Sashe 11
Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ummukulsum ta ja tsaki ta ce" shine kike kuka? Kike kuka dan namiji yace ya fasa aurenki? Da me kuke jira ku a duniyarmu? Koda mun yi auren za'a sako mu ba tare da an waiwayemu ba, idan mun fito da ciki za'a irga mana ranakun haihuwarmu muna haihuwa za'a dauke dan a kaishi nesa da mu
Me kuke jira? Me kuke tunani a rayuwarmu? Yanda ya yiwa y'ayan wasu, yanda ya ringa wulakanta y'ayan mutane yana saki a kan dalilinsa na son zuciya dole sai muma an ringa sako mu ana laya masa zawarawa,
Dole sai mun cika masa gidan nan mun tsufa tare mun mutu tare......
Wani gigitacen marin da ya sauka a kan fuskarta wanda ya tsorata yan uwanta ya saka su zabura sunna kallon wanda ya yi marin a firgice ya sakata dantse harshenta har jinni ya fito na walaha
Kafin su yi wani abu ya warci igiyar cajin dake ajiye ya shiga laftar du wanda hannunsa ya kai...kun san balarabe idan ya tashi dukan yaro yakan yi masa duka kamar zai kashe shi
Mahaifinsu baya duka a banza, aman du randa hannunsa ya daga sai ya daka
Da wani irin tsinanen gudu DAYABU ya warci kananun biyu ya fada dakin NAJEEBA wace ta rigayi kowa guduwa
Yana shigowa suka dantse kofar wanda hakan ya saka uban nasu dukan kofar ransa bace yana jijigawa
Ransa a matukar bace ya ce" bude min, marar kunyar banza marar kunyar wofi, bude min ki fada min maganar banza a gabana
Ummu ni ne zaki yiwa fatan na maku aure a sako ku? Kennan ni jarabawar sake saken mata ba zata iya samuna ba ko? Zahrau shine kika zagar masa uwa kika ce masa shege?
DAYABU shine ka saka su gaba sunna munanan kalamai a kaina ba zaka tataka su ba?
Khairy shine kina ji ta zagar maki uba baki mareta ba?
Najeeba me ya hada ki fada da dan gidan docter Basheer?
Hannunsa ya saka ya kara dukan kofar NAJEEBA wace ita ta fi kusa da shi kafin ya zame ya zauna a jikin kofar yana sauke ajiyar zuciya
Dawowarsa kennan ya tarar da wanda ke neman auren Zahra da mahaifiyarsa da kawayanta biyu a kofa sunna jiransa mai gadi ya hanna su shigowa sai kunfar baki suke wai sai ta fada masu a inda ta ga ta yi shegu
Dama tun a hanya inda ya tsaya siyan fruits ya tsinci maganar fadan NAJEEBA harma ta summa
Daga cen ya nufi asibiti aka shaida masa yayanta ya daukota an sake su
Shine ya shigi ya tarar da Ummu na fadin irin wadinnan magangannun wai koda sun yi aure za'a sako su ne da ciki ko daga sun haihu a sake su
Idannuwansa ya lumshe ya yi shiru yana tunanin rayuwa
A jiya ya so kwarai ya saki Mardiya, sai dai gannin yanzu y'ayan nasa kansu sun fara fada masa magana a kan auri sakinsa ya saka shi kyaleta domin ba'a taba masa y'aya a wanye lafia
Idannuwansa ya kuma lumshewa yana tunanin inda zai bi ya yiwa tufkar hanci, ya zama wajibi ya katse hanzarinta, ya zama wajibi ya yiwa tufkar nan hanci idan kuwa ba haka ba lale watarana y'ayan nasa zasu yi abinda zasu zubar da hawayen jinni, zasu ja sirrin da yake binnewa ya fito fili
Zasu saka baki daya su tatara su bar kasar a lokacin da suka zama abin kyamata sannan abin gori a cikin kasar nan
A hankali ya ce" ku fito
Du sun ji shi, aman ba wanda ya yi yinkurin fitowa
Ajiyar zuciya ya kuma saukewa ya ce" ku fito, ba zan daki kowa ba
Zahrau ta fashe da kuka ta ce" ABIH, dan Allah ka yi hakuri
Muryarsa ya dan daga ya ce" magana nake so mu yi ku fito na fada maku ba zan daki kowa ba
Shiru suka kuma yi, wanda hakan ya saka shi sada kansa yana jin zuciyarsa ba dadi
Sam baya jin dadi a kasan zuciyarsa
Karar bude kofar da yake jingine ya saka shi sauri dagowa harma ya mike tsaye ya juyo yana son gannin wanda ya iya fitowa
A hankali ta fito tana matsowa kusa da shi hankalinta a kan fuskarsa
Shima idannuwansa ya sauke a nata fuskar
Lokaci daya ya ji wata kauna irin ta da da uba na mamaye zuciyarsa
A hankali ta daga kanta tana kallon fuskar nasa, idannuwanta da ta gama sannin sunna da effet a kan mahaifin nata koda ya tashi duka sunna saka shi dakawata
ta kara masu girma sosai sannan ta yi masu kwal kwal
Nan da nan kwallah ta cika su, bakinta take son budawa aman ta kasa
A hankali ta shiga kokarin riko hannayensa muryarta na rawa tana son fitar da lafazi ta kasa, sannan hannayen nasama ta kasa rikowa dan sai take gannin sun mata nisa sosai
Idannuwansa ya rintse sakamakon jin wani irin tausayinta ya gama halaka bacin ran nasa
Tsantsar kaunar y'ayansa yana matukar yin tasiri a rayuwarsa
Ko dan sun kasance mata da yawa wa'inda ya dauki son duniya ya dora masu?
