Sashe 13
Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daya Zinaria ce da yar uwarta da abokanansu dake ta shigi da fici
Dayan kuwa idan baki sun shigo nan suke zama a amshi gaisuwa
Bangare bangaren gidajen kowa ya tara jama'arsa yana amsar gaisuwa
Sai yanke yanke ake ana sadaka, rasuwar dai taro na mamaki tamkar wani tsohon magidanci ne ya rasu
Babu wace ta koma gida, a nan bangaren suke kwana wajen Anmynsu wace ke shiga tsakaninsu su layu du su lalafe mata domin baki daya wayoyinsu ta karbe ta kashe dan ta lura wayar NAJEEBA bata daina kuka gashi ita kuwa ta jima tana son ta kasance da y'ayan nata haka
Iyayen daidaiku sun zo har masarauta sun yi gaisuwa, mahaifiyar NAJEEBA dake saudiya ta yi vidio call sai dai sam NAJEEBA ta ki amsarta, sai da Anmy suka gaisa
Yau akaiwa yarima adu'ar uku
Yau ne jama'a ta ringa ragewa tun bayan adu'ar
Kafin ake cewa azahar ta shigo kai ya kasance du sai na kusa wato na kud da kud
A yaune kuma jirgin mai martaba sarkin agadez ya sauka da abokannan tafiyarsa suka yi tataki da kansu dan zuwa gabatar da gaisuwa wa sirikinsa da kuma yarsa na rashin dansu daya cilo da sukai
An masu tarba irin ta bajinta
An sauke su a bangaren Mai martaba Sarki SHAHEED, ya sauke su tare da mutanensa na arziki su ABIH, su DAYABU, su liman Baba,
Dogarai kuwa sun cika ko'ina sai kai kawo suke sun tatare ko'ina
Cike da kamala ta mike ta kai dubanta wajen ZAHRAU, da UMMULKHAIR da UMMUKULSUM, da NAJEEBA
Cikin nutsuwa ta ce" ku tashi ku min rakiya mu gaishe da mahaifin ZINARIA
Mimikewa sukai yan matan reras , baki dayansu sanye suke da bakaken abayayoyi yan saudiya masu shegen kyau da tsari ga tsada
Wani sirrin kyau ne da y'ayan nan tamkar idan kana kallonsu kar ka daina
Bakin fatarsu irinsa ne ke wartar farar fats harma ta yi mangarin idan ta samu kalar nan ai sai yi
Ga najeeba dake anfani da roger cavalais, sannan sabululukanta na anfani tana hada kayanta ne da kanta ciki kuwa harda su kurkum da sabulun victago da zuma da su kankana da dai sauransu hakan ya saka fatarta ita kadaima sheki take tana haskawa, sai haskenta ya fi na sauran ya kasance bakin nata irin na American din nan ne mai kyan gaske
Ko yanzu da take zaman makokin bakinta baya rabo da dan jan bakin nan, hakama idannuwanta bata cire abin nan ba, gata da kallon kasa kasa sai ta lumshe idannuwan nata
Anmynsu ce gaba
Su kuwa sai sukai biyu a bayanta, biyu a bayan biyun wato sun jeru sunna wata irin tafia mai cike da kasaita idan ta ajiye kafafuwanta sai ta dauke su zahrau dake bayanta ke ajiye nasu, sannan su Najeeba su ajiye nasu
Jakadiya na tafe tana shelar fitowarsu hakan ya sa du wani bawa ko wanda Anmy ta girma ya ja ya tsaya ya sada kansa dan girmamawa ga uwar gidan marigayi sannan uwar mai martaba
Fuskarta sake take daga kanta a hankali sannan da dan murmushi tana amsa irin gaisuwar da ake ta jefo mata, da yawa cikin manyan samarin gidan sukan bi y'ayan dake bayanta da kallo, da yawa sun dauri niyar isar da sakonsu dan a kara kulla zumunci, wasun kuwa na masu kallon sha'awa da tsoro domin su din dai ba dai kyau ba sai dai masifa!
