Sashe 14
Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Abih ne ya dan gyara zamansa shima a nitse ya ce" Allah ya huci zuciyar adalin sarki
DAYABUma ya kara sada kansa cike da girmama sarkin ya furta" a yiwa zinaria afuwa mai martaba
Anmy ta ringa zungurin su NAJEEBA,
Najeeba ta saki murmushi ta ki yin magana, a hankali ZAHRAU ta sada kanta ta ce" Allah ya huci zuciyar sarkin abzin
Haka su Ummu suka ringa furtawa a hankali aman cikin ikon Allah NAJEEBA sai ta sada kanta kawai tana murmushi a saman lebenta wanda bata boye ba
Da yake basu da yawa a dakin dole a fahimci wanda ya yi magana da wanda bai yi ba, gashi maganar a nitse ake yinta ba da hayaniya ba, sannan ba a tare ake yin maganar ba idan daya ya yi sai ya ajiye harma ya saka sekwani sannan wani ya yi cike da biyaya
Da sauri ta zamo kasa ta dukar da kanta ta ce" Allah ya huci zuciyar Aba
SHAHEED ya kawar da dubansa daga kanta, ya maida wajen sarki, da idannuwansa ya risinar da idannuwan nasa sosai sannan ba rufe su ya yi ba haka kuma ana gannin samansu da gashin girarsa
Hannunsa na daman ya dan daga daga ajiyen da yake ya dan dunkule shi sannan ya kara sada kansa
Murmushi sarkin garin Agadez ya yi da kansa ya iya amsa masa shima kafin cike da farin cikin kasancewarsa sirikinsa sarkin da ko cikinsu sarakunna suna maganar irin yanda sarauta ta zauna masa a jinnin jikinsa
Dubansa ya kai wajen Zulaihat a hankali ya ce" na san da kin san cewa dukan mai rai mamaci ne, sannan kin san cewa mamaci baya son kuka
Ba za'a hana ki zubar da hawayen rasa gudan jinninki ba, aman kuma ba za'a barki ki zubar har zubarwa ta dawo ta zama ba kyau
Idan kika tuna shi, ki yi gagawar yi masa adu'a
Idan soyaya ce nuna masa ta hanyar adu'a
Sannan ke kanki ki shirya naki zuwan inda ya tafi
Kanta take gyadawa hakan ya sa NAJEEBA ta kara dagowa ta tsura mata ido
Sai yau ta ji tausayinta, gaskiya ta ji tausayinta har cikin ranta
Kwana ukun nan koke koken da suke a bangaren Anmy sai ta dauke shi kawai na a ringa basu hakuri ne a hadu a lalace, tabas mutuwar Aliyu ta daketa domin yaron ba wanda ya batawa, yaro be mai shiru shiru sosai sai idan kun hada ido yakan sakar maka murmushi
To baima yi maganar ba bale ka ce ya maka ba daidai ba
Sannan koda yaushe yana wajen mahaifinsa sunna zaman fada, bai cika zama a gida ba dan mamansa bata barinsa zama a gida kulun korarsa take ya je ya koyi irin yanda ake juya kujerar da wata rana zai mulka
Idannuwanta ta lumshe ta maida kanta ta sada har ya gama sannan du suka shiga fadin godiya take da dai sauransu
NAJEEBA kuwa abinda ya fi bata daria kennan, irin yanda sha'anin sarauta yake tafia, irin yanda sarki ke zaune magana na masa wahala aman wasu na ta faman Allah ya huci zuciyarsa
To waima me aka masa da za'a ringa neman afuwar mutun? Anmy kadai take iya yiwa wannan kazagin itama sai idan ta tabata cewa ta bata mata to fa takan yi gagawar zubewa kasa ta ringa Allah ya huci zuciyar Gimbiya
Sai da komai ya nitsa Sarki ya nemi da yaran su fita
Du mimikewa suka yi, Zinaria ta fara godiya sannan ta juya ta fita
