Sashe 57
Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya fad'a mata maganar nan ne dan kar ta ji a gari ta tuhume shi da b'oye mata babbar magana irin wannan, kawai daga jin labarin an d'aura auren Zahrau fitintunnu suka tashi kamar zata kama da wuta, saima da ta ji wanda ya aureta nan fa hankalinta ya k'ara tashi idanuwanta suka rufe ta ko wace hanya neman abinda zata lalata lamarin take, shine ta ringa tak'ale tak'ale ganin dai b'angaren Zahrau yarinya ce mai matuk'ar biyayya da matsanancin kamun kai, hakama mahaifiyarta sai kawai ta shiga yada masa magana cewar yanzu da sarkin ya ji ya aikata haka yaya za'a yi ya so had'a zuri'a da shi? Shine fa shima ya ce da ita "In banda abinki Mardiya ni kuwa na had'a da ke?" (Wato idan baki ya san abinda zai fad'a bai san amsar da za'a bashi ba) shine fa ta ringa fad'e fad'en maganar da idanuwansa suka rufe ya wan wanka mata mari domin fadi take" yanzu haka ba ita kad'ai bace shegiyar har sauran duba da irin yanda suke da halayya na shegu." Kamar wani wanda shege yake da halayya tasa daban, hakan ne ya saka Abih hankad'ata yana nunata da yatsa ya ce ta daina sheganta masa y'aya.
Sai aka yi rashin sa'a ta kaiwa madubi duka, dama abinda zai kaita gidan sarki take nema sai kawai ta fad'a motarsa ta nufi gidan sarkin, tun da aka fito daga sallah ta tsaya a hanyarsa dogarai na kakarewa aman sai da ta yi yanda ya gane itace kafin ta fasa kuka ta yi hanyar b'angaren Anmy.
Burinta ta fasa wannan sirrin y'ayansa su san abinda ya aikata, ta wanzar da tashin hankali tsakaninsu da mahaifinsu da su kansu.
A hankali Anmy ke girgiza kanta kafin ta ringa furta "Innalilahi wa inna ilaihi raj'une."
Da sauri ta shiga tatara k'annanun da su suna cike da tsoron ganinsu zaune gaban mai martaba dan su tsoronsa ma suke, sai Nusaiba dake ta mak'alar wuyan DAYABU tana wasa.
Anmy du ta tattara su ta tura su ciki tana jin kamar juwa zata kifata da k'asa.
Shi Kansa sarki sai ya sada kansa k'asa yana jin yanda kansa ke sarawa, ayau yana tare da b'acin ran da wannan fitinaniyar ta haddasa masa, sai ga wani gagarumin da ya tabbata Anmynsa sai ta shiga matsanancin tashin hankali, uwa uba Abih.
Abih gaba d'aya jikinsa ne ya ji ya fara masa wata mijirya kafin ya d'ora hannunsa daidai zuciyarsa ya rintse idannuwansa wasu zafafan hawaye suka shiga biyowa gefen kumatunsa.
Anmy ta sada kanta sai kawai ta fashe da kuka tana girgiza kanta tana b'oye fuskarta dan kunyar da take ji da irin maganar Mardiya.
Baki d'ayansu hankalinsu ne ya k'ara tashi, hakan ya saka du suka rasa ina zasu nufa, wajen Anmy din ko wajen Abih?
Da rarafe wa'inda suka fi kusanci da Anmy suka yi kanta suka ruk'unk'umeta, wa'inda suka fi kusanci da Abih kuwa Ummukulsum ce da Dayabu suka yi wajensa da Nusaiba suka had'e a jikinsa.
Mamakin hakan ya saka Anmy d'agowa hannunta na rawa ta kai dubanta wajen SHAHEED ta ga kansa a sade, aman ya damk'i sandar dake kusa da k'afarsa da damk'a mai tsananin da ya hadasa jijiyoyin hannun nasa k'ara yin tsaye rad'o rad'o.
A rikice take tatab'a jikinsu ta shiga fadin" baku yi mana fushi ba? Wallahi zan fad'a maku yanda aka yi, kun san k'adarar bawa bata fice shi kar ku yiwa mahaifinku da ni kaina da na taya shi b'oye sirrin nan fushi."
