Sashe 47
Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kamata tayi ta fitar da ita daga cikin ruwan dan har lokacin tana ta zubar da hawaye wani irin ciwo take ji a zuciyarta domin a rayuwarta idan akoy abinda ke tayar mata da hankali, ya sakata a firgici to fa irin abinnan ne.
Kayan ta saka jikinta a mace suka fito tare.
K'arasawa tayi ita ma ta zauna ta d'ora kanta gefen wuyan Ummu
Muryarta a sanyaye ta ce" Ummu, kiyi magana mana, dan Allah ki ce wani abu mana."
Suma hawayen suka ringa sharewa shi kuwa yana kallonsu.
Sun d'auki kamar minti goma a haka kafin a hankali ta bud'a bakinta, hawaye ne wasu ke korar wasu cikin disashiyar muryarta ta furta" Dama me kuke jira da rayuwata? Kun manta wacece mahaifiyata? Yanzu haka idan kuka je tudun jamus layi na biyu babbar k'ofa mai ruwan blue gidanta ne, zaune take tana amsar kud'in wannan."
"Ki yi min shiru!" Ya bud'a bakinsa tun d'azun ya fad'a da wata murya ta tsawa wace ta saka du suka rintse idannuwansu suka sada kawunansu
Muryarsa ya kuma bud'awa yana cijewa yace" ku tashi baki d'ayanku mu fita!"
Da sauri Najeeba ta d'ago tana kallonsa, sai dai ba damar yin magana domin har ya juya ya fara fita.
Zahrau kam bata da katab'us, baki d'aya duniyar ce ta yi mata zafi ta rasa wani tunani zata yi da irin wannan lamari, aman tsawatarwar daya yiwa ummu ta sakata jin dama dama domin idan har haka zata ringa fad'i idan bakinta ya bud'e tana iya idasa halaka masu tunani su yi ta kuka.
Kamata suka yi ta mik'e da k'yar tana rintse idannuwanta kafin ta sauko.
Kamata suka yi a hankali tana tafiya suka fito domin basu san inda zai kaisu ba, su kuwa basu isa su k'i fitowar ba.
Irin yanda suka ga duk mutane ne a zazaune kama daga Sarkin Agadez, na damagaram, Gimbiyoyin, yarima da matarsa sai du suka ji hankalinsu ya k'ara tashi.
A hankali suka k'arasa da niyyar zaunar da ita a kasa, sarkin garin Agadez dake kallonsu ne kamar zai fashe da kuka shi kam ko rawanin babu a kansa yau an yi abinda ya cujewa buzu nad'i ya nuna masu doguwar kujerar dake ajiye."
Nufar wajen suka yi suka zaunar da ita kafin su zauna kusa da ita sosai a jikinta.
Najeeba irin kallon da take bin yarima da mahaifiyarsa da shi irin kallon nan ne wanda zaka ji kamar ka kashe mutun.
Yayi d'agowar kansa ya fi a k'irga sai zai bud'i baki sai ya kasa hakan ya saka Gimbiya saurin zamowa kasa ta had'e hannayenta tana kallonsa muryarta na rawa ta furta" dan girman Allah a rufa mana asiri, kar ku manta yarima shine mai jiran gado, sirrinsa ya fita tamkar sirrin baki d'aya gidan nan ne zai fita, Allah ya huci zuciyarka a rufawa yarima asiri a gafarta masa."
Tayi gaggawar juyar da kanta wajen SHAHEED ta d'an k'ara rarafawa hannayenta a had'e ta ci gaba da fadin" Ku rufa mana asiri, wannan sirri namu ne baki d'aya, dan girman Allah ku rufa mana asiri."
Du wani motsin kowa yana hakimce ne yana bi da kallo, bai furta ko A ba.
Kansa dake kasa ya dago, irin kukan da yake sai ya baiwa mutun tausayi.
Da sauro ya rarrafa ya nufi wajenta hakan ya sa sarki sakar masa tsawar da ta saka bai idasa idasawa har inda take ba aman ya ja daga d'an nesa.
