Sashe 93
Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta budi bakinta ta fara magana kamar haka" Allah ya taimaki sarki, Allah ya ja da rai ya ara maka nisan kwana, sannu da hutawa zakaran gwajin dafa, sannu da warhaka takawa"...................
Lafuzanta ne suka yanke sakamakon hannunsa da ya dora daidai bakinta yana kallonta
Idannuwanta ta dago tana kallonsa itama da duba irin na tarin soyayarsa da tarin jin haushinsa da tarin jin tsoronsa
Dayan hannunsa ya saka ya kama hannun nata dake jimke ya ajiye saman cinyarta kafin ya saka hannayen nasa baki daya ya dagota tsaye shima yana mikewar ya kasance sunna mikewa a tare
Wajen doguwar kujerar falon ya kai dubansa, sai dai yana kallo sai da aka hasko masa lamarinta mai girman gaske a idannuwansa
A hankali ya lumshe idannuwansa ya samu kansa da jin zuciyarsa na rike sunnanta a ciki ciki
Dubansa ya kai saman kujerar da kyau, idannuwansa sun hasko masa abinda ya sha'afa bai goge da kansa ba, dan murmushi yake jin na son kwace masa sai dai ya ki barin hakan ya faru ya gimtse fuskarsa da kyau
A hankali ya karasa wajen zama da ita ya zaunar da ita, sai kara sada kai take irin na girmamawa tamkar wace ta zo gaban sarakuwarta farin haduwar nan
Hannunsa na dama ya saka a nitse ya dago habarta yana dubanta
Muryarsa ya sanyaya sosai, sannan a rarabe a hankali irin ya yi niyar cadin da ita yau ya ce" haba Zinariana, shin bakya gajiya da kirarin nan da kike min bayan daga ni sai ke?"
Da mamaki take kallonsa, shi kirarin ne baya so? Ai ita kirarin nan shine karin fasa kanta da sakawa ta ringa taku daidaya, idan ana kodatan nan ko dogon fushi bata iya yi, kai ita da ko shi zai mata kirarin zata washe masa hakora ne!
Shaheed ya kuma dago dubanta ya ce" ki dubeni cikin ido, ki min magana da girmamawar da miji kan iya samu a wajen matarsa, yaya zan zama sarki a waje haka kuma a dakina? Oya yi min zancen soyaya"
Gaba daya wannan karron ta idasa kuro idannuwanta tana kallonsa, muryarta a dan rikice ta ce" zancen soyaya kuma? Da kai?"
Shima abin sai ya bashi daria a kasan zuciyarsa, sai dai bai yin ba ya ce" Zinaria da wa zaki yi idan ba da ni ba? Na maki tsufa ne?"
Sai kawai ta ringa kakare hada ido da shi, tana ta kare fuskarta cike da wani lamari na mamakinsa, shi sarki guda yake magangannun nan? Su an hore su da yi masa kirari da koda shi da fadin ya yi kaza ya fi wane, haka mahaifiyarsu ke yiwa mahaifinsu ko a gaban waye, ahine shi zai kawo wasu magangannu? Sai kawai ta ringa jin zuciyarta ba dadi sakamakon tunanin da ta saka mata a cikin kwakwaluwarta, 'yaya aka yi a da bai ce yana son soyaya ba sai yanzu? Ko dai wannan karuwar bak'ar yar ya fara kulawa?'
Sai da gabanta ya fadi kafin ta kale shi a tsorace, shi kuwa kallon irin yanda du ta rame, an yi mata kwaliya kamar yanda ta saba zuwar masa da kwaliya sai dai raka sosai ta bayana kanta a tare da ita
A hankali ya kai hannunsa, domin ya rigaya ya yiwa kansa alkawarin zai ta lalabata har ta saki, dan kuwa ya ga wani labari da aka yi posting na irin yanda mata ke ji idan za'a masu kishiya, da irin shawarwarin da namiji ya dace ya bi dan gannin ya kwontarwa da matarsa hankali ta dan nustu a kan maganar, a sanyaye ya furta" yaya jikin ki?"