a haka har suka karasa wajen shigar
Dogaran kofar dake tsaitsaye da jakadiyoyin ne suka kwashi summa nasu kirarin da kawo mata gaisuwar da adu'ar Allah ya jikan yarima karami da fatan Allah ya jawo masu zama
Babar jakadiya, tsohuwa ce ta shiga ta duka ta sanar da isowarsu
Tana fitowa anmy ta shiga da bismillah sannan kanta a sade dan girmama sarkin garin agadez duda tana kyautata zaton ta girme shi domin shima ba wani tsoho bane
Saman kujera ta zauna kafin ta ja alkyabarta ta gyara
Baki dayansu kasa suka zazauna kusa da kafafuwan Anmy,
Tun da suka shigo ta lumshe idannuwanta sakamakon kanshin turaran nan dake matukar kasheta a duniya
Sunnan turaran *MUSKI-JAH* sakamakon jinsa da take a wajen wannan bawan Allah ya sakata nemansa a lokacin da suka fita waje a paris
A ranar baki daya tanadinta ta saka ta siyo turaran nan, tana bude shi ta ga wata yar karamar kwalba sannan ba'a cike ba dan ko rabin kwalbar bata kai ba aman kuma yakeda muguwar tsada mai rikitarwa
Daga ranar ta nemi waje ta ajiye maganar turaransa, yanzu abinda ta fi sakowa a gaba irin yanda yake saka tufafinsa
Tana son ta ji wai du suturarsa daya zata kai nawa? Ba dan komai take son gane wasu al'amura nasa ba sai dan ta gane shin gayunsa da sarautarsa na bagidaji ne ko ya waye? (Ji fa rigima)
A hankali ta dago da idannuwanta a lokacin da dogarin nan ke ta fadin" saraki sun amsa gaisuwarku jinnin MUTALAB, saraki sun ji dadin kulawarku .....
Bakinta ta tabe tana ayanna ko a ina mukai magana?
Idannuwanta ta sauke a fuskar mahaifinta wanda akaiwa sasaukan rawani
Irin yanda yake dan murza goshinsa ya sakata sakar masa murmushi domin kwarai ta fanr ya takura da rawanin nan ne
Dubanta ta maida wajen DAYABU, hararar da ya sakar mata ta sakata yi masa murmushi har hakoranta suka bayana domin ta san hararar baya wuce numbersa da wasu daga cikin samarinta zasu dama dan ta tabata zai sha kira domin akoy masu numbersa a cikinsu idan sun sha mata kai ta hada su da yayanta takan basu ba abinda ya shafeta
Kalle kallenta ya kai fuskar sarkin Gadez , a hankali ta bi wajen da ya kurawa ido
Zahrau ce ke kallon Dogarin dake ta zuba ta san tausaya masa take a cikin ranta, sai dai irin kuretan da ya yi da ido ya saka NAJEEBA sakin murmushi har tana dan dantse lebenta na kasa
Idannuwanta masu kale kale suka kaita wajen fuskarsa
Irin yanda sukai ido hudu ya sakata da saurin gaske ta sada kanta sakamakon kallon nan na tsana da ya wurga mata wanda ke sakata jin faduwar gaba da tambayar kanta shin me ta masa? Sam bata iya kallon cikin idannuwansa, dan bakinta ta murguda a kasan zuciyarta kuwa fadi take" wai shi hala dan daudu ne da yake saka kwali?
Kara bin fuskarta da ta sada ya yi da ido, lebensa dake cikin rawaninsa ya datse da hakorinsa na sama
A kasan zuciyarsa ya furta" wani rashin jin maganar kika shirya da ya saka ki sakin murmushi Majanune?
Dubansa ya maida wajen Dayabu, sai kuma ya lumshe idannuwansa yana ayanna ya zama wajibi a koya mata biyaya da bambancin sarkinta da yan iskanta! Irin yanda ta tsinke fuskar Zinaria da mari a gaban sarkinta ta yi rashin kunya mai tsauri!