Hannayensa ya had'e ya kara duk'awa sosai yana ta kuka kamar zai mutu yace" Dan girman Allah ki yafe min wannan lamari da na aikata maki, na rantse maki da Allah ni ba mazinaci bane
na je d'akin iyalina ne ta fito ta bar min d'akin sai na biyo bayanta a tunanina inda kike tsaye itace a tsaye domin idannuwana sun rufe, satina biyu kennan tana guje min a shinfid'ata, zaki ga na rufe maki ido da bakinki ba dan komai ba sai dan sannin tana iya k'wala min ihu ta tara min jama'a ni kuwa na yi alk'awarin a daren sai ta bani hakk'ina, ban san cewa ba da ita nake mu'amala ba sai da na kai ga shiga wajen da ba nawa ba, wallahi wallahi ni ba mazinaci bane, sannan ba mai afkawa mutane bane, na kasance ina koyi da halayen nagartatun mutane dan na kasance nagartace,
ban tab'a aikata zina ba ko a lokacin da bani da aure, dan girman Allah ki yafe min wannan b'arna da na aikatawa rayuwarki sannan na aikatawa rayuwata, ki maka ni kotu a yanke min hukunci daidai da laifina ko ki kaini kotun musulunci a yanke min hukuncin jifa domin ba zan iya rintsa ido da hak'inki irin haka a kaina ba."
Mahaifiyarsa ce ta fashe da kuka mai tsanani.
Da sauri ya juya ya k'arasa kusa da SHAHEED ya duk'a ya kama k'afafuwansa yana gunsheken kuka ya shiga fadin" Dan Allah yaya ka saka baki ta yafe min, ka saka baki ta gafarta min kar abin nan ya tab'a d'iyan d'iyana, ka ga wannan dake zaune zata iya maimaita abinda ya faru tsakanina da ita kafin ta baro d'akina, hakan yasa na biyota da sauri ban san inda ta lab'e min ba na fito da gudu ina nemanta sannan itama wando ne a jikinta da rigar baci na rufe bakinta da hanuna da idanuwanta dan kar ta min ihu ko ta fad'a min abinda zai fitar min da son zuwa gareta a raina hakan ya sa na afka mata, ba zan iya fahimtar ba da matata nake ciki ba, hankalina ya gama tafia burina na samu nutsuwa."
Gannin ya k'ura masa firgitatun idanuwan nan nasa masu matuk'ar abin tsoro ya saka shi sakinsa ya juya wajen mahaifinsa ya karasa ya kama k'afarsa.
Kafin ya fara magana ya hamb'are shi da k'afar tasa hakan yasa ya fad'i gefe aman bai gaza ba ya kuma tashi ya kara ruk'unk'ume k'afar tasa yana wani irin kuka murya a cakule ya furta"BABA."
Sarki ya saka k'afarsa yana kiciniyar kuma hamb'are shi aman ya gaza dan baki d'aya jikinsa yayi sanyi lamarin ya shige shi a lokacin da bai shiryawa hakan ba.
Muryarsa ya bud'a a birkice ya furta" Inna lillahi wa'ina ilaihi raj'une."
Innalilahi wa'ina ilaihi raj'une! Sai kawai muryarsa ta shiga rawa sai kuka ya k'wace masa, hakan ya saka SHAHEED saurin rintse idanuwansa ya sadda kansa.
Muryarsa na rawa ya shiga furta" Lalle kana wasa da adininka, kana wasa da ibadunka, idan kuwa ba haka ba kaima k'addararka mai tsauri ce domin kamar yanda ka fad'a saina hukuntaka! Wani irin rayuwar aure kake da macen dake gudunka har cutuwa ta shiga tsakaninku haka mai tsanani mugun raini ya shiga tsakaninku har ya kaika ga neman afka mata da tsiya ya kasance ka fad'a kan wace ba ita ba?"
