Sashe 35
Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai gata kuma an kawota a babur har kusa da motarsa
Karasa sauka ta yi tana yiwa mai babur ihun" ka yiwa Allah ka yi tafiyarka na ce ka bani cenji ne?
Sai hajia ya fada yana sara mata sannan ya tayar ya juya abinsa
Ja ta yi ta tsaya a wajen da take ta kasa karasawa wajen motar bale har ta shiga
Gaba daya ta gama yankewa kanta hukuncin idan dazu Allah ya kubutar da ita yanzun fa?
Zabura ta yi a lokacin da ta ga yana.........
More cmnt mr pag😌
[1/28, 10:58 PM] Ummu Sadeeq: 🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
20
Zabura ta yi a lokacin da ta ga ana sauke madubin bayan wanda ta tabata a nan yake zaune
Sosai aka zuge shi sannan ya sauke dubansa kakausan duban nan mai abin tsoro a kanta
Fitsarine ta ji zai zubo mata daga mararta
Da sauri ta juya ta matsa sosai tana dan rawar nan dan ta rike shi kar ya zubo
Haska wajen ta yi ta yi bismillah ta janye wandonta kasa kadan ta duka ta shiga fitsarin nan domin idan bata yi shi ta tabata zata yi shi a motar cen
Kansa ya yi saurin kawarwa daga wajenta, amintacensa kuwa dama kansa a sade yake yana cike da mamakin lalle yarinyar nan ta isa
Su suke tare da sarki SHAHEEd , wato gurnanin zaki
Su suka san waye Sarki SHAHEED
Yaya aka yi ta taka doka haka har haka?
Sai da ta kusan karasa fitsarin ta tuna bata da ruwan kama ruwa
Gaba daya ta ji jikinta ya kwashi wani yamyamyam na kyamar kazanta
Bata wasa da tsaftar wajen nan ko da wasa gashi yau ta yi fitsari a wajen nan sannan a gaban sarki gashi babu ruwa
Sai da ta gama sosai ta cire wandonta dan ba zara iya mayar da shi ba ta mike a hankali jikinta na ci gaba da rawa
Tana tunkaro motar ya kuma dagowa yana yi mata duba irin na mamakin fitsarine ta yi d agaske haka gabansu ? Lalee ta cika rashin kamun kai da rainin hankali
Kara datse lebensa ya yi na kasa yana gannin lokacin da ta karasa isowa ta ja ta tsaya daga nesa gaba daya jikinta na rawa hankalinta a matukar tashe baki daya wani kuzarinta ya bace sai tarin tsoron dake cin ranta
Dubansa ya cire daga kanta ya kalli wajen amintacensa
Sai da ya dauki mintunna kafin ya ce" bani faro
Da sauri ya buda wajen da ake saka ruwan ya dauko ya juyo gaba dayansa ya dan risina ya mikowa sarki
SHAHEED ya mika hannunsa na dama ya amsa yana rike da ruwan
Cen ya saka hannunsa zai bude hakan ya sa amintacensa saurin kokarin budewa dan ya bude masa
Bai bashi damar yin hakan ba ya dakatar da shi da hannunsa
A hankali ya bude kofar
Ziro kafarsa da ya yi ne ya saka NAJEEBA daga hannayenta duka biyu ta dora saman kanta
Gaba daya ta ga wajen ya masu kadan idan tace zata gudu ta rantse ba inda zata je zai kamata
Ruwan nan masu sanyin gaske sannan babar butali ne ya yi tsaye daga jikin motar
Da hannunsa ya yafito ta
Kafafuwanta ta shiga dokawa a hankali tana jin uwa ta ce na ki, sai dai gannin daga ita sai shi fa sai mai shigar masa taraya sai kawai ta ji kafafuwanta na kaita inda yake tsaye
Daga dan nesa ta ja ta tsaya ta sada kanta
Kansa ya kara gyadawa gannun bata zube ta ringa yi masa fadanci ba
Rabonsa da ya ga mutun ya yi tsaye haka kansa da kansa ba tare da ya bashi izinin hakan ba tun barin garin sarkin agadez , sai Anmy wace take mahaifiyarsa
Ko matarsa takan zube ne kafin ta nemi wani lamarin a wajensa
Yatsarsa baba da ta tsakiya ya hada ya dan bada wani sautin da ya sakata dagowa
Kudaden daje zube a kasa ya nuna mata da idannuwansa
Itama kudaden ta bi da kallo domin wutar motar a kunne take
Da sauri ta karasa ta duka tana tsintsincewa
Sai da ta gama dauke dukan wa'inda take ganni ta harhada su ta karaso kusa da shi wannan karron ta miko masa su
Hannayen nata da kudin duka ya bi da kallo,
Wa shi? Take mikowa kudi haka?
