Sashe 34
Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gannin yanda take wani ringeshe a cikin motarsa ya kara bata masa rai, me ya sa Anmy ke yi masa haka ne? Yau da ace cikin kannenta ko yayunta ne bashi da damuwa sai ya fita da su a cikin motarsa da su din ya yarda da su cewar koda basa jin magana to fa basu wulakanta kansu ba
Aman sai ta saka shi daukota a motarsa mai tsafta, ta shigo masa mota tana garwaya numfashinta da nasa mai tsafta haka kawai ta zauna a wajen da yake ringesa kansa dan ya huta?
Ya zama wajibi ya batar da motar nan sunna dawowa domin ba zai kuma shigarta ba
Da ta san irin yanda yake kyankyaminta, da bata yi gigin yarda ta shiga wajen da yake ba
Halayenta sam basu yi masa ba
Muguwa ce, azaluma ce, makaryaciya ce, mazinaciya ce!
Idanma bashi da tabas shi zai samowa Anmy shaidar da ba zata iya hanna shi hukuntata a bainar nasi ba! Ya yiwa kansa alkawarin a kanta zai tsoratar da matasan samari da matasan yan mata da manyan yan iskan garinsa domin sai ya yi mata hukunci bulalar da ta hau kanta na zina da aurenta komai yawanta shi yasa yake so ya yi mata damka irin na gani da gani
Muryarsa a dake ya ce" *ki fitar min a mota!*
Maganar nasa rairai a cikin kunnayenta domin dama sauraro take
Dan zabura ta yi ta dago tana ta zarar ido
Amintacensa ne ya fita dan bude mata bangarenta domun dama bai hude bane dan yana jiran umarni
Yana budewa SHAheed ya watsa mata damin kudi a jikinta muryarsa still a dake ya ce" *nan da awa biyu ki tabata mun sameki a nan*
Yana gama fada ya kuma komawa ya gyara zamansa
Ai da wani irin sauri ta fita a motar da kudin a hannunta dan a saman cinyarta suke, ita a yanzu bata da bakin da zata iya budawa ta ce wani abu ko ta meni yin wani abu na rashin kunya
Tana fita ya mayar da mitar ya rufe ya zagaya da sauri ya shige suka daga
Gaba dayanta ta idasa zaro idannuwanta ta dora hannayenta saman kanta a fili ta furta" wayo wayo wayo innalilahi wa'ina ilaihi raj'une yau na ga masifa ido da ido yau na yi mota daya da arne marar mutunci marar tausayi mai cin danyen nama! Na rantse macijin nan ka fito da shi ne dan ka je ka kashe wani, yo waye bai sani ba cewa kashe kashe kuke a tsakaninku dan kujerar nan da kuke sama
Allah ya isana da ka tsoratani, kuma na rantse sai ka sauka sarki mai adalci ya hau kujerar nan annamimi mai ido kamar na mujiya!
Sai a lokacin ta kalli kudin da ya zuba mata
Dami guda ne na manyan kudi sabin bugawa domin yanda suke mike suke hade zai nuna maka cewa sababin fitowa ne daga banki yan jika goma goma je da zara iya rantsewa ba karamin kudi bane
Abin dake jikinsu ta kunce ta watsar a nan sannan ta bi su da yawu tana cire alkyabar nan da ta hana mata sukuni tana ta sauke ajiyar zuciya ta ce" Allah ya tsareni da cin haram! Kai ko abincin fada ina cin wanda na san Anmy ta bada kudin aka kawo domin ban taba cin cimar da ta shafi shinkafa, ko wani abin da na san daga aljihunka zai iya fitowa!
