Sashe 91
Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Karasawa ta yi sosai kusa da shi tana dan jijiga jikinta, irin ga mata an batawa mata rai ta ce" eh mana, ba uwar NAJEEBA bace? A kan me zata zo.nan ta tare ko yar uwar BILKISSU ce? Ko kuwa dan kai take zaune?"
Idannuwa baki daya UMMU ta zaro daga wajen diner da suke zaune ita da Ammi , domin tun fitowarta Ammi ke zaune da ita tana tausarta, baki daya hankulansu ne ya dawo, irin rashin kunyar da matarsa ke tatawa ta saka UMMU zaro idannuwanta cike da mamaki
Abih ya ce" dama haka ne, dama ace zaman da take a nan nawa ne? Ke da na fi kowa farin cikin hakan, da ace zata kuma dubana bayan rashin adalci irin nawa da na yi farin cikin hakan na godewa Allah"
Yana gama fada gaba ya yi ya barta nan tsaye, maimakun ya nemi wajen su UMMUN sai ya bar gidan baki daya
Kwata kwata hankalinsa a tashe zuciyarsa bata da nutsuwa
Tunda ta fito daga wankan nan wanda ta ji dadinsa fiye da na dazu ta zauna ta saka pizzar da Zahrau ta kawo mata mai zafin gaske wace aka sarafata da naman kaza
Sai da ta koshi sannan ta kuma mikewa ta koma bakin gadon da Zahrau ke zaune tana kunce kitson da ala fara yi mata sannan ta mika mata abin kitson ta sauaka kasa ita kuwa ta fara kunce mata a hankali,
Basu yiwa junna magana ba har sai da ta gama mata ta caje kan sosai sannan ta raba shi gida uku cen saman ta fitar da kadan na tsakiya sai ma karshe ta dadaure kafin ta fara tsagawa a hankali ta kuma yiwa na gaban gida gida sannan ta fara daukan wani irin kananen kitso masu kwana kwana da shiga cikin junna sannan har karshe take kitse kitson duda irin yanda bata jin karfi sosai a jikinta aman ta ci burin sauke kitson a kan har uwarta
A hankali Zahrau dake ta harhada yanda zata bilo mata ta ce" tsoho ne?"
Najeeba da sarai ta san wa take nufi aman sai ta kasa bata amsa
Zahrau ta yi murmushi ta ce" matsalarsa dai farinsa da kuma sarautarsa ko?"
Najeeba ta sauke ajiyar zuciya, a hankali kamaninsa suke dawo mata , da sauri ta saki ajiyar zuciyar da ta kwace sakamakon irin yanda kamaninsa suka kawatu a idannuwanta
Wani murmushin Zahrau ta yi, domin a rubuce sai dai ta rubuta labarin kanwar tata ta baiwa wani tsabar yanda ko da ido ta yi magana take gane gaskiyar ciki da kuma wanda ta fada dai ne
A sanyahe ta furta" sai kike ce min na yawaita shiru a kan yawan magana, nan kika nuna min daga mijin da na aura har matansa kar na zake wajen buda bakina ina magangannun da ni kaina zasu gundureni domin kuwa a irin haka ina iya bada kofar da za'a gane raunina, tashin hankalina, sakarcina, jin tsorona"
Najeeba ta ci gaba da kitse gashin Zahrau, itama Zahraun sai ta yi shirun tana sauraronta dan kuwa ta san kitson nan ba na karewar yanzu yanzu bane
Sai cen kamar bata wajen, kamar ba zata tanka ba ta ce" Ban taba shiga halin firgici da tashin hankalin da na shiga ba,
Dan jan iska ta yi ta ci gaba da fadin" just ki kwatanta abin a gabanki, mutumen da tun bana biyewa maganarsa har ta kai min buga wasa daga ni sai shi,
Lebenta na kasa ta cije da hakoranta na sama kafin ta ci gaba da fadin" ya yawaita yi min tambaya a kan gidan nan, sai na nuna masa ni ban san gidan ba, ban san kowa ba, karshe na furta masa ni fa bai min ba"
Tsagawa ta yi da dan karfi har Zahrau na fadin" Aush"
Najeeba ta furta" Du a kan me ya min basaja yake hira da ni? A kan me ya ringa yi min tsmbayoyin da suka shafe shi? A kan me ya ringa hakuri da fadana? A kan me ya ci gaba da janyoni jikinsa ina fadin maganar da ta raya min a kansa?"