Sai abin ya so bashi daria a kasan zuciyarsa
Idab ya fahimta yarinyar banda rashin kunya harda rashin hankali ke damunta
Yau gashi da rigar sarautarsa a tsaye a gaban yar yarinyar nan marar kunya tana miko masa kudi hannu da hannu a tsaye kikam
Baban goran ruwan nan ya saka hannunsa ya bale cikin dakiya ya mika mata muryarsa a kausashe ya ce" *ki tsaftace najasar dake tare da ke*
Najasa? Ta tambayi kanta, ko fitsarin da na yi? Ta kuma tambayar kanta
Amsar gioran ruwan ta yi ta matsa gefe kadan ta duka ba abinda ya dadata da kasa domin ita ai ganni take dare ne yayama aka yi ya gane fitsari na yi? Take tambayar kanta
Ruwan sanyi ne da shi, gata bata saba anfani da ruwa masu sanyi ba sai dai ita kanta yanda take jin jikinta na yi mata kaikayi dole ta yi anfani da ruwan tana kara matse hikinta ta mike tana ajiyar zuciya
Ruwan ta riko ta juyo sai dai ganshi a tsaye a wajen da yake
Dan bakinta ta tabe a ranta tana ayanna wato bayan cin haram ko dai kwarto ne? Yo wannan saka ido har ina?
Karasowa ta yi kanta a sade a kasa dan nesa da shi kadan
Gannin bata yi abinda ya yi jiyar sai ta yi a yau a waje a bakin titi ba ya saka shi juyawa kusa da tagar amintacensa
Murya a kausashe ya ce" bani biyu
Dauko masa biyun ya yi masu sanyin balaki ya miko masa
Amsa ya yi wannan karron ya ringa takawa cike da kasaita da isa har ya karasa inda take tsayen
Buda goran ruwan ya yi cikin dakiyar fuska ya ce" ki dauri niyar yin wankan janaba a zuciyarki
Da sauri ta dago kanta da wani irin tsoro da mamakin jin abinda ya fada
Sai dai kafin ta gama fahimta tuni ya shiga tsiyaya mata wannan ruwa mai sanyin balaki tun daga saman kanta mai dauke da alkyaba da hijab a kasa ruwan na ratsata har cikin jikinta ga yannayi na sanyi ga kuma tana da cutar huka wato athsma
Gaba daya ta rikice jin saukar ruwan nan hakan ya sakata kwala kara tana furta" ANMY
kafarta ta daga da niyar kwatar kanta sai dai abin ya gagara dan wata damka da ya yiwa hannun nata da hannunsa daya ya kuma bale dayan da hakorinsa shima ya daga tun daga kan nata ya shiga bulbule mata shi
Da karfin gaske ta fincike Alkyabar dake saman kanta da dayan hannunta, ido rufe ta yi cikinsa ta rukunkumeshi gaba daya jikinta na rawa tana jin numfashinta na neman fara bugawa
Bakinta ta buda zata bashi hakuri sai dai ta gaza sakamakon jan shedarta da ta fara har numfashin ya fara wani kara sama sama yana hiiiiiiiiik, hiiiiik tamkar wace ta zo fitar rai
Sarai ya san cutarta kuma ya san ta tashi ne aman bai daina ba sai da ya gama bulbule mata yana son bambareta da jikinsa aman ta mane masa tamkar cingan
Yana gamawa ya saka hannunsa ya dago fuskarta
Muryarsa a kausashe yana yi mata duba irin na tsana ya ce" me ya sa kika zabi zubar da mutuncinki? Idan na iyayenki bai dameki ba naki fa? Ke kin kasance sakarya a cikin mata
Ban taba jin kyamar halita irin yanda nake kyamar halayanki ba, na tsani na ji a cikin kanena akoy ki! Ki sani tsakanina da ke ba alfarma ko tausayawa!