A hankali ya kama habarta ya dan dago yana kallon kwayar idannuwanta
Muryarsa ya sanyaya ya ce" kuka zaki yi?
Jin ya sauko hawayenta suka samu damar zubowa tana kallonsa sai a lokacin kuma bakinta ya bude cikin sanyin murya sosai ta ce" kar ka dake mu Abih, ka ga an summar da ni bayan bani da laifi, ka ga ya zazageta dan kawai an fada masa abubuwa
Abih ina zamu shiga mu ji sanyi ne?
Da sauri ya kama hannayenta ya karasa kusan dakinta sosai
Muryarsa ya dan daga ya ce" ku zo gare ni, ku zo kun ji?
Jin irin yanda muryarsa ta sanyaya ya saka du suke budewa sunna fitowa
Du kusa da shi sosai suka zo suka zazauna wasun su har sunna dora hannunsu saman jikinsa
Murmushi ya yi yana kallon ZAHRA ya ce" Zahra, daga yau kar ki kuma zagin mutun da nasabarsa, ko dukiya, koma menene kin ji?
Na gwamace ace da ni gaki cen kun daku da mutun na je na raba da ki yi irin wannan abin, kin san me ya sa?
Kanta ta girgiza tana kallonsa, hakama sauran
Hannayenta ya riko ya ce" abinda ya sa shi mutun ba'a gama halitarsa, baya fasa gannin jarabawar rayuwa har sai ranar da aka saka shi cikin kabarinsa
Eh lale yin fari ne kadara, na biyu ganganci na uku kuwa da gangan
Aman koda y'aya goma ta haifa na hane ki yi mata gorin hakan domin ko ke kin tsufa zaki bar baya kin ji?
Kanta ta ringa gyadawa
Ya maida dubansa wajen Ummu ya yi murmushi ya ce" haba Umana, idan inada mumunan hali ai bana tunanin zaki kulaceni haka, na fi tunanin zaki min adu'a sannan ki yi fatan kar Allah ya jarabeni da ku, wato ya dora hakan a kanku dan na rantse maki ban san wani hali zan shiga ba, ki ringa kyakyawan fata kin ji?
Kanta ta ringa gyadawa itama tana share hawayen fuskarta
Hannun NAJJEBA dake cikin nasa ya kara rikewa yana kallonta, murmushi ya yi ya ce" ni ko dai kece jinnin abuna ba ni ba? Yaya aka yi da wahala safia ta yi dare ya yi baki yi fada ba? Allah ya shirye ki
Kanta ta kifa saman cinyarsa
Ya kai dubansa wajen DAYABU dake tsaye da NAJEEB a hannunsa wanda ya ki yarda ya sauka daga hannun nasa tun da ya tsorata kar aban nasu ya dake shi
Murmushi ya masa mai tsayawa a rai kafin yana kallonsa ya ce" wa ya ce maku baku da wajen da zaku je ku ji sanyi?