Sai da ta ja numfashi ta sauke , irin abu ya dake kan nan ta ce" sai kawai na ganshi a lokacin da ya shirya wulakanta ni shi ne a gabana da kamaninsa da komai sai dai fuskarsa na dauke sa kallon tsanar nan da ya zamo ayar tambaya a wajena!"
"Kun ban amsar hasashenku, sai dai zan kuma yi maki wata tambaya Aunty Zahrau, kasancewarsa baban mutumen dake mu'amala da mutane kala daban daban, har ya kasance ya iya basaja ya shiga gari ya yi lamuransa, shin bai taba sannin menene halayar yan matan zamani hade da samarin zamani ba ko kuwa yana nufin du yan matan yanzun ba soyaya ce suke yi da samarinsu ba aa zubar da mutuncinsu ne suke?, kina so ki ce min Aunty ya taba kamani da namiji turmi da tabarya ne ya saka shi wareni daban a cikin yan uwana ya sako lamarin tsana a tsakanina da shi? Ko tsabar rashin yancin kai ne zai saka matarsa marar tarbiya du haduwata da ita ko yan uwana da ita tun bana kulawa har ya kai kimarta da shakunta suka zube a idannuwa sakamakon mamakin kalar fatata da ta yan uwana da jifanmu da kalmar y'ayan talakawa ya saka har ta kaini da daga hannuna na fara jin dadin sauke iskancina a kan fuskarta shikenan mu ba zamu iya ramawa ba dan bamu da yanci? Shi mutun idan ba sarki bane shikenan sai ya zama talaka? Anya kuwa ta san menene talaka? Ba narar arziki bane talaka, mai mataciyar zuciya shine talaka! Aunty kina son ce min dan muna samun matsala da sakarya nunar ranar matarsa ce ya tsane ni ko me na tare masa ne ni? Na ga dai gidan nan wajen kawo kara ne, na tabata ban kasance wace aka fi kawo karana ko na rako gabansa dan shara'a ba a cikin garin DAMAGARAM! Ko shima so kike ki ce min shine dalili?, Aunty kadara cewar wai na bata rayuwar tawa, na zama fitinaniyar na gagari kowa a kasarnan, ina ruwansa da rayuwata da zai sakota gaba?"
Ta karashe maganar tana huci sosai ranta a matukar bace
Murmushi Zahrau ta kuma yi a hankali ta ce" NAJEEBA kitsa min sannu sannu dan Allah zafi fa"
Bata bata amsa ba, dan kuwa ta gama shaka mata ba dadi a ranta
Aunty Zahrau ta ce" Tambayata Najeeba a kanki shine: shin ke zaki tsara rayuwarki ne ba Allah ba?"
Najeeba ta ce" Me hakan ke nufi Zahrau, na isa na tsara rayuwata ne?"
Zahrau ta yi murmushi ta ce" Good, kin san da wannan shine kike haushi dan Allah ya wanzar da ikonsa a kanki? Daga ni har ke har Ummukulsum shin mun san rayuwa zata kasance haka a kanmu? Kin taba tunanowa cewar ni Zahrau zan auri sarki, sarkinma mahaifin ZINARIA kuma dansa namiji kwalin kwal ya tafka aikin da zai shigo zanen kadarar ahalina?, wa ya taba kawowa kansa cikinmu wace ta fi mu tsoron harkar maza take gudunsu tun karfinta hakan ne zai risketa? Me ta yi? *HAKURI* ta yi, tana kallon ikon Allah a lokacin da ta gane bata isa ta zana zanen rayuwarta ba"
Dan dago kanta ta yi tana kallon NAKEEBA ta ce" Kina nufin kina son nuna min cewar ke din daban kike a cikin halitun Allah da har kika kai matakin da zaki samu aure mai daraja mai mutunci dan kawai ya kasance mutumen da kike naki zato yana nasa kuma ya zama fari sannan yana da mata ciki harda wace haka kawai kuka tsani junna shikenan kin isa ki nuna ba'a maki adalci ba, Najeeba har ta kai da ke da bakinki musulma kike kina kallonsa dan kin rikice ki ce masa ya sake ki ko auri HUZAIFA?"
Najeeba dake kallon yannayin yanda Zahrau ke magana a sanyaye ta ce" Aman"
Zahrau ta ce" Aman me? Idan bamu isa ba, iyayenmu baasu isa ba, kina son ki nunan bakya tsoron Allah?"