Yanda ka tsane ni, ni nama fika tsanarka azalumi kawai mai cinye kudadenmu mu talakawa
Ta saman kudin ta bi tana tafiyarya da dan sauri dan a lokacin da ta duba agogon hannunta har ta ci minti goma a kan wanda ya barta
Saloon dinta ta je suka gagaisa da masu yi mata aiki sannan ta kara duduba komai ta ware kudadenta ta bara masu na anfannin yau da gobe kafin ta dawo nan da kwana hudu
Daga nan sai ta nemi mai babur ta dane tace da shi ya kaira wajen Hashimu mai nama
Agashe ta bashi ya amso mata mai ruwa ruwa har na jaka biyar tukunya ce sannan ta suka kuma daukowa suka nufi wajen saida ice cream
Haka take murmushi gannin yau zata sha mutumen nata wato ice cream dan ta kwana biyu bata sha ba domin Anmy bata barinsu yawan shan sanyin nan ko zaki
Siya ta yi har roba biyu tace da shi ya kaita stade
Yana ajiyeta ta dauki har jaka biyu ta bashi sannan ta ringa takawa a hankali a kafarta har ta karaso wajen mai gadin wajen suka gaisa da mutunci sannan ta samu ta shige cikin nutsuwa ta nufi wajen zamanta wajen hutunta
Tana zuwa ta zauna tana gannin yanda daidaikun mutane kowa ke sha'anninsa, a wajenfa babu yaku bayi, du manya ne kowa kuma na sha'aninsa
Ledarta ta buda mai dauke da naman nan ta fara ci a hankali tana lumshe idannuwanta dan tana mutuwar son tukunya
Sai da ta ji ta yi hani'an sannan ta dauko ice cream dinta roba daya ta buda ta gyara zamanta ta saka yar cokalinta tana dan diba kadan tana sakawa a bakinta
Wayarta ta dauka ta rubuta message kamar haka" *Na so zuwa dan gannin likitan zuciyana, sai dai na cika da fargabar irin yanda ya kasance mau cike da kwarjini a idannuwana, na yi masa kallon tsaf din da har na lura da irin hararar da matarsa ke jefa min wanda ya sakani jin tsoron zuwa wajensa a wannan rana Shin likitan zuciyana zai yi kin alfarmar fadawa gimbiya cewa na zo ya auna ni? Zai taimaka ya hada ji da wani likitan wanda zai auna ni? Domin ina tsoron tsumamun idannuwansa su sakani tsumewa na lume a cikin kogin da ba zan iya fitowa ba.....sako daga NAJEEBA MUTALAB*
Tura sakon ta yi ta ci gaba da shan ice cream dinta
Ta kuwa harbo a daidai, domin a lokacin ya gama shiryawa tarbanta, matarsa kuwa ta gama shiryawa cin ubanta a kofar clinik din domin zuwan wani bako a cikin bakar mota sidik ya saka baki daya aka fitar da kutanen dake ciki sai majinyata da masu jinyarsu daidaya, hakan ya sakata dakatawa a kofa ita da babar y'arta wace ta rakota su ci uban NAJEEBA! (HOUM)
har tsuma hannunsa yake a lokacin da ya karanta mesage din da sai ya rantse bai taba karanta mesage mai dadinsa ba ya shuga bata amsa kamar haka *bukatunki, ki tabatar da amsasu ne hannu bibiyu a wajen likitan zuciyarki, wa kike so ya duba maki zuciya da ya fi ni? Ni zan kula da ke na ririta zuciyarki na yi mata fadan da ba zata kuma yi maki suka ba, zan sanarwa mamanmu cewa kin zo, aman zan biki bashi ko ki zo na duba ki ko na zo na duba ki, domin bana wasa da zuciyar mai dauke da zuciyata!*
Samun kanta ta yi da sakin murmushin mesage dinsa, lale ba laifi kalamansa zafafa ne da har suka sakata kwafarsu
Lale yana da tsumamun kalamai kuma ta yaba
To yaya fagen aljihunsa?
Ta tambayi kanta tana murmushi
Sosai take jin dadin iskar wajen harma ta cika da mamakin ina mai kwali ne yau? Dan bata gansa ba, ko ya shige wani wajen ne? Ko ya koma abujar?
Lokaci na shige mata bata sani ba domin ta dukufa tana amsa mesage din tarin samarinta kowane daidai da takun tafiyarsa ciki kuwa harda sojanta da likitanta, da ambasador dinta
Sosai take nishadi harma yannayi tsoro da firgici suka barta
Bakinta take tabewa idan ta ga wani mesage din,
Takan girgiza kanta idan ta ga sakon kowani gara sai ya daki kirji ya turo mata sako
Wata yar dariya ta yi a bayane a lokacin d ata tuna maganar yayanta da yake cewa, mace idan ta zama ita kowama saurayinta ne, zata ringa haduwa da samarin kala daban daban, su gajale, su zinataile su wawaye, su mahaukataye da sauransu
Najeeba, ki kula a garin damagaram, domin mai damagaram ba zai hukunta wani dan ya maki laifi ba.....