Muryoyin dogarai da jakadiyoyin dake kofa na shaida karasowar Zinaria ya saka NAJEEBA kara janye kafamfafuwanta domin ita ta fi kusanta da hanya ta kuma tabata idan har ta shigo ta ganta a bakin hanyar nan zata baje tafiyarta ta yanda zata taka mata kafa ne ita kuwa ta kara mata na biyu a gaban ubanta!
Za ina tsalake ranakun posting idan har baku daukaka comment dinku ba😔
[1/20, 9:50 AM] Ummu Suhan😍: 🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
9
Cike da wata irin kasaita da alkyaba a jikinta ta sanyo kai, bayanta kuwa jakadiya ce, sai bayi mata uku du suka duduka sannan suka dukar da kawunansu kasa
A hankali ta ringa takawa har ta karasa kusa da Anmy ta samu waje saman luntsumemiyar kujerar dake nan ta zauna hakan ya kasance Zahrau na zaune kusa da kafarta ne
Sai da ta sada kanta a hankali ta gaishe da Anmy, sannan ta juya ta yiwa sarakan gaisuwar tare domin ba wanda zata fara gaishewa ta bar daya dan rabonta da mijin nata kusan kwana uku kennan
Sarki SHAHEED ne ya dubi dogaran dake tsatsaye kansu dan su san maganar tasu ce
Da yatsunsa ya yi masu nuni kan su fita
Da sauri suka ringa zagayowa sai su zube har kasa su kara neman afuwa sannan su fice a haka har ya zama daga su sai su a dakin
Kanta dake kasa ta dan dago ta dubi mahaifinta dake dan nesa da ita
A hankali ta saki kukan da ta aura harma ya zama abokin yinta ba dare ba rana kan rasuwar yaron nata
Mahaifinta yana gannin yanda Anmy ta girgiza kai ta sada kanta hakan ya saka shi yin gyaran murya yana kallonta
A nitse ya ce" shin baki yarda ba a maido maki yaronki ne ZULAIHAT?
Da sauri ta sada kanta dan a kausashe ya yi maganar wace ke nuna ransa ya baci da irin kukan nata, wanda ya tabata kafin ya zo sarakuwarta da mijinta ba zasu kasa rarashinta ba harma su nuna mata adu'a ya fi bukata ba kuka ba
Muryarsa ya kuma budewa a dake wanda hakan ya saka yan matan Anmy baki daya dagowa suka zuba masa ido wanda idan sarki baba na magana haka du kowa kansa yake sadawa
Da sauri Anmy ke saka kafarta tana dan zungurinsu, ta hakan suke tunnawa sunna mayar da dubansu kasa
Sai dai Zahrau haka kawai ta kara kure rawaninsa da kallo kafin ta sada kan nata
Cikin wata kakausar muryar ya ce" wannan ai aikin banza ne bayan kema kin san idan yanzu wanda ya halice ki ya yi kiranki koda duka duniya ne gatanki bamu isa mu tare maki ko mu hanna ki ba ko a dadaure ko a nitse sai kin amsa dan shi ya amsa zaki auri kuka ki ringa yi masa kina hanna shi sukuni a inda yake, shin a kanki aka fara rasa yaro ne ZULAIHAT?