"Aunty wani irin baku isa ba?" NAJEEBA ta fada tana dan nuno hannunta fuskarta na nuna yannayi na tashin hankali
Zahrau ta yi dan murmushi tana dan girgiza kanta ta ce" bamu isa ba NAJEEBA, meye bamu gwada ba? Meye bamu nuna maki ba? Ciki harda mamansa wace ta haife shi ta roke ki, ba wai dan kin fi sauran matansa daraja ko wani abin ba a wajen Allah, aa, sai dan tana yi maki so daya tak fisabililahi sannan ta rayu da son samun iri daga tsatson kawarta aminiyarta? Du kika watsa wannan, yanzun ta kai har kina kallon mutun mai daraja, da mutunci, mai nagarta, mutun wanda Allah ya daukaka, ke dan kin samu dama kike furta masa ka sake ni? Idan har da gaske kike ba zaki iya rayuwa da SHAHEED ba, gwara a yau mu samu Ammi a san yanda za'a yi, ki tashi kawai ki je ki sameta, ki fada mata gaskiyar cewa ke fa ba zaki iya zama da shi ba dan haka a sawake maki, kin san aure Najeeba idan ba so, ba yarda akoy matsala, idan har mace ta tsani namijin komai na iya faruwa, tunda har shi ya amince zai zauna da ke a gaban mahaifinki da yayanki da kuma mahaifiyarsa ke kuwa kin kasa hakura da hakan sai a dauki mataki, ya sake kin ki koma wajen Huzaifanki, mai yiwuwa shine abokin rayuwar taki aman sai kin bi ta kan Sultan kafin ki karasa hannunsa"
NAJEEBA kawai galala ta yi tana kallonta, 'ita? Ta tashi ta je ta samu Ammi da maganar nan? Sannan ita ta rabu da shi ta komawa Huzaifa? Ita kanta tana wannan furuci a kan Huzaifa ne a kan dalilin da bata sani ba, aman yau ko dan dan abinda take taka iya shegenta dan ta kwana da sannin a kilace yake da ya kwace me kuma ya mata saura?'
Kanta ta dukar muryarta a raunane ta ce" Aunty, shi din da ba so na yake ba fa?, ki duba ki ga wai ni ya cewa baya son bak'a, kuma ya auri Nadia Aunty NADIA fa?"
Idannuwa baki daya UMMU ta zaro daga wajen diner da suke zaune ita da Ammi , domin tun fitowarta Ammi ke zaune da ita tana tausarta, baki daya hankulansu ne ya dawo, irin rashin kunyar da matarsa ke tatawa ta saka UMMU zaro idannuwanta cike da mamaki
Abih ya ce" dama haka ne, dama ace zaman da take a nan nawa ne? Ke da na fi kowa farin cikin hakan, da ace zata kuma dubana bayan rashin adalci irin nawa da na yi farin cikin hakan na godewa Allah"
Yana gama fada gaba ya yi ya barta nan tsaye, maimakun ya nemi wajen su UMMUN sai ya bar gidan baki daya
Kwata kwata hankalinsa a tashe zuciyarsa bata da nutsuwa
Tunda ta fito daga wankan nan wanda ta ji dadinsa fiye da na dazu ta zauna ta saka pizzar da Zahrau ta kawo mata mai zafin gaske wace aka sarafata da naman kaza
Sai da ta koshi sannan ta kuma mikewa ta koma bakin gadon da Zahrau ke zaune tana kunce kitson da ala fara yi mata sannan ta mika mata abin kitson ta sauaka kasa ita kuwa ta fara kunce mata a hankali,
Basu yiwa junna magana ba har sai da ta gama mata ta caje kan sosai sannan ta raba shi gida uku cen saman ta fitar da kadan na tsakiya sai ma karshe ta dadaure kafin ta fara tsagawa a hankali ta kuma yiwa na gaban gida gida sannan ta fara daukan wani irin kananen kitso masu kwana kwana da shiga cikin junna sannan har karshe take kitse kitson duda irin yanda bata jin karfi sosai a jikinta aman ta ci burin sauke kitson a kan har uwarta
A hankali Zahrau dake ta harhada yanda zata bilo mata ta ce" tsoho ne?"
Najeeba da sarai ta san wa take nufi aman sai ta kasa bata amsa
Zahrau ta yi murmushi ta ce" matsalarsa dai farinsa da kuma sarautarsa ko?"