Kunada wajen da zaku je ku ji sanyi sosaima
Ina raye, a doron kasa ai zan kasance maku katifar da zaku zo ku kwonta
Tunda shi ya fasa aurenta, dama yana neman hanyar silibe mata ne, da izinin Allah, Allah zai fitar maki da miji na gari
Murmushi DAYABU ya yi gannin du sun dodora kansu jikin Aban nasu
Dan haka ya karasa da najeeb a hannunsa ya ringa dauko ledojin dake dauke da burger din yana kawowa yana ajiyewa
Nan fa suka baje abincin, inda mahaifinsu ya fita ya je ya dauko yar karamar wace ta kai shekara uku a haife wajen uwarta ya dawo da ita bangaren y'ayan nasa inda uwar ta ringa cika tana batsewa ya zaunar da ita tsakiyarsu suka hadu sunna cin abincin sunna hira sunna wasa da daria tamkar ba sune suka shiga hali na matsananciyar damuwa yanzun ba
......................................
Da wani irin karfi ya diro daga saman bed din da yake kwonce a mike idannuwansa lumshe ya kai dubansa kan yaronsa da mamansa ta shigo da shi tana kuka tamkar ranta zai fita ta ajiye masa shi saman bed din hannayenta saman kanta sai jujuya kai take
Irin yanda zuciyarsa ta buga gannin yanda yaron ya mimike sannan jijiyoyin kansa sun yi rado rado sun yi tsanwa sharr idannuwansa na kallon sama sam baya motsi ba allamun motsi a tatare da shi
Hannunsa ya kai wanda ke wata irin rawa a hankali ya juyo yaron
Zinariya ta kara fashewa da kuka hankali tashe ta ce" ya mutu ko? Ya mutu?
Shaheed ya kalleta da sauri haka kuma zuciyarsa ta kara bugawa da karfi ya kara riko yaron ya ce"......
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
8
Da wani irin karfi ya juyo shi yana kuma kallon fuskarsa
Idannuwansa ya lumshe cike da tausayin kansa da kansa kafin ya rage tsayinsa ya shiga dodora hannayensa dan tabatar da abinda yake ganni a gabansa
Tsintsiyar hannunsa ya kama ya saurara da zuciyarsa dan kara tabatarwa kansa
Jikinsa a mace ya juyo wajenta inda ta yi tsaye tana jiran jin amsa
Wani ihu ta so saki, sai dai ta sake shi a cikin zuciyarta sakamakon rufe mata baki da ya yi da hannunsa na dama sanann ya talabeta da hannunsa na hagu
A hankali ya jata ya nufi falo baba da ita inda ta saki jikinta tamkar sumamiya tana gunjin kuka
Sunna fitowa falon a kujera ya zaunar da ita still bai saki bakinta ba
Me kuke jira? Me kuke tunani a rayuwarmu? Yanda ya yiwa y'ayan wasu, yanda ya ringa wulakanta y'ayan mutane yana saki a kan dalilinsa na son zuciya dole sai muma an ringa sako mu ana laya masa zawarawa,
Dole sai mun cika masa gidan nan mun tsufa tare mun mutu tare......
Wani gigitacen marin da ya sauka a kan fuskarta wanda ya tsorata yan uwanta ya saka su zabura sunna kallon wanda ya yi marin a firgice ya sakata dantse harshenta har jinni ya fito na walaha
Kafin su yi wani abu ya warci igiyar cajin dake ajiye ya shiga laftar du wanda hannunsa ya kai...kun san balarabe idan ya tashi dukan yaro yakan yi masa duka kamar zai kashe shi
Mahaifinsu baya duka a banza, aman du randa hannunsa ya daga sai ya daka
Da wani irin tsinanen gudu DAYABU ya warci kananun biyu ya fada dakin NAJEEBA wace ta rigayi kowa guduwa
Yana shigowa suka dantse kofar wanda hakan ya saka uban nasu dukan kofar ransa bace yana jijigawa
Ransa a matukar bace ya ce" bude min, marar kunyar banza marar kunyar wofi, bude min ki fada min maganar banza a gabana
Ummu ni ne zaki yiwa fatan na maku aure a sako ku? Kennan ni jarabawar sake saken mata ba zata iya samuna ba ko? Zahrau shine kika zagar masa uwa kika ce masa shege?
DAYABU shine ka saka su gaba sunna munanan kalamai a kaina ba zaka tataka su ba?
Khairy shine kina ji ta zagar maki uba baki mareta ba?
Najeeba me ya hada ki fada da dan gidan docter Basheer?