A hankali , cikin tatausar murya Anmy ta ce" Zulaihat na neman afuwa Allah ya huci zuciyar sarki mai adalci
Dubanta ta kai wajen Shaheed wanda ya dace ya nema mata afuwa aman ya yi biris, san hararansa Anmy ta yi hakan ya sa ya kawar da dubansa daga kanta
Dayan kuwa idan baki sun shigo nan suke zama a amshi gaisuwa
Bangare bangaren gidajen kowa ya tara jama'arsa yana amsar gaisuwa
Sai yanke yanke ake ana sadaka, rasuwar dai taro na mamaki tamkar wani tsohon magidanci ne ya rasu
Babu wace ta koma gida, a nan bangaren suke kwana wajen Anmynsu wace ke shiga tsakaninsu su layu du su lalafe mata domin baki daya wayoyinsu ta karbe ta kashe dan ta lura wayar NAJEEBA bata daina kuka gashi ita kuwa ta jima tana son ta kasance da y'ayan nata haka
Iyayen daidaiku sun zo har masarauta sun yi gaisuwa, mahaifiyar NAJEEBA dake saudiya ta yi vidio call sai dai sam NAJEEBA ta ki amsarta, sai da Anmy suka gaisa
Yau akaiwa yarima adu'ar uku
Yau ne jama'a ta ringa ragewa tun bayan adu'ar
Kafin ake cewa azahar ta shigo kai ya kasance du sai na kusa wato na kud da kud
A yaune kuma jirgin mai martaba sarkin agadez ya sauka da abokannan tafiyarsa suka yi tataki da kansu dan zuwa gabatar da gaisuwa wa sirikinsa da kuma yarsa na rashin dansu daya cilo da sukai
An masu tarba irin ta bajinta
An sauke su a bangaren Mai martaba Sarki SHAHEED, ya sauke su tare da mutanensa na arziki su ABIH, su DAYABU, su liman Baba,
Dogarai kuwa sun cika ko'ina sai kai kawo suke sun tatare ko'ina
Cike da kamala ta mike ta kai dubanta wajen ZAHRAU, da UMMULKHAIR da UMMUKULSUM, da NAJEEBA
Cikin nutsuwa ta ce" ku tashi ku min rakiya mu gaishe da mahaifin ZINARIA
Mimikewa sukai yan matan reras , baki dayansu sanye suke da bakaken abayayoyi yan saudiya masu shegen kyau da tsari ga tsada
Wani sirrin kyau ne da y'ayan nan tamkar idan kana kallonsu kar ka daina
Bakin fatarsu irinsa ne ke wartar farar fats harma ta yi mangarin idan ta samu kalar nan ai sai yi
Ga najeeba dake anfani da roger cavalais, sannan sabululukanta na anfani tana hada kayanta ne da kanta ciki kuwa harda su kurkum da sabulun victago da zuma da su kankana da dai sauransu hakan ya saka fatarta ita kadaima sheki take tana haskawa, sai haskenta ya fi na sauran ya kasance bakin nata irin na American din nan ne mai kyan gaske
Ko yanzu da take zaman makokin bakinta baya rabo da dan jan bakin nan, hakama idannuwanta bata cire abin nan ba, gata da kallon kasa kasa sai ta lumshe idannuwan nata
Anmynsu ce gaba
Su kuwa sai sukai biyu a bayanta, biyu a bayan biyun wato sun jeru sunna wata irin tafia mai cike da kasaita idan ta ajiye kafafuwanta sai ta dauke su zahrau dake bayanta ke ajiye nasu, sannan su Najeeba su ajiye nasu
Jakadiya na tafe tana shelar fitowarsu hakan ya sa du wani bawa ko wanda Anmy ta girma ya ja ya tsaya ya sada kansa dan girmamawa ga uwar gidan marigayi sannan uwar mai martaba
Fuskarta sake take daga kanta a hankali sannan da dan murmushi tana amsa irin gaisuwar da ake ta jefo mata, da yawa cikin manyan samarin gidan sukan bi y'ayan dake bayanta da kallo, da yawa sun dauri niyar isar da sakonsu dan a kara kulla zumunci, wasun kuwa na masu kallon sha'awa da tsoro domin su din dai ba dai kyau ba sai dai masifa!