DAYABU dake dafe da hannun Abih wanda ya dafe daidai zuciyarsa muryarsa na rawa rawa ya ce" ABIH, kar ka kashe kanka a irin wannan lokacin da matarka take son tona asirinka dan manufarta da mu kanmu bamu sani ba,
Abih mun san da maganar nan dan girman Allah ka sassauta kar ka had'iyi zuciya domin idan ka mutu mu mukai asara ba ita ba."
UMMUKULSUM ta ririk'e hannayensa tana dannawa ta ce" Abih zafi nan ke maka? Idan yana zafi mu je asibiti, Abih wallahi wallahi bama jin kunyar ubanmu ko haushinka domin a haka muke son ka."
NAJEEBA ta k'ara rik'e Anmy tana b'oye fuskarta a jikinta tace" Anmy, meye na kukan? Kanmu aka fara ko kanmu za'a rufe?Anmy, koda mu dukanmu ne shegun shine aka ce zamu zo mu shak'e maku wuyan a kan me hakan ta faru? Innalilahi wa'ina ilaihi raj'une, Anmy ba shege bane abin gudu, d'an halal d'in aman mai halayan shege!
Anmy, ai ba daga yannayin da aka haifeka kake nuna halaya ba, halayanka na nuna wanda ya baka tarbiya."
"Anmy, kowani tsuntsu kukan gidansu yake yi! Koda dubu ya tara mu ubanmu ne, babu wata hallitar da zata zagar mana shi bamu sauke hak'oranta k'asa ba na rantse!"
Ummulkhairma kukan take tana kara share hawayen Anmy ta buda bakinta ta ce" Anmy, ku daina kukan nan haka, kin ga fa Abih sai rike daidai zuciyarsa yake
Najeeba ta saketa tayi wajen Abih ita ma ta d'ora kanta gefen k'afarsa tana jin kamar ranta ne ake wasa da shi, irin yanda iyayen nata ke zubar da hawaye sai ta ji tsoron Allah ya k'ara shigarta,
wai kunyar duniya kennan, duniyar ma yayanka, ina ga kunyar Allah? (ALLAH, ALLAH, DAN GIRMANKA DAN SOYAYARKA DA FIYAYEN HALITA ALLAH KA SHIRYE MU, KA YAFE MANA, KA SA MU GAMA DA DUNIYA LAFIA, KA RUFA MANA ASIRI DUNIYA DA KIYAMA).
Anmy da Ummulkhair ma da rarafe suka k'arasa wajen Abih, Anmy ta d'ora hannunta inda hannunsa yake tana hawaye tace "Ya isa, daga yau nauyin sai ya tafi ya baka lafia, yaya sun ji, sun sani sun sani." Sai ta had'e kanta da su suma sunna ta hawaye, shi kuwa da hannunsa yake daddab'a su yana jin wani irin a cikin ransa.
SHAHEED kuwa abu d'aya ya hana shi tashi daga zaunen da yake shine shara'a, ya hau kujerar nan ne dan ya yi shara'a tsakaninsu
tana zaune ta kawo k'ara ne, du irin kukan da mahaifiyarsa ke yi tamkar ana narka dalma ne ana zuba masa a k'irjinsa.
Mardiya kuwa baki da hanci duka a bud'e suke ta yi wani fik'i fik'i tana ganin abin na neman juyewa a kanta.
Anmy dake kuka tayi saurin d'agowa, hannun Dayyabu ta damk'o sannan ta damk'o na yayanta tana hawayen nan ta ce "Insha Allahu ba zamu yi kunya ba, insha Allahu Allah zai yi ta rufa mana asiri."
A hankali ta kuma fad'in" *YAYA, DAYABU, SHIN ZAKU BAIWA MAI MARTABA AUREN Y'ATA?* *INA BARAR AUREN YARINYATA WA SARKIN DAMAGARAM, INA BARAR AUREN Y'ATA WA YARON KA*?" Ta karashe tana mai hade hannayenta da nuna Abih.
Tunda ta fara neman auren ya d'ago da rinanun idanuwansa ya tsura mata daga ita har yayan nata da kuma y'ayan nata, suma y'ayan mata biyu da suka yi saura sai ya zamana kukan nasu ya d'auke d'if sai kallonta da suke da kallo irin na son ta idasa maganarta.
Anmy ta k'ara kamo hannun Abih na dama tana mai k'ure shi da kallo, gwara a yita ta k'are, gwara ta nunawa Mardiya a lokacin da ka so wulak'anta bawa Allah kan rufa masa asiri, gwara ta fad'i muradinta idan ya so ko wace wace, idanuwanta a kansa, su kuwa idanuwansu a kanta inda zuciyoyi suka shiga bugawa tamkar zasu b'allo su fito daga k'irjin da dama a wajen.