Dubansa ya kai kan matar tasa dake kukan ita ma cike da dana sani ya furta" Anyi haka? Mijinki ya zo maki kin fito da suturar da tayi kamanceceniya da ta baiwar Allahn nan? Idan waje ya ga kin nufa ina kika lab'e masa ya fito waje nemanki? Kina ganni ya aikata haka baki katse masa hanzari ba ko baki gani ba?"
Fashewa tayi da kuka tana k'ara sada kanta muryarta na rawa ta ce" Allah ya huci zuciyarka a yi mana afuwa, a gafarta mana, a ji k'anmu, tabbas hakan ya faru daidai da abinda ya fad'a, kuma a lokacin da na zo fita lab'ewa na yi dan ina jin haushinsa ya hana min wasu kud'ad'e, dan ina so yana fita na koma na d'auka domin mun jima muna gaba tsakaninmu sakamakon mahaifiyarsa ta nunan cewa kar na yarda ya yi yan mata ko ya yi tarayya da 'ya'yan turawa a waje shi kuwa yayi budurwa shine ni kuwa nake nuna masa fushina ta hanyar hana masa abinda yake buk'atar."
Sai kuma ta k'ara sadda kanta tana kukan da na sani da tarin nadama.
Kansa yake girgizawa ya ma rasa me zai ce? A hankali ya furta" Ga irinta nan, ga irinta nan, kin yiwa sarakuwarki muguwar hud'ubar ita ma kar a mata kishiya ga inda abin ya kaiki, lalle ke ba uwa ta gari bace, ke ba mata ta gari bace sannan ke ba shugaba ta gari bace, tabbas kema hukunci zai hau kanki domin ba zan iya ci gaba da zama da ke a matsayin matata ta aure ba."
Baki d'ayansu a zabure suke kallonsa sai a lokacin SHAHEED yayi gyaran murya yana kallonsa ya furta" Allah ya huci zuciyarka, Allah ya ja da zamaninka tuba muke."
Baki d'aya suka ringa maimaitawa banda su NAJEEBA.
Kansa ya k'ara sadawa ya shiga fadin" Tabbas wannan lamari idan ma da ganganci a ciki to fa zanen k'addara ce, abin ne ya zo a harhad'e, shi ga abinda ya fitar da shi daga d'akinsa ita ma ga irin lokacin da ta kai tare da yan uwanta suna shashanci maimakun su kasance a cikin bautar ubangiji!"
Sasautawa yayi ya kuma d'auka da cewa" Tir da matar dake gudun shinfid'ar mijinta, tabas kina cikin tsinuwar ubangiji sannan kina da naki kason a cikin wannan lamari."
Dubansa ya maida wajen yarima ya kausasa muryarsa ya furta" Tir da namijin da ba zai iya rige arzizimun wandonsa a lokacind a fitinarsa ke harbinsa ba!"
Sai kuma ya maida dubansa wajen Gimbiya ya sasauta muryarsa ya furta" Kaico ga uwar da zata ringa shinfid'a hanyoyin b'araka a cikin ahalinta, domin kuwa wannan uwa ta d'auko hanyar tarwatsa iyalanta da al'uma mai yawa, dan kuwa mu dukanmu muna samun tarbiya ne daga iyayenmu, daga bakin lokacin da aka samu gurb'attaciyar tarbiya lamarin b'atanci zai yawaita a cikin al'umah."
Sassauta muryarsa yayi yana kallon sarki ya furta" Rud'ani, tashin hankali ya hana min kallonsu a cikin idannuwa, sai dai ya zama dole zamu hau wata shari'ar a yau a wajen nan dan danne wata b'arakar, amar yanda na fad'a cewar a duniya baki d'aya babu mumunan sirrin da fitarsa ke haifar da mugayen sakamako irin sirin masu mulki da kuma manyan malamai da masu iko,
akan d'auki hakan da fuska biyu, masu d'aukarsa da mummunar fuska ta hanyar kwaikwaya sukan yi yawa a cikin duniya baki d'aya, k'alilan ne ke yi masa kyakyawan fahimta har su gane b'atancinsa."
