? Aman walahi ba wanda zaki aura in dai ina raye , mu zuba ni da ke"
UMMU ta juyo ta zazaro idannuwanta ta ce" mu zuba MUTALAB, idan an zo daura aurena ka hanna! "
Tana kokarin rufe bakinta sukai ido hudu da NAJEEBA wace yar hayaniyar ta fitar da ita, irin kallon da take mata ya saka jin kafafuwanta sun yi mata nauyi,
A hankali ta furta" NAJEEBA"
NAJEEBA ta lumshe idannuwanta zafafan hawaye suka zubo a kurmin idannuwanta, itama a hankali sannan a sanyaye ta furta" *sai kin aure shi MAMA, idan kuwa ba haka ba mu zuba*"
Tana gama fada ta juya da sauri ta yi dakin kannenta da aka kora su da niyar labarta masu abinda UMMU ke yiwa Abihnsu
Wani irin farin ciki ne ya saka UMMU jin saukar hawaye mai dumi a gurbin idannuwanta,
Ba na komai bane sai na wannan kalma da take ji daga bakunnan y'ayanta goma sha shida banda dayar, a yau ta fito daga bakinta cike da rigima ta hanyar turo dan bakinta mai kyau ta ce *MAMA* ,
Ajiyar zuciya ta sauke ta daga kafarta da sauri ta bi bayansu dan a yi komai a gabanta
Murmushi Abih ya yi ya juya da sauro da takamarsa ya zo wucewa ya jiyo ihun kulan Mardiya da ta yi dakinta da gudu tana maimaita ba zata yi zaman kishi da UMMU ba ya mikawa SHAHEED da ya talabe kuncinsa yana kallon ikon Allah hannu ya ce" a tayamu da adu'a su kara rikice mata har ta aminta sai ka daura mana aurenmu"
Shi kam Shaheed sai ya samu kansa shima da yin murmushin ya mika masa hannun suka gaisa ya juya ya yi ficewarsa
Dubansa ya maida Kan AMMI dake ta kalle kalle ya sakar mata murmushi ya mike ya karasa kusa da ita
Hannunta ya dauka na dama ya manawa bayan hannun nata kiss a hankali ya ce" AMMI, i lv u"
Murmushi AMMI ta yi tana kallonsa cike da kaunarsa,
Ya ce" zan je, Ammi zan dawo idan har ban samu gamsuwa da irin hukuncin Umani ba"
Ita dai tana mai binsa da murmushin har ya tafi
Kamar yanda ya fada masu hakan ne ya kasance, a zaunen ya tarar da matansa biyu su duka sun sha kwaliyarsu sai kamshin turare dake tashi, aunna zaune a kujeru masu nesa da junna ba wada ke yiwa yar uwarta magana
Da mamakin ganninsa ba rawani, da shiga irin ta jaruman maza du suka bi shi da kallo
Sunna jira ya zauna ya hakimce su kai gaisuwa sai suka ga ya ja ya tsaya a tsakiya,
Muryarsa a dake ya ce" shin daga baya kika fasa ko menene dalili?"
Zinaria dake kallonsa gannin maganar da ita yake ta kara buda kunnayenta dan jin a kan abinda yake magana,
Sai kuma ta ga ya juya wajen NADIA itama a kausashen ya furta" Daga baya kika fasa ko tunda kika zo baki san wannan shine abu na farko a cikin layin abinda zaki yi dan samun dorewar zama da ni tare da kwonciyar hankali da nutsuwa ba? Shin baki san shine dalilin da ya saka na yi dogayen hanyoyin da zasu kai kowacenku wajen ba tare da ta fito ta bi cikin baban gida ba?"
Kara sada kanta ta yi itama cikin rudu, aman ta kasa furta komai domin a ganninta Zinaria itace baba itace ta san kan mai gidan gannin bata ce komai ba sai itama ta yi shirun ta kara sada kanta sosai
SULTAN ya ajiye wayarsa saman table a hankali ya ce" ku kiyaye"
Gannin yana niyar shigewa ciki ya saka ZINARIA kara saukowa ta rage muryarta sosai ta ce" Allah ya taimake ka, shin a kan me kake magana?"