Su Ummu da zahra dukansu sai da suka yi godiya sannan suka firfito aman NAJEEBA kanta kawai ke kasa a hankali kuma cikin tafiarta wace ake gannin yanga ce ko takama da isa ce bayan haka take tun kankannuwarta bata iya sauri ba a haka ta fita a falon
Kansa kawai ya girgiza......bata nemi afuwar sarki ba, bata yi godiya ba, sannan da zata fita bata gode ba
DAYABU kansa duka abubuwan nan yana hankalce da ita harma ya gama ganewa NAJEEBAR so take ta jaza masu baki daya tashin hankalin Mai Martaba wanda hakan ba zai masu da sauki ba
Sunna tsakiyar tafia NAJEEBA ta ja ta tsaya, sai kawai ta shiga daria tana girgiza kanta
UMMU ta harareta ta yi tsaki ta ce" ke dai, ke dai akoy fitinaniya, wai ke mai martaba sa'ankine da zaki ringa kokarin kawo raini kai tsaye tsakaninku? Kin ga sarai dai yaya ya girme shi aman yake masa biyaya, kin ga Anmy mahaifiyarsa ce aman kasancewarsa sarki idan tana gabansa a lokacin da yake saman mulkinsa takan sanyaya kalamanta sannan ta tafiar da lokacin cikin sada kai
NAJEEBA kina ji kowa na rokar afuwa ke ba zaki yi ba ko?
Ummulkhair ta ce" kin ga, ni kaina dan Anmy ta min wani mintsini ne ya saka ni magana, haba dan Allah matar nan ta Mai martaba bata da mutunta mutane, kunna fa ji ranar nan yanda ta zagi Najeebar
ZAHRAU ta ce" ku dai ku daina irin haka, ina anfanin masifa wai?
NAJEEBA ta ce" ku dakata ni du ba wannan ba so nake ki auri ubanta
Zahrau ta zabura, dan har ga Allah gabanta ne ya fadi jin abinda NAJEEBA ta fada
Ummulkhair dake tare mata ta girgiza kai ta ce" zuwa yanzu na yarda baki da hankali NAJEEBA
Gaba suka fara yi hakan ya sakata itama daga kafarta tana biye da su bayan ta turo bakinta
Sai da suka shige uwar dakan ANMY NAJEEBA ta fada saman bed da baya tana murmushi
Juyawa ta yi tana kallon ZAHRAU ta ce" aunty, yaushe rabonki da ki ga fuskarsa?
Zahrau ta waigota ta ce" wa fa?
Najeeba ta ce" shi SHAHEED din
Da sauri ZAHRAU ta zaro ido, Bilkissu kuwa ta tura kofar da sauri ta rufe wace shigowarta kennan itama da mamaji ta ce" aunty NAJEEBA sunnansa ne kika kama kai tsaye haka?
NAJEEBA ta dubeta ta tabe baki bata bata amsa ba
UMMUKULSUM dake cire mayafinta ta dubi Bilkissu ta ce" ke fice mana a nan muna tataunawa yara sai shiga maganar manya
UMMULKHAIR kuwa itama bakin gadon ta karasa ta zauna tana fadin" walahi aunty ko, nima inaga a yanzu ba zan iya nuna kalarsa ba dan rabona da shi fuskarsa a waje tun kafin a nada shi sarauta
NAJEEBA ta ce" sai dai a yi masa hoto a boye a fitar da shi bayan mun san hotuna yanzu ana iya kara masa haske ko a kara masa girma bayan yaro ne karami
Da sauri Zahrau ta kai hannunta ta buge bakinta ta ce" ke dai neman fitinarki zai saka watarana a yanka maki bakin nan naki gutsi gutsi, ni ba zan manta lokacin da suke hawa dawakai da yaya ba, a lokacinma ya girmi yaya a girman jiki sosai har yaya na nemansa da rigima yana ce masa an hura shi shi din kyankyasar inji ne, shi kuwa yakan ce da yaya shi kuwa dan tamowa ne
Sannanma ina ruwanmu ne muna cikin gidansu muna irin magangannun nan idan ya ji kun san da zai iya sakawa a dauke mu ya halaka mu shikenan ko?
