← Book details Mage Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 28 OF 138

Sashe 28

Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bayan wata dankareriyar mota fara kar suka shiga su dukansu
Direba ne gaba da wani bajimin dogari zaune fuskar nan tasa uwa an zagi mamansa sam ba fara'a

Da wani irin gudu yake ratsa manyan titunnan garin fit fit fit
Kasancewar motar da number gidan sarki ne ya saka sojojin dake hanya da polisai sam basa gigin tsayar da ita duda ba sarkin ne a ciki ba

A hankali NAJEEBA ta ce" *kudi* masu gidan rana kuna gannin mutannen mu da su sai kallo basa tsayar da motar dan tambayar takarda

Ummulkhair ta yi murmushi ta ce" aa Najeeba, sarauta dai
Kudi ai kowama yana iya yinsa
Sarauta kuwa gado ce
Ko baran gidan sarki wani ne a cikin garin sarki bale ka shiga wannan mota? Inaga ko kwaya ka dauko zaka samu hanyar shiga da ita je ba tare da an san ko meye a motar ba

Najeeba ta lumshe idannuwanta ta furta" *Sarauta* wani sa'in sai ma ga sarauta ta cika izgili
Kun ga cewa a fada aka daura auren nan? Maimakun gidan su budurwar tasa?

Zahrau ta yi murmushi tana kallonta ta ce" baba da karamin kennan

Najeeba ta yatsina fuskarta ta ce" ai shi girma ko wani iri ne hawa yake yana sauka
Akoy wajen da zaki ga girman zai samu yaya wanda dole zai sada
Idan har sarki nada zuciya a cikin kirjinsa.......to tabas zai saurari kidan wace ke motsa masa ita

Ummukulsum dake kallon wajen da suka tsaya ne ta yi murmushi duba da irin wajen da sarki ya dauko mace
Tabas ta yarda a yanzu cewa sarkinsu baya mu'amalantarka dan kana mai kudi ko talaka
Yana mu'amalantar kowa ne bisa tsarin da ya zo masa

Ashe da wata motar a bayansu wace ke dauke da wasu yan matan bayi su su shida
Irin kayan gidan sarautar ne a jikinsu sun yi kwaliya daidai misali
Hannayensu dauke da sako du suka layu a bayan su NAJEEBA

A hankali suka ringa takawa inda Dogarin nan ke ta fama wajen ture yaren dake son taba su Najeeba, wajen kaiwa du wani wanda ya janyo waya dan yi masu hoto ba tare da sun amince da hakan ba

Gannin gidan cike da jama'a ya saka dogarin sada kansa da neman alfarmar su koma mota ya fitar da mutanen ciki

Da sauri Zahrau ta girgiza masa kai a fili ta furta" zamu cudu da su dan bama kyamatarsu

Murmushi Najeeba ta sakar mata da ido ta jinjina mata

Duda hakan sai da ya fara shiga ya shela cewa a bada hanya kannen mai martaba na tafe
Sannan ya dawo da sauri ya koma gefensu da zabgegoyar bulaliyarsa a hannunsa yana kuma sama masu hanya sunna ratsawa a hankali a hankali

Kallo fa ana binsu da shi gaba daya sun mimike sunna faman yi masu sannu

Wani daki aka nufa da su wanda suke tunanin a ciki amaryar take

Zaune take da zumbulelen hijab dinta da kawayenta su hudu
Ba kujeru a dakin sai tabarma su kansu sunna zazaune ne saman wata yar katifa wace take ta kanninta domin dakin kanninta ne

Kanta a sade yake tana jin gabanta na faduwa cike da tsoron dago da kanta dan gannin kannen mijin nata
Har yanzu ta kasa gaskata cewa ita Bintu itace ta zama matar mai damagaram
Zata iya rantsewa cewa bata taba gannin fuskarsa ba ko a hoto, haka kuma idan dai ta hange shi to sun fita kallon hawan sarki ne da yake yi ana gobe sallah wanda ke shaidawa al'umar garin cewa sallah ta kama a washe gari ne

Takan hangi hannunsa daya tak dake rike da igiyar dokinsa dayan kuwa a cikin alkyabarsa
Farin hannun wanda ke dauke da wasu irin jijiyoyin sai idannuwansa dake dauke da kwali wa'inda idan ya juyo yana mai bin jama'ar garinsa da kallo sannan yana dan amsa gaisuwarsu da ihun kiran sarkin da suke sunna biye da tawagar
Wai yau ita Bintu yar gidan malan sulaiman itane Allah ya yi zata tare a gidan sarki?
Ko a baiwa bata taba hasaso kanta ba
Hakan ya hadasa mata rawar jiki cike da tsoron kannensama kafin a kai kansa
Tana cike da zulumi da tsoron matarsa da aka yi tataki a jiya aka zo aka baiwa iyayenta labarin wacece Zinaria
Ta san cewa ita tana kasa da ita ne, ita talakarta ce, dan haka zata nemi masalaha da ita tun kafin ta gagari zama a damagram

Daburcewa yan matan suka yi wata na faman bara ta samo kujeru, wara na kallon abin shansu da cinsu da baki daya suka kare saura kadan kadan dan sun yi taro kamar me duda a kure lokacin ya zo ko anko basu samu sun yi ba

Da sauro dayar ta ce" bara na je shagon kalamu na samo jus

Da kallo Najeeba ta bita har ta fita

Kujeru ne dogarin nan ya ja daga kofa ya yi salama yana rike da su
Bashi da hurumin shiga wajen da matar sarki take kai tsaye hakan ya saka shi tsayawa daga kofa da kujerun da ya fita da gudu ya sauke mutane ya dauko