Kayan ta saka jikinta a mace suka fito tare.
K'arasawa tayi ita ma ta zauna ta d'ora kanta gefen wuyan Ummu
Muryarta a sanyaye ta ce" Ummu, kiyi magana mana, dan Allah ki ce wani abu mana."
Suma hawayen suka ringa sharewa shi kuwa yana kallonsu.
Sun d'auki kamar minti goma a haka kafin a hankali ta bud'a bakinta, hawaye ne wasu ke korar wasu cikin disashiyar muryarta ta furta" Dama me kuke jira da rayuwata? Kun manta wacece mahaifiyata? Yanzu haka idan kuka je tudun jamus layi na biyu babbar k'ofa mai ruwan blue gidanta ne, zaune take tana amsar kud'in wannan."
"Ki yi min shiru!" Ya bud'a bakinsa tun d'azun ya fad'a da wata murya ta tsawa wace ta saka du suka rintse idannuwansu suka sada kawunansu
Muryarsa ya kuma bud'awa yana cijewa yace" ku tashi baki d'ayanku mu fita!"
Da sauri Najeeba ta d'ago tana kallonsa, sai dai ba damar yin magana domin har ya juya ya fara fita.
Zahrau kam bata da katab'us, baki d'aya duniyar ce ta yi mata zafi ta rasa wani tunani zata yi da irin wannan lamari, aman tsawatarwar daya yiwa ummu ta sakata jin dama dama domin idan har haka zata ringa fad'i idan bakinta ya bud'e tana iya idasa halaka masu tunani su yi ta kuka.
Kamata suka yi ta mik'e da k'yar tana rintse idannuwanta kafin ta sauko.
Kamata suka yi a hankali tana tafiya suka fito domin basu san inda zai kaisu ba, su kuwa basu isa su k'i fitowar ba.
Irin yanda suka ga duk mutane ne a zazaune kama daga Sarkin Agadez, na damagaram, Gimbiyoyin, yarima da matarsa sai du suka ji hankalinsu ya k'ara tashi.
A hankali suka k'arasa da niyyar zaunar da ita a kasa, sarkin garin Agadez dake kallonsu ne kamar zai fashe da kuka shi kam ko rawanin babu a kansa yau an yi abinda ya cujewa buzu nad'i ya nuna masu doguwar kujerar dake ajiye."
Nufar wajen suka yi suka zaunar da ita kafin su zauna kusa da ita sosai a jikinta.
Najeeba irin kallon da take bin yarima da mahaifiyarsa da shi irin kallon nan ne wanda zaka ji kamar ka kashe mutun.
Yayi d'agowar kansa ya fi a k'irga sai zai bud'i baki sai ya kasa hakan ya saka Gimbiya saurin zamowa kasa ta had'e hannayenta tana kallonsa muryarta na rawa ta furta" dan girman Allah a rufa mana asiri, kar ku manta yarima shine mai jiran gado, sirrinsa ya fita tamkar sirrin baki d'aya gidan nan ne zai fita, Allah ya huci zuciyarka a rufawa yarima asiri a gafarta masa."
Tayi gaggawar juyar da kanta wajen SHAHEED ta d'an k'ara rarafawa hannayenta a had'e ta ci gaba da fadin" Ku rufa mana asiri, wannan sirri namu ne baki d'aya, dan girman Allah ku rufa mana asiri."
Du wani motsin kowa yana hakimce ne yana bi da kallo, bai furta ko A ba.
Kansa dake kasa ya dago, irin kukan da yake sai ya baiwa mutun tausayi.
Da sauro ya rarrafa ya nufi wajenta hakan ya sa sarki sakar masa tsawar da ta saka bai idasa idasawa har inda take ba aman ya ja daga d'an nesa.
