← Book details Mage Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 2 OF 138

Sashe 2

Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kowa kansa na kasa sakamakon tashin da zai yi
A hankali ya sauko kafarsa ta dama mai dauke da takalmin fata irin na jinnin sarauta aman yana da kalar fukafuken dawissu bayan ya yi adu'a a kasan zuciyarsa

Sai da ya gama sauke kafafuwansa sannan ya mike da wani irin isa da takama
Yana mikewa da sauri sauran dogaran da suka karu suka shiga gyara masa rantsatsiyar suturar da ya saka ta yau wace sak irin fukafuken dawisu ne, harta da rawanin da ya sha wani irin rawani ne da akaiwa adon dawisu hakan ya sa baki daya ya dauke hasken wajen

Da sauri suka lallayu shi kuwa ya shiga takawa a hankali yana bi ta tsakiyar mutanen da suka layu

Kanta dake kasa hakama idannuwanta tana kallon kasa
A lokacin da ya kawo kafarsa daidai ita ta kasan gilashin dake fuskarsa mai hasken fari ya ga yar igiyar abin sauraron kidan da ta saka a kunnayenta tana sauraro, hakan ya sa ya dan jima a tsaye a kanta har sai da ta yi saurin dago da dubanta sai dai bata karasa kallon fusakarsa dake lulube da rawani da gilas ta yi saurin sada tsumamun idannuwanta da kanta tana kallon takalminsa da ya tafi da imaninta baki daya

Wata ajiyar zuciya mai zafi ya sauke yana ayanna tabas idan tana tunanin ta gagari kowa zai taka mata birki, a kulun ya hadu da ahalin gidansu yana mamakin irin zubin Halitar salihan mutane da akai masu sai dai tarin jaraba dake ciciyarsu, bare ita dake dauke da irin idannuwan nan masu lumshewa da wani irin lumtu lumtu masu tudun gaske da wani irin kumbura

Kwafa ya yi a ransa ya ayanna: ita har ta isa ta saka abin sauraron kida a lokacin da take zaune a gabansa?

A hankali ya kuma daga kafarsa ya ci gaba da takawa har ya bar wajen wanda barin wajen kadai sai da ya dauki kusan minti talatin tashinsa zuwa tafiarsa

Sai da ya shige sannan dogarin ya shaida masu summa iya daga kai

Kanta ta dago hade da harara ta sauke a fuskar dogarim wanda yake ta lulube kujerar sarki baima san tana yi ba

Yayansu na mikewa suma du suka mimike , mahaifinsu kuwa ya duka sunna magana kasa kasa da malan

Cike da bacin rai ta fara fita
Tana fita ta saka dogon takalminta fari kal mai tsinin gaske ta rike tsatsonta tana girgiza

Yayanta da sauran kannenta ne suka fito sai matar babansu a bayansu dauke da yarinyarta a goye

Da wani irin sauri ta zagaye ta koma kusa da ita ta kama goyon da sauri ta kunce hakan ya sa suka shiga kokowar kar ta kunce mata goyonta ita kuwa sai da ta kunce shi ta yi sauri ta damkawa yayarta mai dan sanyin cikin nasu wace ke fadi" ke meye haka? Ki rufa mana asiri da laya tsakanninmu

Bata tsaya ta saurari abinda take fada ba ta juya da sauro ta karasa kusa da matar mahaifinta wace ke tsaye da yan uwanta suma dangin balaki ta daga hannu ta wankawa matar mari da wani irin masifa ta aniya shigarta da duka

Yan uwan matar babansu na gannin hakan summa suka shigeta da dukan domin ai laya tsakaninta da su aka yi ba da yan uwanta ba
Yan uwanta na gannin hakan summa suka kasa hakuri domin familynsu wata irin family ce mai wuyar fasara, a tsakaninsu sunna cin kansu kamar me sai dai koda wasa basa bari a cuci dan uwansu idan kuwa aka yi gigin hakan sunna iya haduwa su lalasa mutun

Wata irin kokowa ce ta kaure tsakanin dangin matar mahaifinsu da kuma su hakan ya saka baban yayansu dora hannayensa saman kansa a fili furta" shikenan, yau dai karshenmu ya zo, shikenan ta halakamu baki daya

Da sauri ya karasa ya shiga janyo kannen nasa du wanda ya yi gardama kuwa hannunsa yake dagawa ya wankawa mutun mari nan da nan sai mutun ya bar fadan, mutane kuwa sunna kallon ikom Allah basu shiga ba domin kana iya shiga dan rabiya abin ya juye kanka su kuwa basa fatan fada da wannan ahali

Yana damkar hannunta itane ta karshe sai da ya kaita kusa da motarta ya saketa
Tana ta maida numfashi bata ankara ba ya daga hannunsa ya dauketa da gigitacen marin da ya sakata jin wani irin kauuu har kunnayenta suka yi kamar sun rufe tsabar saukar marin da zafi

Cike da fada ya ce" kin kashe mu! Kin kashe mu! Ubanme ya kaiki marinta bayan yanzu aka mana tsakani da laya a gabanki aka dagata?

