Sashe 4
Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai da ya samu ya sauke ajiyar zuciya ya kai sau hudu kafin a hankali ya budi bakinsa ya ce"
🥺🥺🥺🥺🥺🥺🥺🥺
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
3
Kafin ta ankara ta cire lafiyayiya, kwontaciya, farar fatar matar sarki da wani gigitacen mari wanda hakan ya saka baki daya wajen hankalinsu ya dawo kansu
Yaya DAYABU ne ya zabura ya mike tsaye sai dai hararan da Sarki ya Zabga masa ya saka shi komawa ya zauna jikinsa na rawa hankalinsa tashe
Kai Gimbiya ke jujuyawa a hankali ta saci kallon d'anta, kuma sarkin garinta
Ganni ta yi idannuwansa lumshe tamkar wanda bai ga abinda ya faru ba
Dubanta ta mayar kan yar dan uwanta, mafi soyuwa a cikin zuciyarta sannan wace ta fi horawa a kan laifukanta
Cikin tafiar takama da ta zame mata jiki ba da gangan take yi ba ta tunkaro wajen da suke tsaye wanda sai da NAJEEBA ta yi marin ne kuma baki daya jikinta ya kara kwasar rawa ta shiga jin kamar zata kurma ihu, sai kawai ta shiga yarfe hannayen nata tana matso kwalar da ta yi mata tawaye ta ki zuwa a irin wannan lokacin
Tana zuwa tsayawa ta yi tana kallonsu, idan ta kalli wannan sai kuma ta kalli wancen
Muryarta ta buda, kamar wace idan ta fito zaka ji wani tashin hankali da kururuwa, aa sai muryar ta fito da wani irin sanyi sannan tana kalkaltu irin na larabawa ta ce" Ya salam, yayarki kika mara?
NAJEEBA ta ringa matso kwallah aman ina kukan ya ki zuwa dan ta san tana yin kuka yanzu zata manta fadan ta dawo rarashinta domin ita kanta ta san uwar tasu na matukar son ta
A hankali lebenta na rawa ta ce" *ANMY* (wato mama), ta taba martabar iyayena ne
Gimbiya ta kalli Zulaihat dake tsaye dafe da kuncinta, a hankali ta ce" rama
Sarki dake jin dukan abinda ke faruwa ya kara dan muzkutawa yana sauraronsu
Kamar jira take ba wani kauce kauce itama ta daga hannunta ta dauke NAJEEBA da mari
Karar marin nan shi ya saka kanwar NAJEEBA mai bi mata wato Khairat zabura tana ruko idannuwanta da niyar tashi
Da sauri DAYABU ya saka hannunsa ya mayar da ita ya ringa yiwa kannen nasa gargadin kar wanda ya tashi, ya kara sada kansa kasa
Tun da ta mareta ido kawai ta rintse tana jin yanda jijiyar kanta ke harbawa
Da mamaki ta buda idannuwan nata ta sauke a kan hannun Zulaihat, gata dai farar mace, kana kallonta ka ga laushi sai dai hannunta wani irin tauri ne da shi kamar dutse wanda ba komai ya janyo haka ba sai mayukan bleating din da take shafawa fatarta dan karin haske a kan nata kamar yanda wasu buzayen ke yi ya hadasa mata taurin tafin hannu kamar mai kwaba suminti da hannun nata
Da sauri kuma ta maida dubanta wajen Gimbiya wace itama karan marin ya sakata saurin rintse ido da jin wani irin ciwo da daci a ranta, sannan mamakin rashin kunyar Zulaihat ya darsu a cikin zuciyarta, haka kawai take ayanna Zulaihat ba kara? Ba zaki yafe ba ko dan ni?
Juyawa ta yi bata kuma kallon fuskar NAJEEBA ba dan ta san zuciyarta zata karye ne
NAJEEBA kuwa kallon tsana ta bi Zulaihat da shi wace ke binta itama da kallon tsana harda na kyankyami kafin ta motsa labanta ta ce" kin mari *SHAHID* kuma sai na rama a kan *ALI*!
ido ta ruruko tana kallonta sai dai ba damar kuma tofawa da sauri ta juya ta fita tana jin zuciyarta kamar zata bale , ta yi rantsuwa ta maya ba'a yi yar talakawan da zata zagar mata miji da kuma yarima ba! Sai ta ga bayan wannan tsinaniyar bakar yarinyar mai bakar zuciya!