Zinaria ta kara kikifta idannuwanta sai ga hawaye, a hankalin itama ta ce" jikina gayanan dai, shine na zo neman alfarma a wajenka, ina so mu je gida tare da AYYA a yi min magani sannan hankalina ya kwonta kafin na dawo"
Hankalinsa a kanta sosai ya ce" wani irin magani ne da ba zan iya nema maki shi a nan ba? Ko fita ta kama ni mai kaiki ne da kaina, wani irin kwonciyar hankali kike so wanda sai kin yi nisa da dakin mijinki?"
Du magangannunsa na yau, da irin tsayinsu, da irin yanda yake yinsu cike da kulawa na cutar da ita, domin har baki take saki tana kallon jajayen lebunansa da yake dan motsawa a hankali, da idannuwansa da suka cenza launi sakamakon gajiya yana dan lumshe su yana bude su a hankali, sai kawai ya ringa birge idannuwan ganninta
Ita kanta bata san lokacin da bakinta ya furta" NAJEEBA ta tare ne?"
Kama sunnanta da ta yi ya saka masa jin gabansa ya fadi kamar wani wanda aka kaiwa wawan dukan bazata,
A hankali ya kuma kallon fuskarta, a yanda ya kula ko a haduwarsu ta farko ita ba NADIA bace a gabanta Najeeba ce,
Haka kawai sai yake jin ransa ba dadi sakamakon rashin jituwarsu, yau kuma ya fara jin abin a cikin ransa, sosai da sosai
A hankali yar fara'ar da ya ringa saki ya shiga harhadeta, ba dan komai ba sai dan kawai ba zai iya barawa wata cikinsu daman kawo masa maganar wata ko tambayoyi a kan wata ba, idan sunna so sun hadu su yi kishin su, shi abin daria yake bashi sosai domin ranar da aka yi dramar nan har wani hura hanci ya ringa yi daga bayan rawaninsa a kasan zuciyarsa kuwa ya ringa tunanin dama hudu ya jera ya ga iya gudun ruwansu
Fuskarsa a hade aman bai daga muryarsa da karfi ba ya ce" shin ina iya saka tsorin kar zafin kishin ki ya kaiki wajen da zaki kasa gano hanyar dawowa?" (Lauje)
Idannuwanta kawai ta kura masa tana kallonsa, sam ta kasa bashi wata amsar kuma, zafin kishi ne? Inama ace ana yiwa namiji kishiya da ta gwada yiwa SULTAN ta ga irin nasa kishin, shin shi baya jin kishi a ransa ne? ( to fah )
Hannunta ya kamo ya rike a nasa ya ce" ke ce babba, ba zan taba bada kofar da wata zata wulakanta ki ba, ba zan iya wulakanta ki ba domin ke din ke na fara sanni, ina mai rokonki a yau kan ki sanyayawa zuciyarki, ina da abubuwan yi masu girma da yawa, idan har kika talafa min ta hanyar kwontar da hankalinki kika ja yan uwanki a kan akida guda wato zaman lafia da zaman aure, ina mai tabatar maki zaki fi kowa jin dadin zama da ni"
Ya dan tsagaita yana ta sauke numfashi kafin ya dora da fadin" idan kuwa kika kiya Zinaria, ban san a wani kalar zaki iya wayar gari ki ganni ba, ban san idan zan iya fama kamar yaro ba, ban san idan zan iya zubar da shirme kamar wani wawa ba domin sunna na raya"
Yana gama fada ya saki hannun nata da ya riko , ya yi kokarin tashi ya mike tsaye, hakan ya sa ash color din jalabiyarsa sauka kasa
Da ido take kallonsa, ta tabata, ta tabata kennan ya tare da yarinyar nan? Sam bata wani tsinci wasu abubuwa a cikin bayanansa ba
A hankali zuciyarta ta ci gaba da yin kunci sosai da sosai,
Tabas shawarar da wannan mutumen ya kawo masu koda kuwa sun kiya da farko zasu yarda yanzun,
Ba zata iya yarda ya tara da wannan banzar ba!