Wannan maganar ita ta tunatar da ita da maganar dunkum cewar awa biyu ya bata
Wata irin zabura ta yi ta duba agogo
Karfe goma ce ta gota harda minti arba'in
Wato ta dauki awa biyu da minti talatin da bakwai
Wata irin dirowa da ta yi ta mike a guje ta saki ledar naman da ta yi niyar kaiwa yan uwanta da uce cream din ta aniya dankara gudu da alkyabarta a hannunta tana ihun kiran kabu kabu
Tana tsayar da dan acaba ta bashi jaka biyar hakoranta har sunna hadewa ta ce" ka falfala gudun mutuwa da ni ka kaini magama gudun hanyar gidan sarki
Mai yin na banzama bale harda kudi da kuma rokon mai hawan? Ai kuwa ya buga babur ya tayar ya warcu babur a dubub lamba ya nufi wajen da aka bukata
Adu'a kawai take tana saka alkyabarta jikinta na rawa tana fatan Allah ya sa bai zo ba
Na mutu ta fada a dan fili a lokacin da ta ga motarsa tsaye a wajen da suka ajiyeta, sannan daidai kudin nan da ta watsa da yake dare ne Allah bai kawo wanda hankalinsa ya kai wajen ba
Shikenan ta kuma fada tana son dirkowa aman sai da dan acabar nan ya sadata gata ga motar yana washe mata baki irin ya mata abin kirkin nan
Sai kawai ta ji ita kam ta gama yawo,
Dokar Anmy ce kiyaye acaba wace shi ya dora ita kuwa ta dorawa y'ayanta
Yakan fadawa Anmy cewa, bai ga daraja a macen da zata wara kafarta ta hau acaba ta zauna jikin mai mashin ya jata ba
Tuki da ya gaji birki da sauransu komai na iya faruwa a babur din nan
Gaba faya jikinta na rawa ta shiga kiciniyar saukowa
Kyar ita yake kallo, tun da suka karaso kusan minti talatin kennan ya ga kudadensa da ya bata a zubde a kasa
Wato ita bata cin halal shine ta je ta nemo haram dinta?
Sai kuma irin jiran da ta saka shi yi, zai rantse da Allah ko mahaifiyarsa bata saka shi jira daga lokacin da Allah ya kara daga darajarsa ko mamansa ke bashi daraja ta kiyaye lokutansa
Aman sai ta saka shi daukota a motarsa mai tsafta, ta shigo masa mota tana garwaya numfashinta da nasa mai tsafta haka kawai ta zauna a wajen da yake ringesa kansa dan ya huta?
Ya zama wajibi ya batar da motar nan sunna dawowa domin ba zai kuma shigarta ba
Da ta san irin yanda yake kyankyaminta, da bata yi gigin yarda ta shiga wajen da yake ba
Halayenta sam basu yi masa ba
Muguwa ce, azaluma ce, makaryaciya ce, mazinaciya ce!
Idanma bashi da tabas shi zai samowa Anmy shaidar da ba zata iya hanna shi hukuntata a bainar nasi ba! Ya yiwa kansa alkawarin a kanta zai tsoratar da matasan samari da matasan yan mata da manyan yan iskan garinsa domin sai ya yi mata hukunci bulalar da ta hau kanta na zina da aurenta komai yawanta shi yasa yake so ya yi mata damka irin na gani da gani
Muryarsa a dake ya ce" *ki fitar min a mota!*
Maganar nasa rairai a cikin kunnayenta domin dama sauraro take
Dan zabura ta yi ta dago tana ta zarar ido
Amintacensa ne ya fita dan bude mata bangarenta domun dama bai hude bane dan yana jiran umarni
Yana budewa SHAheed ya watsa mata damin kudi a jikinta muryarsa still a dake ya ce" *nan da awa biyu ki tabata mun sameki a nan*
Yana gama fada ya kuma komawa ya gyara zamansa
Ai da wani irin sauri ta fita a motar da kudin a hannunta dan a saman cinyarta suke, ita a yanzu bata da bakin da zata iya budawa ta ce wani abu ko ta meni yin wani abu na rashin kunya
Tana fita ya mayar da mitar ya rufe ya zagaya da sauri ya shige suka daga
Gaba dayanta ta idasa zaro idannuwanta ta dora hannayenta saman kanta a fili ta furta" wayo wayo wayo innalilahi wa'ina ilaihi raj'une yau na ga masifa ido da ido yau na yi mota daya da arne marar mutunci marar tausayi mai cin danyen nama! Na rantse macijin nan ka fito da shi ne dan ka je ka kashe wani, yo waye bai sani ba cewa kashe kashe kuke a tsakaninku dan kujerar nan da kuke sama
Allah ya isana da ka tsoratani, kuma na rantse sai ka sauka sarki mai adalci ya hau kujerar nan annamimi mai ido kamar na mujiya!