A firgice sakamakon zafin marin da ya dada mata da dago shanyayun idannuwanta masu matukar haske da girma ta kale shi, kamar an mintsineta ta kwala ihu tana fadin" *karya ne! Ba cikaken bane! Bilahilazi sun daukeka wawa ba cikaken Alkur.anin bane suka saka yaya DAYABU!*

Da sauri ya tsaya ya kura mata ido yanda aka yaga mata rigarta sai haki take tana hararan wajensu , sai da ya karyar da wuyansa ya sanyaya muryarsa ya ce"
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻

*Na*

*SAJIDA*

4

Tana murmushi tana kallon yanda sarauta ta karbi yaron nata, yanda sarauta ke kara masa wani irin nutsuwa da kamala a hankali ta ce" Allah ya tsare gabanka, Allah ya tsare bayanka, ya tsare makwoncinka, ya tasheka da kansa
Allah ya yi maka albarka

Idannuwansa ya lumshe sakamakon jin dadin adu'ar da mahaidiyarsa ke yi masa har sai da ta dasa Aya sannan ya juyo ya kara dukar da kansa ya furta" amen Anmy

Cike da tafiar kasaita ya fito daga bangaren mahaifiyarsa
Bai zame ko'ina ba sai baban dakin karatun da suke raba dare sunna karatu da kuma ayukan sirri shi da mutanensa na sirri ciki kuwa harda yayan mahaifiyarsa da baban liman din fadar baki daya

Sai da ta tsaya a baban wajen saida abinci ta sayi pizza wajen gida goma inda ta bayar da jaka hamsin cif aka zuba mata a cikin motarta

Tana tayarwa ta karasa gidansu,

Mai gadi ne ya bude mata kofar ta idasa shiga da motarta

Yabi daya daga cikin masu aikinsu ta saka kwaso mata pizzar tana kai mata bangarensu da kannenta mata

Sai da ta gama kwashewa ta rufe motarta da dan kwalin nan a hannunta tana dan wasa da shi ta shige cikin falon nasu

Ja ta yi ta tsaya sakamakon gannin yayanta na bangarensu sannan kannen nata da kuma yayunta har sun yi wanka sun sasaka kayan baci

Wani dan malalacin murmushi ta saki tana idasa shiga ta ce" aa, me kuke a zaune?

Dubanta sukai gaba dayansu, gannin sai wayancewa take ya saka yayarta mai sunna Umakhulsum girgiza kanta ta ce" ai dole ki ce haka, dole ki ce haka Najeeba bayan ke kin iya tankwalo masifa tana baci!

Da sauri NAJEEBA ta ce" toh fa

Dayar mai sunna Zahrau wace itace mai sanyinsu ta ce" yanzu Najeeba kennan nima kina iya daga hannu ki wanke ni da mari? Kuma kin sani sarai da ba barinki zai yi haka ba koda kuwa Anmy ta yi dabarar sakawa ta rama sai ya maki wata muguwar muguntar marin masa matarsa ko?

Da Sauri DAYABU na dan dago hannayensa ya dunkule guda ya ce" fisabililahi idan ba jarababiyar y'a ba bilahilazi da ta wanka mata marin nan sai na shiga neman na tashi ni ba fifike ba, NAJEEBA a gaban sarki ki mari matarsa dan kina yar yayan mamansa?

Gaban goshinta ta dafe tana karasa shigowa
Sai da ta zauna tana kallonsu ta ce" meye hukuncina? Cin uwani zaku yi yanzun ko yaya?

Tasowa yayansu ya yi da sauri ransa bace ya nufota

Da sauri ta rufe fuskarta domin wajen da bata so a kuma taba mata a yau kennan ,

Sai da ya karaso ya daga hannunsa ya yi ya yi ya bambarw hannayen nata aman sai kara shigewa cikin jikinsa take, nan fa tumurtu ya tashi gannin zata wahalar da shi a banza ya saka shi sakinta yana maida numfashi ya zauna ya ce" shegiya mai ilimin kokowa, kin ci sa'a fuskarki a boye da yau na fitar da sahun hannuna a jikinta

Kanwar NAJEEBA dake dariya ne ta ce" wai ku ji fa, kamar wanda yaya zai mata wani duka mai karfi abinda nan zaka ringa zanen idan ka kamata ka fara kwalo da ita, tana zuwa gabanka sai ka bige da yi mata nasiha

Da sauri ya kaleta yana zaro ido ya ce" kin ga wannan mai sunnan Gimbiyar sam bata da kirki, idan ta tashi magana sai ta ringa yiwa mutun shari ba gashi ba na jijigata kuma ki bari ki ga ta kuma marin matar sarki zara ga abinda zan mata

Su dai du murmushi suke ita kuwa NAJEEBA ta hade fuska sai kara turo baki take wai sun hade mata kai sunna mata fada

Sai da suka gama yi mata kashedin ta kiyayi yiwa sarki hayen nan ta sada kanta ta ce" kennan sai na kyaleta ko? Kun san me tace ne? Cewa fa ta yi *ke kauce yar talakawa*

Ido Umulkhair ta zaro ba shiri ta ce" kan ubancen, shi yasa na so zuwa na ji a kan me zata maida maki mari yaya ya rikeni ashe iyayenmu ta zaga?

Yayansu ya yi shiru shima ransa na kunna

Zahra ta ce" kin min daidai dan ubanta ya kashe mu!

Su masu yi mata kashedin kar ta kuma sai gasu sunna fadin ai ko sunne sai sun rama, nan da nan suka shiga zanen idan ya kama su ya kashe su sun yi, yayansu kuwa ya rafka tagumi yana kallon dan karamin kanensu wanda su biyu ne kawai maza sauran su goma sha biyar baki dayansu mata ne kuma ko daya ba'a yiwa aure ba tukunnan

Ajiyar zuciya kawai ya kuma saukewa ya janyo pizzar ya shiga bubudewa yana raba du gida guda a biyu yana mikawa yaran kannanu
Sai da ya yi sauran manyan ya basu guda guda har NAJEEBAR sannan suka shiga ci sunna dan taba hirarsu

Sai da suka gama yar karamarsu mai sunna lalla wace bata kai shekara shida ba ta je ta langwabe a jikinsa tana hamma, a hankali ta ce" yaya Dayabu, ina Abihna?
Chapter 2 · 0% Book details