Da sauri ta kara neman alfarmar tafiyarta garin agadez
Yana jinta sai kawai ya yi biris tamkar bai ji ba, ya shigewarsa cikin dakinsa mai dauke da harkar takardunsa da abubuwan nemansa
Baki daya sai ta ringa cika tana hawa tana jin idannuwanta na neman kara rufewa, sam bata wani yi yinkurin binsa ko neman kara lalabashi cikin ruwan sanyi ba, saima ta ji ai wannan tsana ce da nuna halin rashin damuwa da ita
Ranta bace again ta fice a fallon nasa ta nufi wajen mahaifiyarta
Tana zuwa ta udasa ta zauna kusa da ita
Wayar da Gimbiya ke yi ne ta ajiye ta ce" yaya ya yardan ne mu saka a kawo mana tkt ?"
Da yannayi na zata iya fashewa da kuka ta ringa girgiza kanta tana daga idannuwanta ta kai kan yayarta daya da ta rage wace itama mijinta a yau ya mata magana ta karshe cewar idan ba zata dawo dakinta ba ta zauna, tana kallonta ta ce" baki daya ya cenza, kamar ba Sultan dina ba, yau ni yake cewa na daina yi masa kirari na masa hirar soyaya, karshema kan maganar bai tanka min ba tun bayan da ya nunan shima yana iya sama min ko wani irin magani na lafiata!"
Gimbiya ta ce" wani irin kirari kuma? A cikin dakin naki da shi kike masa kirari?"
Da mamaki ta kalli mahaifiyar tata, ta ga dai tsakaninta da mahaifinta kirari babu lokaci, to wace irin magana ce wannan?
Gimbiya ta ja tsaki tana fadin" shashashar banza, to ba dole ya gama rainaki ba? Wai ke daga ke sai shima hirarki tsakaninki da shi kirari ne? Arrrrrrr da ke walahi"
Yayarta kuwa banda daria me zata yi ta ce" Auta wai Allah da gaske kike?"
Du sai suka daure mata kai, maimakun kuma su zaunar da ita, su fahimci ai ga matsalar baba da take kara nisantata da mijinta harma su nemi maganceta cikin ruwan sanyi sai abin ya shashance a daria suka shiga neman layin mai martaba dan su bi ta kansa ko zai amince masu da tafia da Zinariar, sai sheda mata ake yana kan waya wanda ya makale da wayar Zahrau yana karbar caji da lamura dan ya kara mata kwanaki cike da shagwaba
Lafuzanta ne suka yanke sakamakon hannunsa da ya dora daidai bakinta yana kallonta
Idannuwanta ta dago tana kallonsa itama da duba irin na tarin soyayarsa da tarin jin haushinsa da tarin jin tsoronsa
Dayan hannunsa ya saka ya kama hannun nata dake jimke ya ajiye saman cinyarta kafin ya saka hannayen nasa baki daya ya dagota tsaye shima yana mikewar ya kasance sunna mikewa a tare
Wajen doguwar kujerar falon ya kai dubansa, sai dai yana kallo sai da aka hasko masa lamarinta mai girman gaske a idannuwansa
A hankali ya lumshe idannuwansa ya samu kansa da jin zuciyarsa na rike sunnanta a ciki ciki
Dubansa ya kai saman kujerar da kyau, idannuwansa sun hasko masa abinda ya sha'afa bai goge da kansa ba, dan murmushi yake jin na son kwace masa sai dai ya ki barin hakan ya faru ya gimtse fuskarsa da kyau
A hankali ya karasa wajen zama da ita ya zaunar da ita, sai kara sada kai take irin na girmamawa tamkar wace ta zo gaban sarakuwarta farin haduwar nan
Hannunsa na dama ya saka a nitse ya dago habarta yana dubanta
Muryarsa ya sanyaya sosai, sannan a rarabe a hankali irin ya yi niyar cadin da ita yau ya ce" haba Zinariana, shin bakya gajiya da kirarin nan da kike min bayan daga ni sai ke?"
Da mamaki take kallonsa, shi kirarin ne baya so? Ai ita kirarin nan shine karin fasa kanta da sakawa ta ringa taku daidaya, idan ana kodatan nan ko dogon fushi bata iya yi, kai ita da ko shi zai mata kirarin zata washe masa hakora ne!