Sai a lokacin ta kalli kudin da ya zuba mata
Dami guda ne na manyan kudi sabin bugawa domin yanda suke mike suke hade zai nuna maka cewa sababin fitowa ne daga banki yan jika goma goma je da zara iya rantsewa ba karamin kudi bane
Abin dake jikinsu ta kunce ta watsar a nan sannan ta bi su da yawu tana cire alkyabar nan da ta hana mata sukuni tana ta sauke ajiyar zuciya ta ce" Allah ya tsareni da cin haram! Kai ko abincin fada ina cin wanda na san Anmy ta bada kudin aka kawo domin ban taba cin cimar da ta shafi shinkafa, ko wani abin da na san daga aljihunka zai iya fitowa!
Yanda ka tsane ni, ni nama fika tsanarka azalumi kawai mai cinye kudadenmu mu talakawa
Ta saman kudin ta bi tana tafiyarya da dan sauri dan a lokacin da ta duba agogon hannunta har ta ci minti goma a kan wanda ya barta
Saloon dinta ta je suka gagaisa da masu yi mata aiki sannan ta kara duduba komai ta ware kudadenta ta bara masu na anfannin yau da gobe kafin ta dawo nan da kwana hudu
Daga nan sai ta nemi mai babur ta dane tace da shi ya kaira wajen Hashimu mai nama
Agashe ta bashi ya amso mata mai ruwa ruwa har na jaka biyar tukunya ce sannan ta suka kuma daukowa suka nufi wajen saida ice cream
Haka take murmushi gannin yau zata sha mutumen nata wato ice cream dan ta kwana biyu bata sha ba domin Anmy bata barinsu yawan shan sanyin nan ko zaki
Siya ta yi har roba biyu tace da shi ya kaita stade
Yana ajiyeta ta dauki har jaka biyu ta bashi sannan ta ringa takawa a hankali a kafarta har ta karaso wajen mai gadin wajen suka gaisa da mutunci sannan ta samu ta shige cikin nutsuwa ta nufi wajen zamanta wajen hutunta
Tana zuwa ta zauna tana gannin yanda daidaikun mutane kowa ke sha'anninsa, a wajenfa babu yaku bayi, du manya ne kowa kuma na sha'aninsa
Ledarta ta buda mai dauke da naman nan ta fara ci a hankali tana lumshe idannuwanta dan tana mutuwar son tukunya
Sai da ta ji ta yi hani'an sannan ta dauko ice cream dinta roba daya ta buda ta gyara zamanta ta saka yar cokalinta tana dan diba kadan tana sakawa a bakinta
Wayarta ta dauka ta rubuta message kamar haka" *Na so zuwa dan gannin likitan zuciyana, sai dai na cika da fargabar irin yanda ya kasance mau cike da kwarjini a idannuwana, na yi masa kallon tsaf din da har na lura da irin hararar da matarsa ke jefa min wanda ya sakani jin tsoron zuwa wajensa a wannan rana Shin likitan zuciyana zai yi kin alfarmar fadawa gimbiya cewa na zo ya auna ni? Zai taimaka ya hada ji da wani likitan wanda zai auna ni? Domin ina tsoron tsumamun idannuwansa su sakani tsumewa na lume a cikin kogin da ba zan iya fitowa ba.....sako daga NAJEEBA MUTALAB*
Tura sakon ta yi ta ci gaba da shan ice cream dinta
Ta kuwa harbo a daidai, domin a lokacin ya gama shiryawa tarbanta, matarsa kuwa ta gama shiryawa cin ubanta a kofar clinik din domin zuwan wani bako a cikin bakar mota sidik ya saka baki daya aka fitar da kutanen dake ciki sai majinyata da masu jinyarsu daidaya, hakan ya sakata dakatawa a kofa ita da babar y'arta wace ta rakota su ci uban NAJEEBA! (HOUM)
har tsuma hannunsa yake a lokacin da ya karanta mesage din da sai ya rantse bai taba karanta mesage mai dadinsa ba ya shuga bata amsa kamar haka *bukatunki, ki tabatar da amsasu ne hannu bibiyu a wajen likitan zuciyarki, wa kike so ya duba maki zuciya da ya fi ni? Ni zan kula da ke na ririta zuciyarki na yi mata fadan da ba zata kuma yi maki suka ba, zan sanarwa mamanmu cewa kin zo, aman zan biki bashi ko ki zo na duba ki ko na zo na duba ki, domin bana wasa da zuciyar mai dauke da zuciyata!*
Samun kanta ta yi da sakin murmushin mesage dinsa, lale ba laifi kalamansa zafafa ne da har suka sakata kwafarsu
Lale yana da tsumamun kalamai kuma ta yaba
To yaya fagen aljihunsa?