Najeeba ta sauke ajiyar zuciya, a hankali kamaninsa suke dawo mata , da sauri ta saki ajiyar zuciyar da ta kwace sakamakon irin yanda kamaninsa suka kawatu a idannuwanta
Wani murmushin Zahrau ta yi, domin a rubuce sai dai ta rubuta labarin kanwar tata ta baiwa wani tsabar yanda ko da ido ta yi magana take gane gaskiyar ciki da kuma wanda ta fada dai ne
A sanyahe ta furta" sai kike ce min na yawaita shiru a kan yawan magana, nan kika nuna min daga mijin da na aura har matansa kar na zake wajen buda bakina ina magangannun da ni kaina zasu gundureni domin kuwa a irin haka ina iya bada kofar da za'a gane raunina, tashin hankalina, sakarcina, jin tsorona"
Najeeba ta ci gaba da kitse gashin Zahrau, itama Zahraun sai ta yi shirun tana sauraronta dan kuwa ta san kitson nan ba na karewar yanzu yanzu bane
Sai cen kamar bata wajen, kamar ba zata tanka ba ta ce" Ban taba shiga halin firgici da tashin hankalin da na shiga ba,
Dan jan iska ta yi ta ci gaba da fadin" just ki kwatanta abin a gabanki, mutumen da tun bana biyewa maganarsa har ta kai min buga wasa daga ni sai shi,
Lebenta na kasa ta cije da hakoranta na sama kafin ta ci gaba da fadin" ya yawaita yi min tambaya a kan gidan nan, sai na nuna masa ni ban san gidan ba, ban san kowa ba, karshe na furta masa ni fa bai min ba"
Tsagawa ta yi da dan karfi har Zahrau na fadin" Aush"
Najeeba ta furta" Du a kan me ya min basaja yake hira da ni? A kan me ya ringa yi min tsmbayoyin da suka shafe shi? A kan me ya ringa hakuri da fadana? A kan me ya ci gaba da janyoni jikinsa ina fadin maganar da ta raya min a kansa?"
Sai da ta ja numfashi ta sauke , irin abu ya dake kan nan ta ce" sai kawai na ganshi a lokacin da ya shirya wulakanta ni shi ne a gabana da kamaninsa da komai sai dai fuskarsa na dauke sa kallon tsanar nan da ya zamo ayar tambaya a wajena!"
"Kun ban amsar hasashenku, sai dai zan kuma yi maki wata tambaya Aunty Zahrau, kasancewarsa baban mutumen dake mu'amala da mutane kala daban daban, har ya kasance ya iya basaja ya shiga gari ya yi lamuransa, shin bai taba sannin menene halayar yan matan zamani hade da samarin zamani ba ko kuwa yana nufin du yan matan yanzun ba soyaya ce suke yi da samarinsu ba aa zubar da mutuncinsu ne suke?, kina so ki ce min Aunty ya taba kamani da namiji turmi da tabarya ne ya saka shi wareni daban a cikin yan uwana ya sako lamarin tsana a tsakanina da shi? Ko tsabar rashin yancin kai ne zai saka matarsa marar tarbiya du haduwata da ita ko yan uwana da ita tun bana kulawa har ya kai kimarta da shakunta suka zube a idannuwa sakamakon mamakin kalar fatata da ta yan uwana da jifanmu da kalmar y'ayan talakawa ya saka har ta kaini da daga hannuna na fara jin dadin sauke iskancina a kan fuskarta shikenan mu ba zamu iya ramawa ba dan bamu da yanci? Shi mutun idan ba sarki bane shikenan sai ya zama talaka? Anya kuwa ta san menene talaka? Ba narar arziki bane talaka, mai mataciyar zuciya shine talaka! Aunty kina son ce min dan muna samun matsala da sakarya nunar ranar matarsa ce ya tsane ni ko me na tare masa ne ni? Na ga dai gidan nan wajen kawo kara ne, na tabata ban kasance wace aka fi kawo karana ko na rako gabansa dan shara'a ba a cikin garin DAMAGARAM! Ko shima so kike ki ce min shine dalili?, Aunty kadara cewar wai na bata rayuwar tawa, na zama fitinaniyar na gagari kowa a kasarnan, ina ruwansa da rayuwata da zai sakota gaba?"