Shaheed ya kuma dago dubanta ya ce" ki dubeni cikin ido, ki min magana da girmamawar da miji kan iya samu a wajen matarsa, yaya zan zama sarki a waje haka kuma a dakina? Oya yi min zancen soyaya"
Gaba daya wannan karron ta idasa kuro idannuwanta tana kallonsa, muryarta a dan rikice ta ce" zancen soyaya kuma? Da kai?"
Shima abin sai ya bashi daria a kasan zuciyarsa, sai dai bai yin ba ya ce" Zinaria da wa zaki yi idan ba da ni ba? Na maki tsufa ne?"
Sai kawai ta ringa kakare hada ido da shi, tana ta kare fuskarta cike da wani lamari na mamakinsa, shi sarki guda yake magangannun nan? Su an hore su da yi masa kirari da koda shi da fadin ya yi kaza ya fi wane, haka mahaifiyarsu ke yiwa mahaifinsu ko a gaban waye, ahine shi zai kawo wasu magangannu? Sai kawai ta ringa jin zuciyarta ba dadi sakamakon tunanin da ta saka mata a cikin kwakwaluwarta, 'yaya aka yi a da bai ce yana son soyaya ba sai yanzu? Ko dai wannan karuwar bak'ar yar ya fara kulawa?'
Sai da gabanta ya fadi kafin ta kale shi a tsorace, shi kuwa kallon irin yanda du ta rame, an yi mata kwaliya kamar yanda ta saba zuwar masa da kwaliya sai dai raka sosai ta bayana kanta a tare da ita
A hankali ya kai hannunsa, domin ya rigaya ya yiwa kansa alkawarin zai ta lalabata har ta saki, dan kuwa ya ga wani labari da aka yi posting na irin yanda mata ke ji idan za'a masu kishiya, da irin shawarwarin da namiji ya dace ya bi dan gannin ya kwontarwa da matarsa hankali ta dan nustu a kan maganar, a sanyaye ya furta" yaya jikin ki?"
Zinaria ta kara kikifta idannuwanta sai ga hawaye, a hankalin itama ta ce" jikina gayanan dai, shine na zo neman alfarma a wajenka, ina so mu je gida tare da AYYA a yi min magani sannan hankalina ya kwonta kafin na dawo"
Hankalinsa a kanta sosai ya ce" wani irin magani ne da ba zan iya nema maki shi a nan ba? Ko fita ta kama ni mai kaiki ne da kaina, wani irin kwonciyar hankali kike so wanda sai kin yi nisa da dakin mijinki?"
Du magangannunsa na yau, da irin tsayinsu, da irin yanda yake yinsu cike da kulawa na cutar da ita, domin har baki take saki tana kallon jajayen lebunansa da yake dan motsawa a hankali, da idannuwansa da suka cenza launi sakamakon gajiya yana dan lumshe su yana bude su a hankali, sai kawai ya ringa birge idannuwan ganninta
Ita kanta bata san lokacin da bakinta ya furta" NAJEEBA ta tare ne?"
Kama sunnanta da ta yi ya saka masa jin gabansa ya fadi kamar wani wanda aka kaiwa wawan dukan bazata,
A hankali ya kuma kallon fuskarta, a yanda ya kula ko a haduwarsu ta farko ita ba NADIA bace a gabanta Najeeba ce,
Haka kawai sai yake jin ransa ba dadi sakamakon rashin jituwarsu, yau kuma ya fara jin abin a cikin ransa, sosai da sosai
A hankali yar fara'ar da ya ringa saki ya shiga harhadeta, ba dan komai ba sai dan kawai ba zai iya barawa wata cikinsu daman kawo masa maganar wata ko tambayoyi a kan wata ba, idan sunna so sun hadu su yi kishin su, shi abin daria yake bashi sosai domin ranar da aka yi dramar nan har wani hura hanci ya ringa yi daga bayan rawaninsa a kasan zuciyarsa kuwa ya ringa tunanin dama hudu ya jera ya ga iya gudun ruwansu
Fuskarsa a hade aman bai daga muryarsa da karfi ba ya ce" shin ina iya saka tsorin kar zafin kishin ki ya kaiki wajen da zaki kasa gano hanyar dawowa?" (Lauje)