Kusa da yayanta ta je ta zauna wanda ke bin kuncinta da kallo zuciyarsa na karyewa, walahi baya son abinda zai taba masa kannensa, ko dan ya kasance baba a cikin gidansu, ko dan du yawancinsu iyayensu na fita sunna kannanu ne su bar masa yar jarirai ya raina? Du cikinsu ba wanda uwarsa ta rufa shekara hudu da shi, da wuri take tafiarta inda za'a bar masa shi kuwa ya raina domin mahaifinsu mai tafiye tafiye ne, sunna da masu raino aman baya iya motsawa yana tare da su hakan ya sa yake masu soyaya daya tak tamkar mahaifinsu, gani yake yama fi mahaifin nasu son su domin baya tunanin da shine wata mace ta isa ta shiga tsakaninsa da su ba!
Sai da ta saisaita nutsuwarta daga tsayen da take kafin ta karasa gabansu ta aniya neman zama a kasa saman kafet din
Da wani irin sauri SARKI wato mai martaba ya zabura daga zaune a saman kujerar falon ta alfarmar da yake ya tashi tsaye, da wani irin sauri ya karasa ya saka hannunsa ya tare ta
A tare suka tarota da sauran y'ayan
Sai a lokacin kukan ya zo mata ta fashe da kula tana rike da hannun Gimbiya ta ce" ANMY a kasa kuma?
Irin yanda zuciyarsa ke bugawa gannin majaifiyarsa zata zauna kasa bayan shi yana sama ya saka shi lumshe idannuwansa
DAYABU dake rike da ita shiga ta gabanta ya ce"ANMY ki rufa mana asiri kar ki zauna a kasa
Itama fuskar ta kwabe, wanda sai a nan na gano kwabewar fuskar nan ta NAJEEBA tata ce,
A hankali ta ja shashekar kuka ta ce" ku barni mana, ku barni na zauna kasa nima ya zo ya saka min layar, ku barni ya zo ya mana tsakanin nima kar a je na cuce ku a zamantakewar yau da kulun
Kanta take girgizawa da sauri ta shige jikin Gimbiyar ta rukukumeta ta cusa kanta a kirjinta tana ta juya kanta tana nufin aa, aa
Gimbiya ta kara riketa da kyau a jikinta, ga hannunta na dama dake cikin na SARKI ga kuma DAYABU da ya koma gefen hagu shima ya riketa da kyau, ga sauran yaran du sun zagayeta kowane ya kama kunnensa ya rike
Idannuwanta lumshe ta ce" so kuke ku kashe min shi shima ya kasance bani da kowa? Ai gwara ku hade mu ku kashe sa8 ku huta ya ku y'ayana
Du kansu suke jujuyawa cike da dana sani
Gimbiya ta ce" yaya zaku kawo karar mahaifinku a cikin bainar jama'a? Koma me kuke tsoro shin baku yarda da Allah zai kare ku bane ko kun fi yarda da tozarcin? Yaya ina tashin tsakiyar dare ina rokan Allah ya raba ku da bakin duniya irin yanda kuka sha jinnin rigima aman kunna kara janyowa kunna hada kanku da su? Kai kuwa da na yi hannin ku tozarta mu sai ka nunan ai adalci aka nema ka je ka yi gaban kanka ka zaunar da yayana a gabanka ka bashi laya?
Da sauri NAJEEBA ta kara riketa ta ce" Anmy, Layar fa ba a cike take ba, ya zare abubuwa a cikinta
Da sauri ya kai dubansa keyarta da dan kwalinta ya zame ya fadi sai gashin kanta dake waje wanda yake daure da dan ribom a sama sama ya zubo sosai
Mamaki ne ya kama shi na yanda aka yi ta gane Alkur.anin ba a cike yake ba, ko wani ne ya fada mata?
Kai ina da wuya a cikin mutanensa wani ya fitar da sirrin, hasalima liman baba ne ya cire abinda ya cire a ciki daga baya kuma ya mayar da shi yanda yake , wanda sun yi haka ne daga shi sai shi sai Allahn dake kallonsu
Idannuwansa ya lumshe yana jin mamansa na tambayarsa wai gaske ba cikaken bane?