A sanyaye tace "
_Idan kun yi comment zafafa, zaku samu zafafa🤣, wasan fa yanzu ne ya fara._🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
31
Irin yanda NAJEEBA, da UMMULKHAIR suka dago suka tsatsare Anmy da ido tamkar zasu dauketa da idannuwansu dan yannayin girman maganarsu masha Allah
Hakan ya saka Anmy daburcewa ta juya ta kalli SHAHEED
Ganni ta yi shima ya dago kansa daga duken da yake ya kura mata duban da ya sakata jin gaban jikinta sunna kara mutuwa tsoron abinda ta yi niyar fada ya darsu a cikin zuciyarta harma ta ringa dan kokarin sakin hannun Abih
Hannunta Abih ya riko da kyau yana kallonta ya ce" ki fadi muradinki kai tsaye kan yaren nan, kin isa da ni ubansu bale su, BILKISSU ki fadi koma me kike son fada kai tsaye, idanma ba zaki fada ba ki saka rana da lokacin da kike son a daura auren da ko wa kika zaba cikinsu ina mai tanatar maki mutuwata da mutuwar wace kika zabar kawai zai hanna wannan lamari
Mardiya baki daya jikinta rawa yake hakan ya saka ta shiga kokarin matsowa
Hankalinsa ne ya kai kanta
Sai da ya dan girgiza kansa kafin ya ce" MARDIYA, ki fita mu yi maganar sirri da masu rike sirrina, domin ni a yanzu ko lokacin cin abincina da izinin Allah ba zaki kuma sani ba kar ki je waje ki saka speaker ki ringa ihun na cika ci
Irin kallon tsanar da DAYABU ke mata da kallon gargadin dake shaida mata idanfa ta yarda ta matso kisa da su sai dai wata ba ita ba ya saka tana dogon wiya jikinta na rawa ta mike ta kai dubanta wajen mai martaba
Sai dai irin yanda ta ga idannuwansa ya saka ta fice da sauri ta tsaya kofa hankalinta tashe sakamakon rashin jin da waye kuma za'a daurawa sarkinsu aure a cikin y'ayan da ta tsana?
Fatanta kar ya kasance da wace sanadiyarta ta shigo rayuwarsu
Domin kuwa ta rantse da Allah idan har aka aurawa sarki Najeeba ta tabata gaba ta ci ba baya ba dan kuwa shi kansa saurayin nata ba wani uban mai kudin bane bale mulkin da zai yarda ya kama kafar Mai martaba
Kennan ta yi a banza ko me?
Alkawarin da ta yi cewar sai dai ta ji ana yiwa wata buda sai ta tabatar da shi koda kuwa hakan zai yi sanadiyar rabuwar nata auren
Waigawa ta shiga yi dan samun mafita
Sai aka yi rashin sa'a ta kaiwa madubi duka, dama abinda zai kaita gidan sarki take nema sai kawai ta fad'a motarsa ta nufi gidan sarkin, tun da aka fito daga sallah ta tsaya a hanyarsa dogarai na kakarewa aman sai da ta yi yanda ya gane itace kafin ta fasa kuka ta yi hanyar b'angaren Anmy.
Burinta ta fasa wannan sirrin y'ayansa su san abinda ya aikata, ta wanzar da tashin hankali tsakaninsu da mahaifinsu da su kansu.
A hankali Anmy ke girgiza kanta kafin ta ringa furta "Innalilahi wa inna ilaihi raj'une."
Da sauri ta shiga tatara k'annanun da su suna cike da tsoron ganinsu zaune gaban mai martaba dan su tsoronsa ma suke, sai Nusaiba dake ta mak'alar wuyan DAYABU tana wasa.
Anmy du ta tattara su ta tura su ciki tana jin kamar juwa zata kifata da k'asa.
Shi Kansa sarki sai ya sada kansa k'asa yana jin yanda kansa ke sarawa, ayau yana tare da b'acin ran da wannan fitinaniyar ta haddasa masa, sai ga wani gagarumin da ya tabbata Anmynsa sai ta shiga matsanancin tashin hankali, uwa uba Abih.
Abih gaba d'aya jikinsa ne ya ji ya fara masa wata mijirya kafin ya d'ora hannunsa daidai zuciyarsa ya rintse idannuwansa wasu zafafan hawaye suka shiga biyowa gefen kumatunsa.