Hannayensa ya had'e ya kara duk'awa sosai yana ta kuka kamar zai mutu yace" Dan girman Allah ki yafe min wannan lamari da na aikata maki, na rantse maki da Allah ni ba mazinaci bane
na je d'akin iyalina ne ta fito ta bar min d'akin sai na biyo bayanta a tunanina inda kike tsaye itace a tsaye domin idannuwana sun rufe, satina biyu kennan tana guje min a shinfid'ata, zaki ga na rufe maki ido da bakinki ba dan komai ba sai dan sannin tana iya k'wala min ihu ta tara min jama'a ni kuwa na yi alk'awarin a daren sai ta bani hakk'ina, ban san cewa ba da ita nake mu'amala ba sai da na kai ga shiga wajen da ba nawa ba, wallahi wallahi ni ba mazinaci bane, sannan ba mai afkawa mutane bane, na kasance ina koyi da halayen nagartatun mutane dan na kasance nagartace,
ban tab'a aikata zina ba ko a lokacin da bani da aure, dan girman Allah ki yafe min wannan b'arna da na aikatawa rayuwarki sannan na aikatawa rayuwata, ki maka ni kotu a yanke min hukunci daidai da laifina ko ki kaini kotun musulunci a yanke min hukuncin jifa domin ba zan iya rintsa ido da hak'inki irin haka a kaina ba."
Mahaifiyarsa ce ta fashe da kuka mai tsanani.
Da sauri ya juya ya k'arasa kusa da SHAHEED ya duk'a ya kama k'afafuwansa yana gunsheken kuka ya shiga fadin" Dan Allah yaya ka saka baki ta yafe min, ka saka baki ta gafarta min kar abin nan ya tab'a d'iyan d'iyana, ka ga wannan dake zaune zata iya maimaita abinda ya faru tsakanina da ita kafin ta baro d'akina, hakan yasa na biyota da sauri ban san inda ta lab'e min ba na fito da gudu ina nemanta sannan itama wando ne a jikinta da rigar baci na rufe bakinta da hanuna da idanuwanta dan kar ta min ihu ko ta fad'a min abinda zai fitar min da son zuwa gareta a raina hakan ya sa na afka mata, ba zan iya fahimtar ba da matata nake ciki ba, hankalina ya gama tafia burina na samu nutsuwa."
Gannin ya k'ura masa firgitatun idanuwan nan nasa masu matuk'ar abin tsoro ya saka shi sakinsa ya juya wajen mahaifinsa ya karasa ya kama k'afarsa.
Kafin ya fara magana ya hamb'are shi da k'afar tasa hakan yasa ya fad'i gefe aman bai gaza ba ya kuma tashi ya kara ruk'unk'ume k'afar tasa yana wani irin kuka murya a cakule ya furta"BABA."
Sarki ya saka k'afarsa yana kiciniyar kuma hamb'are shi aman ya gaza dan baki d'aya jikinsa yayi sanyi lamarin ya shige shi a lokacin da bai shiryawa hakan ba.
Muryarsa ya bud'a a birkice ya furta" Inna lillahi wa'ina ilaihi raj'une."
Innalilahi wa'ina ilaihi raj'une! Sai kawai muryarsa ta shiga rawa sai kuka ya k'wace masa, hakan ya saka SHAHEED saurin rintse idanuwansa ya sadda kansa.
Muryarsa na rawa ya shiga furta" Lalle kana wasa da adininka, kana wasa da ibadunka, idan kuwa ba haka ba kaima k'addararka mai tsauri ce domin kamar yanda ka fad'a saina hukuntaka! Wani irin rayuwar aure kake da macen dake gudunka har cutuwa ta shiga tsakaninku haka mai tsanani mugun raini ya shiga tsakaninku har ya kaika ga neman afka mata da tsiya ya kasance ka fad'a kan wace ba ita ba?"