A hankali, a karon fari kennan da ya budi bakinsa tun farko cikin wata irin murya mai dadin sauraro da nitsar da firgitace ya ce" Na'am
Wata ajiyar zuciya ta saki a hankali ta janyo shi ta hade shi da NAJEEBA dake jikinta ta gefenta ta kuma janyo DAYABU ta dayan gefen ta hade su ta rungume su tsam a jikinta wanda hakan ya sa kwabrin hannunsa na gogan wajen wuyan NAJEEBA
Ajiyar zuciya ta ringa saukewa na samun nutsuwa kafin ta sake su
Juyawa ta yi da NAJEEBA rike a hannunta du ta yiwa sauran nuni da wajen zama
Baki dayansu a kasa suka zauna, Banda Sarki da ya koma kujerarsa ya lume ciki ya lumshe idannuwansa
A hankali ta ce" yaya zaku biye mata koma me take maku ku fitar da sirrin cikin gidanku waje? Yaya kuke so hankalinmu ya kwonta a yanzu da tsufa ke riskarmu na zamu iya tafia kowani lokaci mu barku bari na har abada bayan kuna kokarin lalata kanku?
Ko da gaskiyarka a lokacin da aka saka maka shi sai jijiyoyin jikinka arba'in sun tsinke
Shine kai da girmanka ka tashi ka yi ja gabar kannenka da ka san cewa ko me za'a yi idan dai fada ya tashi sai sun yi ka zo ka tsugunna aka saka masu layar fada? Wato baki dayanku ku mace ko ku lalace shikennan ko?
Kansa ya kara sadawa ya ce" Allah ya huci zuciyarki
Hannunta ta buga gefen kujerar ta ce" ba wannan na tambayeka malan ka bani bayanin uban me take maku da ya karfina ni ka fada min na magance maku shi?
Rintse ido sarki ya yi a ramsa kuwa fadi yake" subahannalah, itama zata fitan kennan?
DAYABU ya kara sada kansa ya ce" Anmy, tana zargin ko mu ke hada mata fitinar da take yawan samun matsala da Abih, tana tunanin ko zamu hadewa yarta kai ne mu cuce ta, yajin nan da ta yi ta dawo ne da abubuwan nan wa'inda suka birkita mana lisafi
Yan uwanta sun zo har gida da laya za'a saka mana iya mu aman banda ita, mune kawai za'aiwa shingen nan kuma ABIH na kallo bai hanna ba saima fadi da ya yi cewa a core duka, a cire fada, a saka mana iya na magani kar mu yi mata magani domin ya yarda da tarbiyar y'ayansa, bama bin boka bare malan
Anmy to idan itafa ta mana?
Sasauta muryarsa ya yi ya dago yana kallonta da idannuwansa da suka cika da kwallah ya ce" idan ta lalata rayuwar kanena fa?
🥺🥺🥺🥺🥺🥺🥺🥺
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
3
Kafin ta ankara ta cire lafiyayiya, kwontaciya, farar fatar matar sarki da wani gigitacen mari wanda hakan ya saka baki daya wajen hankalinsu ya dawo kansu
Yaya DAYABU ne ya zabura ya mike tsaye sai dai hararan da Sarki ya Zabga masa ya saka shi komawa ya zauna jikinsa na rawa hankalinsa tashe
Kai Gimbiya ke jujuyawa a hankali ta saci kallon d'anta, kuma sarkin garinta
Ganni ta yi idannuwansa lumshe tamkar wanda bai ga abinda ya faru ba
Dubanta ta mayar kan yar dan uwanta, mafi soyuwa a cikin zuciyarta sannan wace ta fi horawa a kan laifukanta
Cikin tafiar takama da ta zame mata jiki ba da gangan take yi ba ta tunkaro wajen da suke tsaye wanda sai da NAJEEBA ta yi marin ne kuma baki daya jikinta ya kara kwasar rawa ta shiga jin kamar zata kurma ihu, sai kawai ta shiga yarfe hannayen nata tana matso kwalar da ta yi mata tawaye ta ki zuwa a irin wannan lokacin
Tana zuwa tsayawa ta yi tana kallonsu, idan ta kalli wannan sai kuma ta kalli wancen
Muryarta ta buda, kamar wace idan ta fito zaka ji wani tashin hankali da kururuwa, aa sai muryar ta fito da wani irin sanyi sannan tana kalkaltu irin na larabawa ta ce" Ya salam, yayarki kika mara?