Ta tambayi kanta tana murmushi
Sosai take jin dadin iskar wajen harma ta cika da mamakin ina mai kwali ne yau? Dan bata gansa ba, ko ya shige wani wajen ne? Ko ya koma abujar?
Lokaci na shige mata bata sani ba domin ta dukufa tana amsa mesage din tarin samarinta kowane daidai da takun tafiyarsa ciki kuwa harda sojanta da likitanta, da ambasador dinta
Sosai take nishadi harma yannayi tsoro da firgici suka barta
Bakinta take tabewa idan ta ga wani mesage din,
Takan girgiza kanta idan ta ga sakon kowani gara sai ya daki kirji ya turo mata sako
Wata yar dariya ta yi a bayane a lokacin d ata tuna maganar yayanta da yake cewa, mace idan ta zama ita kowama saurayinta ne, zata ringa haduwa da samarin kala daban daban, su gajale, su zinataile su wawaye, su mahaukataye da sauransu
Najeeba, ki kula a garin damagaram, domin mai damagaram ba zai hukunta wani dan ya maki laifi ba.....
Wannan maganar ita ta tunatar da ita da maganar dunkum cewar awa biyu ya bata
Wata irin zabura ta yi ta duba agogo
Karfe goma ce ta gota harda minti arba'in
Wato ta dauki awa biyu da minti talatin da bakwai
Wata irin dirowa da ta yi ta mike a guje ta saki ledar naman da ta yi niyar kaiwa yan uwanta da uce cream din ta aniya dankara gudu da alkyabarta a hannunta tana ihun kiran kabu kabu
Tana tsayar da dan acaba ta bashi jaka biyar hakoranta har sunna hadewa ta ce" ka falfala gudun mutuwa da ni ka kaini magama gudun hanyar gidan sarki
Mai yin na banzama bale harda kudi da kuma rokon mai hawan? Ai kuwa ya buga babur ya tayar ya warcu babur a dubub lamba ya nufi wajen da aka bukata
Adu'a kawai take tana saka alkyabarta jikinta na rawa tana fatan Allah ya sa bai zo ba
Na mutu ta fada a dan fili a lokacin da ta ga motarsa tsaye a wajen da suka ajiyeta, sannan daidai kudin nan da ta watsa da yake dare ne Allah bai kawo wanda hankalinsa ya kai wajen ba
Shikenan ta kuma fada tana son dirkowa aman sai da dan acabar nan ya sadata gata ga motar yana washe mata baki irin ya mata abin kirkin nan
Sai kawai ta ji ita kam ta gama yawo,
Dokar Anmy ce kiyaye acaba wace shi ya dora ita kuwa ta dorawa y'ayanta
Yakan fadawa Anmy cewa, bai ga daraja a macen da zata wara kafarta ta hau acaba ta zauna jikin mai mashin ya jata ba
Tuki da ya gaji birki da sauransu komai na iya faruwa a babur din nan
Gaba faya jikinta na rawa ta shiga kiciniyar saukowa
Kyar ita yake kallo, tun da suka karaso kusan minti talatin kennan ya ga kudadensa da ya bata a zubde a kasa
Wato ita bata cin halal shine ta je ta nemo haram dinta?
Sai kuma irin jiran da ta saka shi yi, zai rantse da Allah ko mahaifiyarsa bata saka shi jira daga lokacin da Allah ya kara daga darajarsa ko mamansa ke bashi daraja ta kiyaye lokutansa