Magana ta karshe da zan maki bayan ta idannuwana da nake maki kan ki kiyayi hada hanya da ni, sarkinki nake ba tsaranki ba! Idan ke takamarki *Mage ce* ni kuwa *kaifin wuka ne NAJEEBA MUTALAB!*
gaba daya ta idasa sikewa ta tafi luuuuu ta fada a jikinsa sumamiya
Baya tare da wani damuwa ko firgicin gannin ta summe masa
Hasalima idasa rikota ya yi ya turata motar sannan ya shiga gidan gaba domin ko suturar jikinsa kyamatarta yake bare zama kusa da ita a karo na biyu bayan ta gama wannan wulakancin
Amintacensa kansa a kasa, magangannun sarki tas a kunnayensa sai dai bai san wanka ne ya mata da kayanta a saman titi ba
A hankali ya tashi motar zai nufi cikin gida, muryarsa a cinkushe ya ce" Degza da allura
Yana gama fada ya maida dubansa bakin titin yana mai bale agogon hannunsa
A nan ya yarda agogon , ya kuma bale botiran rigarsa daga ciki
Da gudu ya shiga pharmacy ya amso maganin da allurar
Yana kawo masa ya duka ya mika masa sannan ya juya ya shiga wajen direban
Ruwan Allurar ya fashe kanta ya tsira tsinnin allurar ya zuki ruwan ya saka kwalbar cikin ledar
Sunna karasawa cikin gida hanyar sirrinsa ya fito da kansa cikin takamarsa ya buda bangaren da take
Hijab din nata ya kama ya cire dan samun wajen da zai mata allurar
Rigar dake kasa ta atamfa ce mai damamen hannu
Jikinsa ya laluba ya ciro wata yar siririyar wuka mai kaifin balaki ya kama rigar ya yaga wajen hannun
Allurar nan ya caka ya tsira mata ba tare da ya bi ka'idar a hankali ba domin zafin tsiya ne da ita
Yana gama tsira mata ya dauki ruwa ya dan warwatsa mata
A zabure ta farka daga summar wahalar da ta yi, idannuwanta ne suka sauka a kan macijin da ya cire masa dafinsa suka zuki abubuwan bukata a jikinsa hakan ya sa ya kasa motsawa sai ya ki mayar da shi cikin kwalbar dan bashi da niyar kashe shi, zai mayar da shi wajensa ne
Gefen fuskarta na gogar jikinsa hakan ya sa ta sauke ajiyar zuciya ta koma duniyar summa daga kwoncen da take
Tsaki ya ja a cikin zuciyarsa gannin summan fa ta kuma yi
Karasa sauka ta yi tana yiwa mai babur ihun" ka yiwa Allah ka yi tafiyarka na ce ka bani cenji ne?
Sai hajia ya fada yana sara mata sannan ya tayar ya juya abinsa
Ja ta yi ta tsaya a wajen da take ta kasa karasawa wajen motar bale har ta shiga
Gaba daya ta gama yankewa kanta hukuncin idan dazu Allah ya kubutar da ita yanzun fa?
Zabura ta yi a lokacin da ta ga yana.........
More cmnt mr pag😌
[1/28, 10:58 PM] Ummu Sadeeq: 🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
20
Zabura ta yi a lokacin da ta ga ana sauke madubin bayan wanda ta tabata a nan yake zaune
Sosai aka zuge shi sannan ya sauke dubansa kakausan duban nan mai abin tsoro a kanta
Fitsarine ta ji zai zubo mata daga mararta
Da sauri ta juya ta matsa sosai tana dan rawar nan dan ta rike shi kar ya zubo
Haska wajen ta yi ta yi bismillah ta janye wandonta kasa kadan ta duka ta shiga fitsarin nan domin idan bata yi shi ta tabata zata yi shi a motar cen
Kansa ya yi saurin kawarwa daga wajenta, amintacensa kuwa dama kansa a sade yake yana cike da mamakin lalle yarinyar nan ta isa
Su suke tare da sarki SHAHEEd , wato gurnanin zaki
Su suka san waye Sarki SHAHEED
Yaya aka yi ta taka doka haka har haka?