NAJEEBA ta ringa matso kwallah aman ina kukan ya ki zuwa dan ta san tana yin kuka yanzu zata manta fadan ta dawo rarashinta domin ita kanta ta san uwar tasu na matukar son ta
A hankali lebenta na rawa ta ce" *ANMY* (wato mama), ta taba martabar iyayena ne
Gimbiya ta kalli Zulaihat dake tsaye dafe da kuncinta, a hankali ta ce" rama
Sarki dake jin dukan abinda ke faruwa ya kara dan muzkutawa yana sauraronsu
Kamar jira take ba wani kauce kauce itama ta daga hannunta ta dauke NAJEEBA da mari
Karar marin nan shi ya saka kanwar NAJEEBA mai bi mata wato Khairat zabura tana ruko idannuwanta da niyar tashi
Da sauri DAYABU ya saka hannunsa ya mayar da ita ya ringa yiwa kannen nasa gargadin kar wanda ya tashi, ya kara sada kansa kasa
Tun da ta mareta ido kawai ta rintse tana jin yanda jijiyar kanta ke harbawa
Da mamaki ta buda idannuwan nata ta sauke a kan hannun Zulaihat, gata dai farar mace, kana kallonta ka ga laushi sai dai hannunta wani irin tauri ne da shi kamar dutse wanda ba komai ya janyo haka ba sai mayukan bleating din da take shafawa fatarta dan karin haske a kan nata kamar yanda wasu buzayen ke yi ya hadasa mata taurin tafin hannu kamar mai kwaba suminti da hannun nata
Da sauri kuma ta maida dubanta wajen Gimbiya wace itama karan marin ya sakata saurin rintse ido da jin wani irin ciwo da daci a ranta, sannan mamakin rashin kunyar Zulaihat ya darsu a cikin zuciyarta, haka kawai take ayanna Zulaihat ba kara? Ba zaki yafe ba ko dan ni?
Juyawa ta yi bata kuma kallon fuskar NAJEEBA ba dan ta san zuciyarta zata karye ne
NAJEEBA kuwa kallon tsana ta bi Zulaihat da shi wace ke binta itama da kallon tsana harda na kyankyami kafin ta motsa labanta ta ce" kin mari *SHAHID* kuma sai na rama a kan *ALI*!
ido ta ruruko tana kallonta sai dai ba damar kuma tofawa da sauri ta juya ta fita tana jin zuciyarta kamar zata bale , ta yi rantsuwa ta maya ba'a yi yar talakawan da zata zagar mata miji da kuma yarima ba! Sai ta ga bayan wannan tsinaniyar bakar yarinyar mai bakar zuciya!
Kusa da yayanta ta je ta zauna wanda ke bin kuncinta da kallo zuciyarsa na karyewa, walahi baya son abinda zai taba masa kannensa, ko dan ya kasance baba a cikin gidansu, ko dan du yawancinsu iyayensu na fita sunna kannanu ne su bar masa yar jarirai ya raina? Du cikinsu ba wanda uwarsa ta rufa shekara hudu da shi, da wuri take tafiarta inda za'a bar masa shi kuwa ya raina domin mahaifinsu mai tafiye tafiye ne, sunna da masu raino aman baya iya motsawa yana tare da su hakan ya sa yake masu soyaya daya tak tamkar mahaifinsu, gani yake yama fi mahaifin nasu son su domin baya tunanin da shine wata mace ta isa ta shiga tsakaninsa da su ba!
Sai da ta saisaita nutsuwarta daga tsayen da take kafin ta karasa gabansu ta aniya neman zama a kasa saman kafet din
Da wani irin sauri SARKI wato mai martaba ya zabura daga zaune a saman kujerar falon ta alfarmar da yake ya tashi tsaye, da wani irin sauri ya karasa ya saka hannunsa ya tare ta
A tare suka tarota da sauran y'ayan
Sai a lokacin kukan ya zo mata ta fashe da kula tana rike da hannun Gimbiya ta ce" ANMY a kasa kuma?
Irin yanda zuciyarsa ke bugawa gannin majaifiyarsa zata zauna kasa bayan shi yana sama ya saka shi lumshe idannuwansa
DAYABU dake rike da ita shiga ta gabanta ya ce"ANMY ki rufa mana asiri kar ki zauna a kasa
Itama fuskar ta kwabe, wanda sai a nan na gano kwabewar fuskar nan ta NAJEEBA tata ce,
A hankali ta ja shashekar kuka ta ce" ku barni mana, ku barni na zauna kasa nima ya zo ya saka min layar, ku barni ya zo ya mana tsakanin nima kar a je na cuce ku a zamantakewar yau da kulun
Kanta take girgizawa da sauri ta shige jikin Gimbiyar ta rukukumeta ta cusa kanta a kirjinta tana ta juya kanta tana nufin aa, aa
Gimbiya ta kara riketa da kyau a jikinta, ga hannunta na dama dake cikin na SARKI ga kuma DAYABU da ya koma gefen hagu shima ya riketa da kyau, ga sauran yaran du sun zagayeta kowane ya kama kunnensa ya rike
Idannuwanta lumshe ta ce" so kuke ku kashe min shi shima ya kasance bani da kowa? Ai gwara ku hade mu ku kashe sa8 ku huta ya ku y'ayana
Du kansu suke jujuyawa cike da dana sani
Gimbiya ta ce" yaya zaku kawo karar mahaifinku a cikin bainar jama'a? Koma me kuke tsoro shin baku yarda da Allah zai kare ku bane ko kun fi yarda da tozarcin? Yaya ina tashin tsakiyar dare ina rokan Allah ya raba ku da bakin duniya irin yanda kuka sha jinnin rigima aman kunna kara janyowa kunna hada kanku da su? Kai kuwa da na yi hannin ku tozarta mu sai ka nunan ai adalci aka nema ka je ka yi gaban kanka ka zaunar da yayana a gabanka ka bashi laya?