Hannunsa ya saka ya kara dukan kofar NAJEEBA wace ita ta fi kusa da shi kafin ya zame ya zauna a jikin kofar yana sauke ajiyar zuciya
Dawowarsa kennan ya tarar da wanda ke neman auren Zahra da mahaifiyarsa da kawayanta biyu a kofa sunna jiransa mai gadi ya hanna su shigowa sai kunfar baki suke wai sai ta fada masu a inda ta ga ta yi shegu
Dama tun a hanya inda ya tsaya siyan fruits ya tsinci maganar fadan NAJEEBA harma ta summa
Daga cen ya nufi asibiti aka shaida masa yayanta ya daukota an sake su
Shine ya shigi ya tarar da Ummu na fadin irin wadinnan magangannun wai koda sun yi aure za'a sako su ne da ciki ko daga sun haihu a sake su
Idannuwansa ya lumshe ya yi shiru yana tunanin rayuwa
A jiya ya so kwarai ya saki Mardiya, sai dai gannin yanzu y'ayan nasa kansu sun fara fada masa magana a kan auri sakinsa ya saka shi kyaleta domin ba'a taba masa y'aya a wanye lafia
Idannuwansa ya kuma lumshewa yana tunanin inda zai bi ya yiwa tufkar hanci, ya zama wajibi ya katse hanzarinta, ya zama wajibi ya yiwa tufkar nan hanci idan kuwa ba haka ba lale watarana y'ayan nasa zasu yi abinda zasu zubar da hawayen jinni, zasu ja sirrin da yake binnewa ya fito fili
Zasu saka baki daya su tatara su bar kasar a lokacin da suka zama abin kyamata sannan abin gori a cikin kasar nan
A hankali ya ce" ku fito
Du sun ji shi, aman ba wanda ya yi yinkurin fitowa
Ajiyar zuciya ya kuma saukewa ya ce" ku fito, ba zan daki kowa ba
Zahrau ta fashe da kuka ta ce" ABIH, dan Allah ka yi hakuri
Muryarsa ya dan daga ya ce" magana nake so mu yi ku fito na fada maku ba zan daki kowa ba
Shiru suka kuma yi, wanda hakan ya saka shi sada kansa yana jin zuciyarsa ba dadi
Sam baya jin dadi a kasan zuciyarsa
Karar bude kofar da yake jingine ya saka shi sauri dagowa harma ya mike tsaye ya juyo yana son gannin wanda ya iya fitowa
A hankali ta fito tana matsowa kusa da shi hankalinta a kan fuskarsa
Shima idannuwansa ya sauke a nata fuskar
Lokaci daya ya ji wata kauna irin ta da da uba na mamaye zuciyarsa
A hankali ta daga kanta tana kallon fuskar nasa, idannuwanta da ta gama sannin sunna da effet a kan mahaifin nata koda ya tashi duka sunna saka shi dakawata
ta kara masu girma sosai sannan ta yi masu kwal kwal
Nan da nan kwallah ta cika su, bakinta take son budawa aman ta kasa
A hankali ta shiga kokarin riko hannayensa muryarta na rawa tana son fitar da lafazi ta kasa, sannan hannayen nasama ta kasa rikowa dan sai take gannin sun mata nisa sosai
Idannuwansa ya rintse sakamakon jin wani irin tausayinta ya gama halaka bacin ran nasa
Tsantsar kaunar y'ayansa yana matukar yin tasiri a rayuwarsa
Ko dan sun kasance mata da yawa wa'inda ya dauki son duniya ya dora masu?
A hankali ya kama habarta ya dan dago yana kallon kwayar idannuwanta
Muryarsa ya sanyaya ya ce" kuka zaki yi?
Jin ya sauko hawayenta suka samu damar zubowa tana kallonsa sai a lokacin kuma bakinta ya bude cikin sanyin murya sosai ta ce" kar ka dake mu Abih, ka ga an summar da ni bayan bani da laifi, ka ga ya zazageta dan kawai an fada masa abubuwa
Abih ina zamu shiga mu ji sanyi ne?
Da sauri ya kama hannayenta ya karasa kusan dakinta sosai
Muryarsa ya dan daga ya ce" ku zo gare ni, ku zo kun ji?
Jin irin yanda muryarsa ta sanyaya ya saka du suke budewa sunna fitowa
Du kusa da shi sosai suka zo suka zazauna wasun su har sunna dora hannunsu saman jikinsa
Murmushi ya yi yana kallon ZAHRA ya ce" Zahra, daga yau kar ki kuma zagin mutun da nasabarsa, ko dukiya, koma menene kin ji?
Na gwamace ace da ni gaki cen kun daku da mutun na je na raba da ki yi irin wannan abin, kin san me ya sa?