Najeeba ta bi hannunsa da kallo
Kujerun da alama zasu yi nauyi gashi itane karama a cikinsu
Matsalar bata daukan abu mai nauyi gaskiya dan haka ta juya ta koma cikin dakin da du suka bubude windows din dakunnan ta kakabe tabarmar nan ta dube su da murmushi a fuskarta ta furta" bismillah

Ba tare da wani damuwa ba yayun nata suka zazauna baki dayansu

NAJEEBA kuwa ta kai dubanta wajen amaryar

A hankali ta shiga takawa ta karasa kusa da bed din

Baki baki ta zauna cikin nutsuwa ta saka hannunta ta dago habarta wanda hakan ya saka baki dayansu jin gabansu ya fadi
Ita Najeeba gabanta ya fadi ne a kan dalilin da bata sani ba
Ita kuwa gabanta ya fadi ne jin wani irin lalausan hannu ya taba fuskarta wanda zata iya rantsewa hannun nan ya fi fuskarta laushi

Da sauri ta sada kanta, yar karamar muryarta na rawa rawa ta ce" Barkanku da isowa

Subahannalah
Najeeba ta furta a kasan zuciyarta
Bata so haka ba!
Sam bata so haka ba!
Ta yaya za'ayi wannan ta iya kwatar kanta a wajen Zinaria? Yarinyar kamaninta sam basu nuna yannayi na wada ta iya fada ko ta san tsatsaya a rayuwarta ba
Yarinyar gaba dayanta yannayi na wata irin saliha ne a tatare da ita

Haka kawai ta ji ranta na bacewa domin ita ba haka ta so ba,
ta so ace wada ya auran nan ta ci ubam Zinariya a iya iskanci sai su ga ta iskanci

Muryarta a sanyaye ta ce" yaya sunnan ki?

Bintu ta kara sada kanta ta ce" sunna na Bintu

Najeeba ta gyada kanta ta kai dubanta wajen kawayen nata
Su kansu basa yannayi da yan iska
Aman a kan me zai tashi ya wani dauko saliha haka? Wannan ai wulakanci ne salon banzar matarsa ta wulakanta yar mutane?

Cikin nutsuwa Najeeba ta ce" ku dakata daga kofa, lokaci na tafia zamu kimtsa gimbiya

Gaba daya suka yi waje bayan sun risina sun kara gaishe su

Tabatarwar da suka yi cewa ta yi wanka mahaifiyarta na zaune tana kallo Najeeba ta buda akwatinta na kayan mak up

Cikin nutsuwa ta shiga gabatar da aikinta cikin wata irin kwarewa wace a dan kankannin lokaci yar budurwar ta kara wani irin fresh da ita ta kara wani irin kyau hancinta ya fito zuwat sa shi yana wani irin sheki

Gaba daya yarinyar kanta ce mai kyau, wani irin nutsatsen kyau mai birgewa

Turaran wuta suka shiga yi mata ita kanta kafin su dora kayan da suka zo da su suka shiga turare mata su baki daya

Mahaifiyarta na rike da turaren ruwan da suka bata concentrer mai wani irin dadi tana shafa mata lungu lungu na jikinta

Daidai da pant dinta sai da suka turara mata sannan suka bata baya ta saka sabuwar bra din da pant din

Taimaka mata suka yi wajen suturta mata jikinta da suturar da aka zo mata da ita wani farin lesh ne mai wani irin laushi
Dinkin ya karbi Bintu sosai
Nan Najeeba ta kuma zaunawa da agraf dinta tana kashe mata daurin dan kwali tana dantse shi yanda zai zauna
Dole yarnan ta birgeka
Saima da suka rufa mata alkyabarta mai dauke da wani irin ado tamkar dawisu

da ta kalli kanta a madubi sai kawai ta fashe da kuka ta fada jikin mahaifiyarta tana jin gaban kirjinta na dokawa
Ashe zata ga irin wannan daukaka daga Allah kafin ta mutu?

Mahaifiyarta na mata murmushi ta rasa inda zara ajiyeta domin sai ta ga katifar nan ba zata zaunu da alkyabar nan ba

Zahrau ta kamata tana murmushi itama ta zaunar da ita suka sakata tsakiya suka kashe hoto nan suka fito reras da su tamkar ka sace su ka gudu

Sakwanin aka ringa ajiyewa kala daban daban kafin su yi masu salama a lokacin har an shiga salar magariba suka fito
Tuni kuma motoci sun fara layuwa dan daukan amaryar mota hudu ce kawai dan ba'a so a ga shigarta ta kofar baya idan ya so daga baya sai a kawo mutane

Su dai daukansu ya yi ya maida su fada

Sunna fita Najeeba ta tserewarta dan tana son zuwa ta shaki iskar duniya ta ji sanyi na ratsa mata jikinta

Motar yaya Dayabu ta shiga ta tayar abinta ta tafi siyan ice cream

Zuwa lokacin da ta nufi wajen hutunta wanda rabonta da wajen yau kwana hudu kennan tuni an kira isha

Da piyawatanta a mota da kuma abin sallah
Tana sauka daga motar ta dauki piyawatan

Gefe ta koma ta daura alwalarta sannan ta dawo cikin motar ta dauko salayarsa ta dauko alkyabarta

A nan ta shinfida cikin nutsuwa ta tayar da sallarta

Sai da ta gama baki daya sannan ta mike ta mayar cikin motar ta cire alkyabar ta dauko ledar ice cream dinta da wayarta

Tun da ta tinkaro wajen ta dan ja ta tsaya sakamakon gannin mutumen nan zaune kansa sade
Yau kuma irin shigarsa sai ta sakata kara kallonsa da kyau
Dan waigawa ta yi ko zata ga motar da ta kawo shi? Sai dai hata ga mota ba
Chapter 28 · 0% Book details