Da sauri NAJEEBA ta kara riketa ta ce" Anmy, Layar fa ba a cike take ba, ya zare abubuwa a cikinta
Da sauri ya kai dubansa keyarta da dan kwalinta ya zame ya fadi sai gashin kanta dake waje wanda yake daure da dan ribom a sama sama ya zubo sosai
Mamaki ne ya kama shi na yanda aka yi ta gane Alkur.anin ba a cike yake ba, ko wani ne ya fada mata?
Kai ina da wuya a cikin mutanensa wani ya fitar da sirrin, hasalima liman baba ne ya cire abinda ya cire a ciki daga baya kuma ya mayar da shi yanda yake , wanda sun yi haka ne daga shi sai shi sai Allahn dake kallonsu
Idannuwansa ya lumshe yana jin mamansa na tambayarsa wai gaske ba cikaken bane?
A hankali, a karon fari kennan da ya budi bakinsa tun farko cikin wata irin murya mai dadin sauraro da nitsar da firgitace ya ce" Na'am
Wata ajiyar zuciya ta saki a hankali ta janyo shi ta hade shi da NAJEEBA dake jikinta ta gefenta ta kuma janyo DAYABU ta dayan gefen ta hade su ta rungume su tsam a jikinta wanda hakan ya sa kwabrin hannunsa na gogan wajen wuyan NAJEEBA
Ajiyar zuciya ta ringa saukewa na samun nutsuwa kafin ta sake su
Juyawa ta yi da NAJEEBA rike a hannunta du ta yiwa sauran nuni da wajen zama
Baki dayansu a kasa suka zauna, Banda Sarki da ya koma kujerarsa ya lume ciki ya lumshe idannuwansa
A hankali ta ce" yaya zaku biye mata koma me take maku ku fitar da sirrin cikin gidanku waje? Yaya kuke so hankalinmu ya kwonta a yanzu da tsufa ke riskarmu na zamu iya tafia kowani lokaci mu barku bari na har abada bayan kuna kokarin lalata kanku?
Ko da gaskiyarka a lokacin da aka saka maka shi sai jijiyoyin jikinka arba'in sun tsinke
Shine kai da girmanka ka tashi ka yi ja gabar kannenka da ka san cewa ko me za'a yi idan dai fada ya tashi sai sun yi ka zo ka tsugunna aka saka masu layar fada? Wato baki dayanku ku mace ko ku lalace shikennan ko?
Kansa ya kara sadawa ya ce" Allah ya huci zuciyarki
Hannunta ta buga gefen kujerar ta ce" ba wannan na tambayeka malan ka bani bayanin uban me take maku da ya karfina ni ka fada min na magance maku shi?
Rintse ido sarki ya yi a ramsa kuwa fadi yake" subahannalah, itama zata fitan kennan?
DAYABU ya kara sada kansa ya ce" Anmy, tana zargin ko mu ke hada mata fitinar da take yawan samun matsala da Abih, tana tunanin ko zamu hadewa yarta kai ne mu cuce ta, yajin nan da ta yi ta dawo ne da abubuwan nan wa'inda suka birkita mana lisafi
Yan uwanta sun zo har gida da laya za'a saka mana iya mu aman banda ita, mune kawai za'aiwa shingen nan kuma ABIH na kallo bai hanna ba saima fadi da ya yi cewa a core duka, a cire fada, a saka mana iya na magani kar mu yi mata magani domin ya yarda da tarbiyar y'ayansa, bama bin boka bare malan
Anmy to idan itafa ta mana?
Sasauta muryarsa ya yi ya dago yana kallonta da idannuwansa da suka cika da kwallah ya ce" idan ta lalata rayuwar kanena fa?