Ta karashe maganar tana huci sosai ranta a matukar bace
Murmushi Zahrau ta kuma yi a hankali ta ce" NAJEEBA kitsa min sannu sannu dan Allah zafi fa"
Bata bata amsa ba, dan kuwa ta gama shaka mata ba dadi a ranta
Aunty Zahrau ta ce" Tambayata Najeeba a kanki shine: shin ke zaki tsara rayuwarki ne ba Allah ba?"
Najeeba ta ce" Me hakan ke nufi Zahrau, na isa na tsara rayuwata ne?"
Zahrau ta yi murmushi ta ce" Good, kin san da wannan shine kike haushi dan Allah ya wanzar da ikonsa a kanki? Daga ni har ke har Ummukulsum shin mun san rayuwa zata kasance haka a kanmu? Kin taba tunanowa cewar ni Zahrau zan auri sarki, sarkinma mahaifin ZINARIA kuma dansa namiji kwalin kwal ya tafka aikin da zai shigo zanen kadarar ahalina?, wa ya taba kawowa kansa cikinmu wace ta fi mu tsoron harkar maza take gudunsu tun karfinta hakan ne zai risketa? Me ta yi? *HAKURI* ta yi, tana kallon ikon Allah a lokacin da ta gane bata isa ta zana zanen rayuwarta ba"
Dan dago kanta ta yi tana kallon NAKEEBA ta ce" Kina nufin kina son nuna min cewar ke din daban kike a cikin halitun Allah da har kika kai matakin da zaki samu aure mai daraja mai mutunci dan kawai ya kasance mutumen da kike naki zato yana nasa kuma ya zama fari sannan yana da mata ciki harda wace haka kawai kuka tsani junna shikenan kin isa ki nuna ba'a maki adalci ba, Najeeba har ta kai da ke da bakinki musulma kike kina kallonsa dan kin rikice ki ce masa ya sake ki ko auri HUZAIFA?"
Najeeba dake kallon yannayin yanda Zahrau ke magana a sanyaye ta ce" Aman"
Zahrau ta ce" Aman me? Idan bamu isa ba, iyayenmu baasu isa ba, kina son ki nunan bakya tsoron Allah?"
"Aunty wani irin baku isa ba?" NAJEEBA ta fada tana dan nuno hannunta fuskarta na nuna yannayi na tashin hankali
Zahrau ta yi dan murmushi tana dan girgiza kanta ta ce" bamu isa ba NAJEEBA, meye bamu gwada ba? Meye bamu nuna maki ba? Ciki harda mamansa wace ta haife shi ta roke ki, ba wai dan kin fi sauran matansa daraja ko wani abin ba a wajen Allah, aa, sai dan tana yi maki so daya tak fisabililahi sannan ta rayu da son samun iri daga tsatson kawarta aminiyarta? Du kika watsa wannan, yanzun ta kai har kina kallon mutun mai daraja, da mutunci, mai nagarta, mutun wanda Allah ya daukaka, ke dan kin samu dama kike furta masa ka sake ni? Idan har da gaske kike ba zaki iya rayuwa da SHAHEED ba, gwara a yau mu samu Ammi a san yanda za'a yi, ki tashi kawai ki je ki sameta, ki fada mata gaskiyar cewa ke fa ba zaki iya zama da shi ba dan haka a sawake maki, kin san aure Najeeba idan ba so, ba yarda akoy matsala, idan har mace ta tsani namijin komai na iya faruwa, tunda har shi ya amince zai zauna da ke a gaban mahaifinki da yayanki da kuma mahaifiyarsa ke kuwa kin kasa hakura da hakan sai a dauki mataki, ya sake kin ki koma wajen Huzaifanki, mai yiwuwa shine abokin rayuwar taki aman sai kin bi ta kan Sultan kafin ki karasa hannunsa"
NAJEEBA kawai galala ta yi tana kallonta, 'ita? Ta tashi ta je ta samu Ammi da maganar nan? Sannan ita ta rabu da shi ta komawa Huzaifa? Ita kanta tana wannan furuci a kan Huzaifa ne a kan dalilin da bata sani ba, aman yau ko dan dan abinda take taka iya shegenta dan ta kwana da sannin a kilace yake da ya kwace me kuma ya mata saura?'
Kanta ta dukar muryarta a raunane ta ce" Aunty, shi din da ba so na yake ba fa?, ki duba ki ga wai ni ya cewa baya son bak'a, kuma ya auri Nadia Aunty NADIA fa?"