Idannuwanta kawai ta kura masa tana kallonsa, sam ta kasa bashi wata amsar kuma, zafin kishi ne? Inama ace ana yiwa namiji kishiya da ta gwada yiwa SULTAN ta ga irin nasa kishin, shin shi baya jin kishi a ransa ne? ( to fah )
Hannunta ya kamo ya rike a nasa ya ce" ke ce babba, ba zan taba bada kofar da wata zata wulakanta ki ba, ba zan iya wulakanta ki ba domin ke din ke na fara sanni, ina mai rokonki a yau kan ki sanyayawa zuciyarki, ina da abubuwan yi masu girma da yawa, idan har kika talafa min ta hanyar kwontar da hankalinki kika ja yan uwanki a kan akida guda wato zaman lafia da zaman aure, ina mai tabatar maki zaki fi kowa jin dadin zama da ni"
Ya dan tsagaita yana ta sauke numfashi kafin ya dora da fadin" idan kuwa kika kiya Zinaria, ban san a wani kalar zaki iya wayar gari ki ganni ba, ban san idan zan iya fama kamar yaro ba, ban san idan zan iya zubar da shirme kamar wani wawa ba domin sunna na raya"
Yana gama fada ya saki hannun nata da ya riko , ya yi kokarin tashi ya mike tsaye, hakan ya sa ash color din jalabiyarsa sauka kasa
Da ido take kallonsa, ta tabata, ta tabata kennan ya tare da yarinyar nan? Sam bata wani tsinci wasu abubuwa a cikin bayanansa ba
A hankali zuciyarta ta ci gaba da yin kunci sosai da sosai,
Tabas shawarar da wannan mutumen ya kawo masu koda kuwa sun kiya da farko zasu yarda yanzun,
Ba zata iya yarda ya tara da wannan banzar ba!
Da sauri ta kara neman alfarmar tafiyarta garin agadez
Yana jinta sai kawai ya yi biris tamkar bai ji ba, ya shigewarsa cikin dakinsa mai dauke da harkar takardunsa da abubuwan nemansa
Baki daya sai ta ringa cika tana hawa tana jin idannuwanta na neman kara rufewa, sam bata wani yi yinkurin binsa ko neman kara lalabashi cikin ruwan sanyi ba, saima ta ji ai wannan tsana ce da nuna halin rashin damuwa da ita
Ranta bace again ta fice a fallon nasa ta nufi wajen mahaifiyarta
Tana zuwa ta udasa ta zauna kusa da ita
Wayar da Gimbiya ke yi ne ta ajiye ta ce" yaya ya yardan ne mu saka a kawo mana tkt ?"
Da yannayi na zata iya fashewa da kuka ta ringa girgiza kanta tana daga idannuwanta ta kai kan yayarta daya da ta rage wace itama mijinta a yau ya mata magana ta karshe cewar idan ba zata dawo dakinta ba ta zauna, tana kallonta ta ce" baki daya ya cenza, kamar ba Sultan dina ba, yau ni yake cewa na daina yi masa kirari na masa hirar soyaya, karshema kan maganar bai tanka min ba tun bayan da ya nunan shima yana iya sama min ko wani irin magani na lafiata!"
Gimbiya ta ce" wani irin kirari kuma? A cikin dakin naki da shi kike masa kirari?"
Da mamaki ta kalli mahaifiyar tata, ta ga dai tsakaninta da mahaifinta kirari babu lokaci, to wace irin magana ce wannan?
Gimbiya ta ja tsaki tana fadin" shashashar banza, to ba dole ya gama rainaki ba? Wai ke daga ke sai shima hirarki tsakaninki da shi kirari ne? Arrrrrrr da ke walahi"
Yayarta kuwa banda daria me zata yi ta ce" Auta wai Allah da gaske kike?"
Du sai suka daure mata kai, maimakun kuma su zaunar da ita, su fahimci ai ga matsalar baba da take kara nisantata da mijinta harma su nemi maganceta cikin ruwan sanyi sai abin ya shashance a daria suka shiga neman layin mai martaba dan su bi ta kansa ko zai amince masu da tafia da Zinariar, sai sheda mata ake yana kan waya wanda ya makale da wayar Zahrau yana karbar caji da lamura dan ya kara mata kwanaki cike da shagwaba