Sai da ta kusan karasa fitsarin ta tuna bata da ruwan kama ruwa
Gaba daya ta ji jikinta ya kwashi wani yamyamyam na kyamar kazanta
Bata wasa da tsaftar wajen nan ko da wasa gashi yau ta yi fitsari a wajen nan sannan a gaban sarki gashi babu ruwa
Sai da ta gama sosai ta cire wandonta dan ba zara iya mayar da shi ba ta mike a hankali jikinta na ci gaba da rawa
Tana tunkaro motar ya kuma dagowa yana yi mata duba irin na mamakin fitsarine ta yi d agaske haka gabansu ? Lalee ta cika rashin kamun kai da rainin hankali
Kara datse lebensa ya yi na kasa yana gannin lokacin da ta karasa isowa ta ja ta tsaya daga nesa gaba daya jikinta na rawa hankalinta a matukar tashe baki daya wani kuzarinta ya bace sai tarin tsoron dake cin ranta
Dubansa ya cire daga kanta ya kalli wajen amintacensa
Sai da ya dauki mintunna kafin ya ce" bani faro
Da sauri ya buda wajen da ake saka ruwan ya dauko ya juyo gaba dayansa ya dan risina ya mikowa sarki
SHAHEED ya mika hannunsa na dama ya amsa yana rike da ruwan
Cen ya saka hannunsa zai bude hakan ya sa amintacensa saurin kokarin budewa dan ya bude masa
Bai bashi damar yin hakan ba ya dakatar da shi da hannunsa
A hankali ya bude kofar
Ziro kafarsa da ya yi ne ya saka NAJEEBA daga hannayenta duka biyu ta dora saman kanta
Gaba daya ta ga wajen ya masu kadan idan tace zata gudu ta rantse ba inda zata je zai kamata
Ruwan nan masu sanyin gaske sannan babar butali ne ya yi tsaye daga jikin motar
Da hannunsa ya yafito ta
Kafafuwanta ta shiga dokawa a hankali tana jin uwa ta ce na ki, sai dai gannin daga ita sai shi fa sai mai shigar masa taraya sai kawai ta ji kafafuwanta na kaita inda yake tsaye
Daga dan nesa ta ja ta tsaya ta sada kanta
Kansa ya kara gyadawa gannun bata zube ta ringa yi masa fadanci ba
Rabonsa da ya ga mutun ya yi tsaye haka kansa da kansa ba tare da ya bashi izinin hakan ba tun barin garin sarkin agadez , sai Anmy wace take mahaifiyarsa
Ko matarsa takan zube ne kafin ta nemi wani lamarin a wajensa
Yatsarsa baba da ta tsakiya ya hada ya dan bada wani sautin da ya sakata dagowa
Kudaden daje zube a kasa ya nuna mata da idannuwansa
Itama kudaden ta bi da kallo domin wutar motar a kunne take
Da sauri ta karasa ta duka tana tsintsincewa
Sai da ta gama dauke dukan wa'inda take ganni ta harhada su ta karaso kusa da shi wannan karron ta miko masa su
Hannayen nata da kudin duka ya bi da kallo,
Wa shi? Take mikowa kudi haka?
Sai abin ya so bashi daria a kasan zuciyarsa
Idab ya fahimta yarinyar banda rashin kunya harda rashin hankali ke damunta
Yau gashi da rigar sarautarsa a tsaye a gaban yar yarinyar nan marar kunya tana miko masa kudi hannu da hannu a tsaye kikam
Baban goran ruwan nan ya saka hannunsa ya bale cikin dakiya ya mika mata muryarsa a kausashe ya ce" *ki tsaftace najasar dake tare da ke*
Najasa? Ta tambayi kanta, ko fitsarin da na yi? Ta kuma tambayar kanta
Amsar gioran ruwan ta yi ta matsa gefe kadan ta duka ba abinda ya dadata da kasa domin ita ai ganni take dare ne yayama aka yi ya gane fitsari na yi? Take tambayar kanta
Ruwan sanyi ne da shi, gata bata saba anfani da ruwa masu sanyi ba sai dai ita kanta yanda take jin jikinta na yi mata kaikayi dole ta yi anfani da ruwan tana kara matse hikinta ta mike tana ajiyar zuciya
Ruwan ta riko ta juyo sai dai ganshi a tsaye a wajen da yake
Dan bakinta ta tabe a ranta tana ayanna wato bayan cin haram ko dai kwarto ne? Yo wannan saka ido har ina?