NAJEEBA ta koma ta kwonta tana kada kafarta ta ce" ina tausayawa talakawansa ne, kin ga ya ci ya cinye ya tayar da kai
Turaran nan da yake anfani da shi sai da ya cinye min tanadina na shekara biyu a paris bayan kun san nima mai kudi ce
Ta karashe tana kanne ido daya ta ci gaba da fadin" ku duba ku ga irin yanda fallonsa yake, Ac ban san adadin ko nawa bane, labulayen da karafunnan labulayen dakin nan sai ka rantse ba a africa bane,
Cafet din falon, da kujerun falon kadai ya isa ya haukata wanda bai taba fita ba
Duba ki ga irin dankara dankaran TV da windows da maficin nan dake kyali wanda aka ce da ruwan zinari ake wanke shi
Kausasa dubanta ta yi ta ce" ku kun san me nake nufi da ruwan zinari dan irin tsadar da wankin sarka yake a kasar nan!
Zobunnan hannunsa, da agogon hannunsa da takalmin kafarsa da shadar jikinsa da zubin da ake yiwa suturunsa kan sakani tunanin anya y'ayan mutane dake bata ba mafiya mai garin garin yake ba?
Zuwa lokacin Ummulkhair mayafinta ta dauka ta ce" kun ga, ba'ai min aure ba bale na haihu na haifi mai min adu'a, haka kawai na zauna a je wani tsanwan kuda ya kai labarin nan kunnayen fadawansama ba shi ba walahi sai sun ci ubanmu ko kannensa muke ba cousins dinsa ba
Tsakaninki da Allah NAJEEBA mutumen da ake yiwa maganar adalci wanda mutane suka shaida ake yabonsa ke jarababiya har kika iya kurewa rayuwarsa kallo kina neman masa shari?
NAJEEBA ta mike zaune tana kallon Ummulkhair ta ce" Ummu, wata uku fa kika bani a duniya kin ga yaya baya nan idan kika kuma zagina Allah sai na mare ki! Kuma ai ba shari na masa ba gaskiya na fada da yake hararena yana min kallon tsana me na masa yo ni bayan shi da kudaden talakawa yake takama? Ni kuwa neman na kaina nake walahi!
DAYABUma ya kara sada kansa cike da girmama sarkin ya furta" a yiwa zinaria afuwa mai martaba
Anmy ta ringa zungurin su NAJEEBA,
Najeeba ta saki murmushi ta ki yin magana, a hankali ZAHRAU ta sada kanta ta ce" Allah ya huci zuciyar sarkin abzin
Haka su Ummu suka ringa furtawa a hankali aman cikin ikon Allah NAJEEBA sai ta sada kanta kawai tana murmushi a saman lebenta wanda bata boye ba
Da yake basu da yawa a dakin dole a fahimci wanda ya yi magana da wanda bai yi ba, gashi maganar a nitse ake yinta ba da hayaniya ba, sannan ba a tare ake yin maganar ba idan daya ya yi sai ya ajiye harma ya saka sekwani sannan wani ya yi cike da biyaya
Da sauri ta zamo kasa ta dukar da kanta ta ce" Allah ya huci zuciyar Aba
SHAHEED ya kawar da dubansa daga kanta, ya maida wajen sarki, da idannuwansa ya risinar da idannuwan nasa sosai sannan ba rufe su ya yi ba haka kuma ana gannin samansu da gashin girarsa
Hannunsa na daman ya dan daga daga ajiyen da yake ya dan dunkule shi sannan ya kara sada kansa
Murmushi sarkin garin Agadez ya yi da kansa ya iya amsa masa shima kafin cike da farin cikin kasancewarsa sirikinsa sarkin da ko cikinsu sarakunna suna maganar irin yanda sarauta ta zauna masa a jinnin jikinsa
Dubansa ya kai wajen Zulaihat a hankali ya ce" na san da kin san cewa dukan mai rai mamaci ne, sannan kin san cewa mamaci baya son kuka
Ba za'a hana ki zubar da hawayen rasa gudan jinninki ba, aman kuma ba za'a barki ki zubar har zubarwa ta dawo ta zama ba kyau