Anmy ta sada kanta sai kawai ta fashe da kuka tana girgiza kanta tana b'oye fuskarta dan kunyar da take ji da irin maganar Mardiya.
Baki d'ayansu hankalinsu ne ya k'ara tashi, hakan ya saka du suka rasa ina zasu nufa, wajen Anmy din ko wajen Abih?
Da rarafe wa'inda suka fi kusanci da Anmy suka yi kanta suka ruk'unk'umeta, wa'inda suka fi kusanci da Abih kuwa Ummukulsum ce da Dayabu suka yi wajensa da Nusaiba suka had'e a jikinsa.
Mamakin hakan ya saka Anmy d'agowa hannunta na rawa ta kai dubanta wajen SHAHEED ta ga kansa a sade, aman ya damk'i sandar dake kusa da k'afarsa da damk'a mai tsananin da ya hadasa jijiyoyin hannun nasa k'ara yin tsaye rad'o rad'o.
A rikice take tatab'a jikinsu ta shiga fadin" baku yi mana fushi ba? Wallahi zan fad'a maku yanda aka yi, kun san k'adarar bawa bata fice shi kar ku yiwa mahaifinku da ni kaina da na taya shi b'oye sirrin nan fushi."
DAYABU dake dafe da hannun Abih wanda ya dafe daidai zuciyarsa muryarsa na rawa rawa ya ce" ABIH, kar ka kashe kanka a irin wannan lokacin da matarka take son tona asirinka dan manufarta da mu kanmu bamu sani ba,
Abih mun san da maganar nan dan girman Allah ka sassauta kar ka had'iyi zuciya domin idan ka mutu mu mukai asara ba ita ba."
UMMUKULSUM ta ririk'e hannayensa tana dannawa ta ce" Abih zafi nan ke maka? Idan yana zafi mu je asibiti, Abih wallahi wallahi bama jin kunyar ubanmu ko haushinka domin a haka muke son ka."
NAJEEBA ta k'ara rik'e Anmy tana b'oye fuskarta a jikinta tace" Anmy, meye na kukan? Kanmu aka fara ko kanmu za'a rufe?Anmy, koda mu dukanmu ne shegun shine aka ce zamu zo mu shak'e maku wuyan a kan me hakan ta faru? Innalilahi wa'ina ilaihi raj'une, Anmy ba shege bane abin gudu, d'an halal d'in aman mai halayan shege!
Anmy, ai ba daga yannayin da aka haifeka kake nuna halaya ba, halayanka na nuna wanda ya baka tarbiya."
"Anmy, kowani tsuntsu kukan gidansu yake yi! Koda dubu ya tara mu ubanmu ne, babu wata hallitar da zata zagar mana shi bamu sauke hak'oranta k'asa ba na rantse!"
Ummulkhairma kukan take tana kara share hawayen Anmy ta buda bakinta ta ce" Anmy, ku daina kukan nan haka, kin ga fa Abih sai rike daidai zuciyarsa yake
Najeeba ta saketa tayi wajen Abih ita ma ta d'ora kanta gefen k'afarsa tana jin kamar ranta ne ake wasa da shi, irin yanda iyayen nata ke zubar da hawaye sai ta ji tsoron Allah ya k'ara shigarta,
wai kunyar duniya kennan, duniyar ma yayanka, ina ga kunyar Allah? (ALLAH, ALLAH, DAN GIRMANKA DAN SOYAYARKA DA FIYAYEN HALITA ALLAH KA SHIRYE MU, KA YAFE MANA, KA SA MU GAMA DA DUNIYA LAFIA, KA RUFA MANA ASIRI DUNIYA DA KIYAMA).
Anmy da Ummulkhair ma da rarafe suka k'arasa wajen Abih, Anmy ta d'ora hannunta inda hannunsa yake tana hawaye tace "Ya isa, daga yau nauyin sai ya tafi ya baka lafia, yaya sun ji, sun sani sun sani." Sai ta had'e kanta da su suma sunna ta hawaye, shi kuwa da hannunsa yake daddab'a su yana jin wani irin a cikin ransa.
SHAHEED kuwa abu d'aya ya hana shi tashi daga zaunen da yake shine shara'a, ya hau kujerar nan ne dan ya yi shara'a tsakaninsu
tana zaune ta kawo k'ara ne, du irin kukan da mahaifiyarsa ke yi tamkar ana narka dalma ne ana zuba masa a k'irjinsa.