Karasowa ta yi kanta a sade a kasa dan nesa da shi kadan
Gannin bata yi abinda ya yi jiyar sai ta yi a yau a waje a bakin titi ba ya saka shi juyawa kusa da tagar amintacensa
Murya a kausashe ya ce" bani biyu
Dauko masa biyun ya yi masu sanyin balaki ya miko masa
Amsa ya yi wannan karron ya ringa takawa cike da kasaita da isa har ya karasa inda take tsayen
Buda goran ruwan ya yi cikin dakiyar fuska ya ce" ki dauri niyar yin wankan janaba a zuciyarki
Da sauri ta dago kanta da wani irin tsoro da mamakin jin abinda ya fada
Sai dai kafin ta gama fahimta tuni ya shiga tsiyaya mata wannan ruwa mai sanyin balaki tun daga saman kanta mai dauke da alkyaba da hijab a kasa ruwan na ratsata har cikin jikinta ga yannayi na sanyi ga kuma tana da cutar huka wato athsma
Gaba daya ta rikice jin saukar ruwan nan hakan ya sakata kwala kara tana furta" ANMY
kafarta ta daga da niyar kwatar kanta sai dai abin ya gagara dan wata damka da ya yiwa hannun nata da hannunsa daya ya kuma bale dayan da hakorinsa shima ya daga tun daga kan nata ya shiga bulbule mata shi
Da karfin gaske ta fincike Alkyabar dake saman kanta da dayan hannunta, ido rufe ta yi cikinsa ta rukunkumeshi gaba daya jikinta na rawa tana jin numfashinta na neman fara bugawa
Bakinta ta buda zata bashi hakuri sai dai ta gaza sakamakon jan shedarta da ta fara har numfashin ya fara wani kara sama sama yana hiiiiiiiiik, hiiiiik tamkar wace ta zo fitar rai
Sarai ya san cutarta kuma ya san ta tashi ne aman bai daina ba sai da ya gama bulbule mata yana son bambareta da jikinsa aman ta mane masa tamkar cingan
Yana gamawa ya saka hannunsa ya dago fuskarta
Muryarsa a kausashe yana yi mata duba irin na tsana ya ce" me ya sa kika zabi zubar da mutuncinki? Idan na iyayenki bai dameki ba naki fa? Ke kin kasance sakarya a cikin mata
Ban taba jin kyamar halita irin yanda nake kyamar halayanki ba, na tsani na ji a cikin kanena akoy ki! Ki sani tsakanina da ke ba alfarma ko tausayawa!
Magana ta karshe da zan maki bayan ta idannuwana da nake maki kan ki kiyayi hada hanya da ni, sarkinki nake ba tsaranki ba! Idan ke takamarki *Mage ce* ni kuwa *kaifin wuka ne NAJEEBA MUTALAB!*
gaba daya ta idasa sikewa ta tafi luuuuu ta fada a jikinsa sumamiya
Baya tare da wani damuwa ko firgicin gannin ta summe masa
Hasalima idasa rikota ya yi ya turata motar sannan ya shiga gidan gaba domin ko suturar jikinsa kyamatarta yake bare zama kusa da ita a karo na biyu bayan ta gama wannan wulakancin
Amintacensa kansa a kasa, magangannun sarki tas a kunnayensa sai dai bai san wanka ne ya mata da kayanta a saman titi ba
A hankali ya tashi motar zai nufi cikin gida, muryarsa a cinkushe ya ce" Degza da allura
Yana gama fada ya maida dubansa bakin titin yana mai bale agogon hannunsa
A nan ya yarda agogon , ya kuma bale botiran rigarsa daga ciki
Da gudu ya shiga pharmacy ya amso maganin da allurar
Yana kawo masa ya duka ya mika masa sannan ya juya ya shiga wajen direban
Ruwan Allurar ya fashe kanta ya tsira tsinnin allurar ya zuki ruwan ya saka kwalbar cikin ledar
Sunna karasawa cikin gida hanyar sirrinsa ya fito da kansa cikin takamarsa ya buda bangaren da take
Hijab din nata ya kama ya cire dan samun wajen da zai mata allurar
Rigar dake kasa ta atamfa ce mai damamen hannu
Jikinsa ya laluba ya ciro wata yar siririyar wuka mai kaifin balaki ya kama rigar ya yaga wajen hannun
Allurar nan ya caka ya tsira mata ba tare da ya bi ka'idar a hankali ba domin zafin tsiya ne da ita
Yana gama tsira mata ya dauki ruwa ya dan warwatsa mata
A zabure ta farka daga summar wahalar da ta yi, idannuwanta ne suka sauka a kan macijin da ya cire masa dafinsa suka zuki abubuwan bukata a jikinsa hakan ya sa ya kasa motsawa sai ya ki mayar da shi cikin kwalbar dan bashi da niyar kashe shi, zai mayar da shi wajensa ne
Gefen fuskarta na gogar jikinsa hakan ya sa ta sauke ajiyar zuciya ta koma duniyar summa daga kwoncen da take
Tsaki ya ja a cikin zuciyarsa gannin summan fa ta kuma yi