Idan kika tuna shi, ki yi gagawar yi masa adu'a
Idan soyaya ce nuna masa ta hanyar adu'a
Sannan ke kanki ki shirya naki zuwan inda ya tafi
Kanta take gyadawa hakan ya sa NAJEEBA ta kara dagowa ta tsura mata ido
Sai yau ta ji tausayinta, gaskiya ta ji tausayinta har cikin ranta
Kwana ukun nan koke koken da suke a bangaren Anmy sai ta dauke shi kawai na a ringa basu hakuri ne a hadu a lalace, tabas mutuwar Aliyu ta daketa domin yaron ba wanda ya batawa, yaro be mai shiru shiru sosai sai idan kun hada ido yakan sakar maka murmushi
To baima yi maganar ba bale ka ce ya maka ba daidai ba
Sannan koda yaushe yana wajen mahaifinsa sunna zaman fada, bai cika zama a gida ba dan mamansa bata barinsa zama a gida kulun korarsa take ya je ya koyi irin yanda ake juya kujerar da wata rana zai mulka
Idannuwanta ta lumshe ta maida kanta ta sada har ya gama sannan du suka shiga fadin godiya take da dai sauransu
NAJEEBA kuwa abinda ya fi bata daria kennan, irin yanda sha'anin sarauta yake tafia, irin yanda sarki ke zaune magana na masa wahala aman wasu na ta faman Allah ya huci zuciyarsa
To waima me aka masa da za'a ringa neman afuwar mutun? Anmy kadai take iya yiwa wannan kazagin itama sai idan ta tabata cewa ta bata mata to fa takan yi gagawar zubewa kasa ta ringa Allah ya huci zuciyar Gimbiya
Sai da komai ya nitsa Sarki ya nemi da yaran su fita
Du mimikewa suka yi, Zinaria ta fara godiya sannan ta juya ta fita
Su Ummu da zahra dukansu sai da suka yi godiya sannan suka firfito aman NAJEEBA kanta kawai ke kasa a hankali kuma cikin tafiarta wace ake gannin yanga ce ko takama da isa ce bayan haka take tun kankannuwarta bata iya sauri ba a haka ta fita a falon
Kansa kawai ya girgiza......bata nemi afuwar sarki ba, bata yi godiya ba, sannan da zata fita bata gode ba
DAYABU kansa duka abubuwan nan yana hankalce da ita harma ya gama ganewa NAJEEBAR so take ta jaza masu baki daya tashin hankalin Mai Martaba wanda hakan ba zai masu da sauki ba
Sunna tsakiyar tafia NAJEEBA ta ja ta tsaya, sai kawai ta shiga daria tana girgiza kanta
UMMU ta harareta ta yi tsaki ta ce" ke dai, ke dai akoy fitinaniya, wai ke mai martaba sa'ankine da zaki ringa kokarin kawo raini kai tsaye tsakaninku? Kin ga sarai dai yaya ya girme shi aman yake masa biyaya, kin ga Anmy mahaifiyarsa ce aman kasancewarsa sarki idan tana gabansa a lokacin da yake saman mulkinsa takan sanyaya kalamanta sannan ta tafiar da lokacin cikin sada kai
NAJEEBA kina ji kowa na rokar afuwa ke ba zaki yi ba ko?
Ummulkhair ta ce" kin ga, ni kaina dan Anmy ta min wani mintsini ne ya saka ni magana, haba dan Allah matar nan ta Mai martaba bata da mutunta mutane, kunna fa ji ranar nan yanda ta zagi Najeebar
ZAHRAU ta ce" ku dai ku daina irin haka, ina anfanin masifa wai?
NAJEEBA ta ce" ku dakata ni du ba wannan ba so nake ki auri ubanta
Zahrau ta zabura, dan har ga Allah gabanta ne ya fadi jin abinda NAJEEBA ta fada
Ummulkhair dake tare mata ta girgiza kai ta ce" zuwa yanzu na yarda baki da hankali NAJEEBA
Gaba suka fara yi hakan ya sakata itama daga kafarta tana biye da su bayan ta turo bakinta
Sai da suka shige uwar dakan ANMY NAJEEBA ta fada saman bed da baya tana murmushi
Juyawa ta yi tana kallon ZAHRAU ta ce" aunty, yaushe rabonki da ki ga fuskarsa?