Mardiya kuwa baki da hanci duka a bud'e suke ta yi wani fik'i fik'i tana ganin abin na neman juyewa a kanta.
Anmy dake kuka tayi saurin d'agowa, hannun Dayyabu ta damk'o sannan ta damk'o na yayanta tana hawayen nan ta ce "Insha Allahu ba zamu yi kunya ba, insha Allahu Allah zai yi ta rufa mana asiri."
A hankali ta kuma fad'in" *YAYA, DAYABU, SHIN ZAKU BAIWA MAI MARTABA AUREN Y'ATA?* *INA BARAR AUREN YARINYATA WA SARKIN DAMAGARAM, INA BARAR AUREN Y'ATA WA YARON KA*?" Ta karashe tana mai hade hannayenta da nuna Abih.
Tunda ta fara neman auren ya d'ago da rinanun idanuwansa ya tsura mata daga ita har yayan nata da kuma y'ayan nata, suma y'ayan mata biyu da suka yi saura sai ya zamana kukan nasu ya d'auke d'if sai kallonta da suke da kallo irin na son ta idasa maganarta.
Anmy ta k'ara kamo hannun Abih na dama tana mai k'ure shi da kallo, gwara a yita ta k'are, gwara ta nunawa Mardiya a lokacin da ka so wulak'anta bawa Allah kan rufa masa asiri, gwara ta fad'i muradinta idan ya so ko wace wace, idanuwanta a kansa, su kuwa idanuwansu a kanta inda zuciyoyi suka shiga bugawa tamkar zasu b'allo su fito daga k'irjin da dama a wajen.
A sanyaye tace "
_Idan kun yi comment zafafa, zaku samu zafafa🤣, wasan fa yanzu ne ya fara._🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
31
Irin yanda NAJEEBA, da UMMULKHAIR suka dago suka tsatsare Anmy da ido tamkar zasu dauketa da idannuwansu dan yannayin girman maganarsu masha Allah
Hakan ya saka Anmy daburcewa ta juya ta kalli SHAHEED
Ganni ta yi shima ya dago kansa daga duken da yake ya kura mata duban da ya sakata jin gaban jikinta sunna kara mutuwa tsoron abinda ta yi niyar fada ya darsu a cikin zuciyarta harma ta ringa dan kokarin sakin hannun Abih
Hannunta Abih ya riko da kyau yana kallonta ya ce" ki fadi muradinki kai tsaye kan yaren nan, kin isa da ni ubansu bale su, BILKISSU ki fadi koma me kike son fada kai tsaye, idanma ba zaki fada ba ki saka rana da lokacin da kike son a daura auren da ko wa kika zaba cikinsu ina mai tanatar maki mutuwata da mutuwar wace kika zabar kawai zai hanna wannan lamari
Mardiya baki daya jikinta rawa yake hakan ya saka ta shiga kokarin matsowa
Hankalinsa ne ya kai kanta
Sai da ya dan girgiza kansa kafin ya ce" MARDIYA, ki fita mu yi maganar sirri da masu rike sirrina, domin ni a yanzu ko lokacin cin abincina da izinin Allah ba zaki kuma sani ba kar ki je waje ki saka speaker ki ringa ihun na cika ci
Irin kallon tsanar da DAYABU ke mata da kallon gargadin dake shaida mata idanfa ta yarda ta matso kisa da su sai dai wata ba ita ba ya saka tana dogon wiya jikinta na rawa ta mike ta kai dubanta wajen mai martaba
Sai dai irin yanda ta ga idannuwansa ya saka ta fice da sauri ta tsaya kofa hankalinta tashe sakamakon rashin jin da waye kuma za'a daurawa sarkinsu aure a cikin y'ayan da ta tsana?
Fatanta kar ya kasance da wace sanadiyarta ta shigo rayuwarsu
Domin kuwa ta rantse da Allah idan har aka aurawa sarki Najeeba ta tabata gaba ta ci ba baya ba dan kuwa shi kansa saurayin nata ba wani uban mai kudin bane bale mulkin da zai yarda ya kama kafar Mai martaba
Kennan ta yi a banza ko me?
Alkawarin da ta yi cewar sai dai ta ji ana yiwa wata buda sai ta tabatar da shi koda kuwa hakan zai yi sanadiyar rabuwar nata auren
Waigawa ta shiga yi dan samun mafita