Kanta ta girgiza tana kallonsa, hakama sauran
Hannayenta ya riko ya ce" abinda ya sa shi mutun ba'a gama halitarsa, baya fasa gannin jarabawar rayuwa har sai ranar da aka saka shi cikin kabarinsa
Eh lale yin fari ne kadara, na biyu ganganci na uku kuwa da gangan
Aman koda y'aya goma ta haifa na hane ki yi mata gorin hakan domin ko ke kin tsufa zaki bar baya kin ji?
Kanta ta ringa gyadawa
Ya maida dubansa wajen Ummu ya yi murmushi ya ce" haba Umana, idan inada mumunan hali ai bana tunanin zaki kulaceni haka, na fi tunanin zaki min adu'a sannan ki yi fatan kar Allah ya jarabeni da ku, wato ya dora hakan a kanku dan na rantse maki ban san wani hali zan shiga ba, ki ringa kyakyawan fata kin ji?
Kanta ta ringa gyadawa itama tana share hawayen fuskarta
Hannun NAJJEBA dake cikin nasa ya kara rikewa yana kallonta, murmushi ya yi ya ce" ni ko dai kece jinnin abuna ba ni ba? Yaya aka yi da wahala safia ta yi dare ya yi baki yi fada ba? Allah ya shirye ki
Kanta ta kifa saman cinyarsa
Ya kai dubansa wajen DAYABU dake tsaye da NAJEEB a hannunsa wanda ya ki yarda ya sauka daga hannun nasa tun da ya tsorata kar aban nasu ya dake shi
Murmushi ya masa mai tsayawa a rai kafin yana kallonsa ya ce" wa ya ce maku baku da wajen da zaku je ku ji sanyi?
Kunada wajen da zaku je ku ji sanyi sosaima
Ina raye, a doron kasa ai zan kasance maku katifar da zaku zo ku kwonta
Tunda shi ya fasa aurenta, dama yana neman hanyar silibe mata ne, da izinin Allah, Allah zai fitar maki da miji na gari
Murmushi DAYABU ya yi gannin du sun dodora kansu jikin Aban nasu
Dan haka ya karasa da najeeb a hannunsa ya ringa dauko ledojin dake dauke da burger din yana kawowa yana ajiyewa
Nan fa suka baje abincin, inda mahaifinsu ya fita ya je ya dauko yar karamar wace ta kai shekara uku a haife wajen uwarta ya dawo da ita bangaren y'ayan nasa inda uwar ta ringa cika tana batsewa ya zaunar da ita tsakiyarsu suka hadu sunna cin abincin sunna hira sunna wasa da daria tamkar ba sune suka shiga hali na matsananciyar damuwa yanzun ba
......................................
Da wani irin karfi ya diro daga saman bed din da yake kwonce a mike idannuwansa lumshe ya kai dubansa kan yaronsa da mamansa ta shigo da shi tana kuka tamkar ranta zai fita ta ajiye masa shi saman bed din hannayenta saman kanta sai jujuya kai take
Irin yanda zuciyarsa ta buga gannin yanda yaron ya mimike sannan jijiyoyin kansa sun yi rado rado sun yi tsanwa sharr idannuwansa na kallon sama sam baya motsi ba allamun motsi a tatare da shi
Hannunsa ya kai wanda ke wata irin rawa a hankali ya juyo yaron
Zinariya ta kara fashewa da kuka hankali tashe ta ce" ya mutu ko? Ya mutu?
Shaheed ya kalleta da sauri haka kuma zuciyarsa ta kara bugawa da karfi ya kara riko yaron ya ce"......
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
8
Da wani irin karfi ya juyo shi yana kuma kallon fuskarsa
Idannuwansa ya lumshe cike da tausayin kansa da kansa kafin ya rage tsayinsa ya shiga dodora hannayensa dan tabatar da abinda yake ganni a gabansa
Tsintsiyar hannunsa ya kama ya saurara da zuciyarsa dan kara tabatarwa kansa
Jikinsa a mace ya juyo wajenta inda ta yi tsaye tana jiran jin amsa
Wani ihu ta so saki, sai dai ta sake shi a cikin zuciyarta sakamakon rufe mata baki da ya yi da hannunsa na dama sanann ya talabeta da hannunsa na hagu
A hankali ya jata ya nufi falo baba da ita inda ta saki jikinta tamkar sumamiya tana gunjin kuka
Sunna fitowa falon a kujera ya zaunar da ita still bai saki bakinta ba