Zahrau ta waigota ta ce" wa fa?
Najeeba ta ce" shi SHAHEED din
Da sauri ZAHRAU ta zaro ido, Bilkissu kuwa ta tura kofar da sauri ta rufe wace shigowarta kennan itama da mamaji ta ce" aunty NAJEEBA sunnansa ne kika kama kai tsaye haka?
NAJEEBA ta dubeta ta tabe baki bata bata amsa ba
UMMUKULSUM dake cire mayafinta ta dubi Bilkissu ta ce" ke fice mana a nan muna tataunawa yara sai shiga maganar manya
UMMULKHAIR kuwa itama bakin gadon ta karasa ta zauna tana fadin" walahi aunty ko, nima inaga a yanzu ba zan iya nuna kalarsa ba dan rabona da shi fuskarsa a waje tun kafin a nada shi sarauta
NAJEEBA ta ce" sai dai a yi masa hoto a boye a fitar da shi bayan mun san hotuna yanzu ana iya kara masa haske ko a kara masa girma bayan yaro ne karami
Da sauri Zahrau ta kai hannunta ta buge bakinta ta ce" ke dai neman fitinarki zai saka watarana a yanka maki bakin nan naki gutsi gutsi, ni ba zan manta lokacin da suke hawa dawakai da yaya ba, a lokacinma ya girmi yaya a girman jiki sosai har yaya na nemansa da rigima yana ce masa an hura shi shi din kyankyasar inji ne, shi kuwa yakan ce da yaya shi kuwa dan tamowa ne
Sannanma ina ruwanmu ne muna cikin gidansu muna irin magangannun nan idan ya ji kun san da zai iya sakawa a dauke mu ya halaka mu shikenan ko?
NAJEEBA ta koma ta kwonta tana kada kafarta ta ce" ina tausayawa talakawansa ne, kin ga ya ci ya cinye ya tayar da kai
Turaran nan da yake anfani da shi sai da ya cinye min tanadina na shekara biyu a paris bayan kun san nima mai kudi ce
Ta karashe tana kanne ido daya ta ci gaba da fadin" ku duba ku ga irin yanda fallonsa yake, Ac ban san adadin ko nawa bane, labulayen da karafunnan labulayen dakin nan sai ka rantse ba a africa bane,
Cafet din falon, da kujerun falon kadai ya isa ya haukata wanda bai taba fita ba
Duba ki ga irin dankara dankaran TV da windows da maficin nan dake kyali wanda aka ce da ruwan zinari ake wanke shi
Kausasa dubanta ta yi ta ce" ku kun san me nake nufi da ruwan zinari dan irin tsadar da wankin sarka yake a kasar nan!
Zobunnan hannunsa, da agogon hannunsa da takalmin kafarsa da shadar jikinsa da zubin da ake yiwa suturunsa kan sakani tunanin anya y'ayan mutane dake bata ba mafiya mai garin garin yake ba?
Zuwa lokacin Ummulkhair mayafinta ta dauka ta ce" kun ga, ba'ai min aure ba bale na haihu na haifi mai min adu'a, haka kawai na zauna a je wani tsanwan kuda ya kai labarin nan kunnayen fadawansama ba shi ba walahi sai sun ci ubanmu ko kannensa muke ba cousins dinsa ba
Tsakaninki da Allah NAJEEBA mutumen da ake yiwa maganar adalci wanda mutane suka shaida ake yabonsa ke jarababiya har kika iya kurewa rayuwarsa kallo kina neman masa shari?
NAJEEBA ta mike zaune tana kallon Ummulkhair ta ce" Ummu, wata uku fa kika bani a duniya kin ga yaya baya nan idan kika kuma zagina Allah sai na mare ki! Kuma ai ba shari na masa ba gaskiya na fada da yake hararena yana min kallon tsana me na masa yo ni bayan shi da kudaden talakawa yake takama? Ni kuwa neman na kaina nake walahi!