Dubansa ya kai kan matar tasa dake kukan ita ma cike da dana sani ya furta" Anyi haka? Mijinki ya zo maki kin fito da suturar da tayi kamanceceniya da ta baiwar Allahn nan? Idan waje ya ga kin nufa ina kika lab'e masa ya fito waje nemanki? Kina ganni ya aikata haka baki katse masa hanzari ba ko baki gani ba?"
Fashewa tayi da kuka tana k'ara sada kanta muryarta na rawa ta ce" Allah ya huci zuciyarka a yi mana afuwa, a gafarta mana, a ji k'anmu, tabbas hakan ya faru daidai da abinda ya fad'a, kuma a lokacin da na zo fita lab'ewa na yi dan ina jin haushinsa ya hana min wasu kud'ad'e, dan ina so yana fita na koma na d'auka domin mun jima muna gaba tsakaninmu sakamakon mahaifiyarsa ta nunan cewa kar na yarda ya yi yan mata ko ya yi tarayya da 'ya'yan turawa a waje shi kuwa yayi budurwa shine ni kuwa nake nuna masa fushina ta hanyar hana masa abinda yake buk'atar."
Sai kuma ta k'ara sadda kanta tana kukan da na sani da tarin nadama.
Kansa yake girgizawa ya ma rasa me zai ce? A hankali ya furta" Ga irinta nan, ga irinta nan, kin yiwa sarakuwarki muguwar hud'ubar ita ma kar a mata kishiya ga inda abin ya kaiki, lalle ke ba uwa ta gari bace, ke ba mata ta gari bace sannan ke ba shugaba ta gari bace, tabbas kema hukunci zai hau kanki domin ba zan iya ci gaba da zama da ke a matsayin matata ta aure ba."
Baki d'ayansu a zabure suke kallonsa sai a lokacin SHAHEED yayi gyaran murya yana kallonsa ya furta" Allah ya huci zuciyarka, Allah ya ja da zamaninka tuba muke."
Baki d'aya suka ringa maimaitawa banda su NAJEEBA.
Kansa ya k'ara sadawa ya shiga fadin" Tabbas wannan lamari idan ma da ganganci a ciki to fa zanen k'addara ce, abin ne ya zo a harhad'e, shi ga abinda ya fitar da shi daga d'akinsa ita ma ga irin lokacin da ta kai tare da yan uwanta suna shashanci maimakun su kasance a cikin bautar ubangiji!"
Sasautawa yayi ya kuma d'auka da cewa" Tir da matar dake gudun shinfid'ar mijinta, tabas kina cikin tsinuwar ubangiji sannan kina da naki kason a cikin wannan lamari."
Dubansa ya maida wajen yarima ya kausasa muryarsa ya furta" Tir da namijin da ba zai iya rige arzizimun wandonsa a lokacind a fitinarsa ke harbinsa ba!"
Sai kuma ya maida dubansa wajen Gimbiya ya sasauta muryarsa ya furta" Kaico ga uwar da zata ringa shinfid'a hanyoyin b'araka a cikin ahalinta, domin kuwa wannan uwa ta d'auko hanyar tarwatsa iyalanta da al'uma mai yawa, dan kuwa mu dukanmu muna samun tarbiya ne daga iyayenmu, daga bakin lokacin da aka samu gurb'attaciyar tarbiya lamarin b'atanci zai yawaita a cikin al'umah."
Sassauta muryarsa yayi yana kallon sarki ya furta" Rud'ani, tashin hankali ya hana min kallonsu a cikin idannuwa, sai dai ya zama dole zamu hau wata shari'ar a yau a wajen nan dan danne wata b'arakar, amar yanda na fad'a cewar a duniya baki d'aya babu mumunan sirrin da fitarsa ke haifar da mugayen sakamako irin sirin masu mulki da kuma manyan malamai da masu iko,
akan d'auki hakan da fuska biyu, masu d'aukarsa da mummunar fuska ta hanyar kwaikwaya sukan yi yawa a cikin duniya baki d'aya, k'alilan ne ke yi masa kyakyawan fahimta har su gane b'atancinsa."