a haka har suka karasa wajen shigar
Dogaran kofar dake tsaitsaye da jakadiyoyin ne suka kwashi summa nasu kirarin da kawo mata gaisuwar da adu'ar Allah ya jikan yarima karami da fatan Allah ya jawo masu zama
Babar jakadiya, tsohuwa ce ta shiga ta duka ta sanar da isowarsu
Tana fitowa anmy ta shiga da bismillah sannan kanta a sade dan girmama sarkin garin agadez duda tana kyautata zaton ta girme shi domin shima ba wani tsoho bane
Saman kujera ta zauna kafin ta ja alkyabarta ta gyara
Baki dayansu kasa suka zazauna kusa da kafafuwan Anmy,
Tun da suka shigo ta lumshe idannuwanta sakamakon kanshin turaran nan dake matukar kasheta a duniya
Sunnan turaran *MUSKI-JAH* sakamakon jinsa da take a wajen wannan bawan Allah ya sakata nemansa a lokacin da suka fita waje a paris
A ranar baki daya tanadinta ta saka ta siyo turaran nan, tana bude shi ta ga wata yar karamar kwalba sannan ba'a cike ba dan ko rabin kwalbar bata kai ba aman kuma yakeda muguwar tsada mai rikitarwa
Daga ranar ta nemi waje ta ajiye maganar turaransa, yanzu abinda ta fi sakowa a gaba irin yanda yake saka tufafinsa
Tana son ta ji wai du suturarsa daya zata kai nawa? Ba dan komai take son gane wasu al'amura nasa ba sai dan ta gane shin gayunsa da sarautarsa na bagidaji ne ko ya waye? (Ji fa rigima)
A hankali ta dago da idannuwanta a lokacin da dogarin nan ke ta fadin" saraki sun amsa gaisuwarku jinnin MUTALAB, saraki sun ji dadin kulawarku .....
Bakinta ta tabe tana ayanna ko a ina mukai magana?
Idannuwanta ta sauke a fuskar mahaifinta wanda akaiwa sasaukan rawani
Irin yanda yake dan murza goshinsa ya sakata sakar masa murmushi domin kwarai ta fanr ya takura da rawanin nan ne
Dubanta ta maida wajen DAYABU, hararar da ya sakar mata ta sakata yi masa murmushi har hakoranta suka bayana domin ta san hararar baya wuce numbersa da wasu daga cikin samarinta zasu dama dan ta tabata zai sha kira domin akoy masu numbersa a cikinsu idan sun sha mata kai ta hada su da yayanta takan basu ba abinda ya shafeta
Kalle kallenta ya kai fuskar sarkin Gadez , a hankali ta bi wajen da ya kurawa ido
Zahrau ce ke kallon Dogarin dake ta zuba ta san tausaya masa take a cikin ranta, sai dai irin kuretan da ya yi da ido ya saka NAJEEBA sakin murmushi har tana dan dantse lebenta na kasa
Idannuwanta masu kale kale suka kaita wajen fuskarsa
Irin yanda sukai ido hudu ya sakata da saurin gaske ta sada kanta sakamakon kallon nan na tsana da ya wurga mata wanda ke sakata jin faduwar gaba da tambayar kanta shin me ta masa? Sam bata iya kallon cikin idannuwansa, dan bakinta ta murguda a kasan zuciyarta kuwa fadi take" wai shi hala dan daudu ne da yake saka kwali?
Kara bin fuskarta da ta sada ya yi da ido, lebensa dake cikin rawaninsa ya datse da hakorinsa na sama
A kasan zuciyarsa ya furta" wani rashin jin maganar kika shirya da ya saka ki sakin murmushi Majanune?
Dubansa ya maida wajen Dayabu, sai kuma ya lumshe idannuwansa yana ayanna ya zama wajibi a koya mata biyaya da bambancin sarkinta da yan iskanta! Irin yanda ta tsinke fuskar Zinaria da mari a gaban sarkinta ta yi rashin kunya mai tsauri!
Muryoyin dogarai da jakadiyoyin dake kofa na shaida karasowar Zinaria ya saka NAJEEBA kara janye kafamfafuwanta domin ita ta fi kusanta da hanya ta kuma tabata idan har ta shigo ta ganta a bakin hanyar nan zata baje tafiyarta ta yanda zata taka mata kafa ne ita kuwa ta kara mata na biyu a gaban ubanta!
Za ina tsalake ranakun posting idan har baku daukaka comment dinku ba😔
[1/20, 9:50 AM] Ummu Suhan😍: 🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
9
Cike da wata irin kasaita da alkyaba a jikinta ta sanyo kai, bayanta kuwa jakadiya ce, sai bayi mata uku du suka duduka sannan suka dukar da kawunansu kasa
A hankali ta ringa takawa har ta karasa kusa da Anmy ta samu waje saman luntsumemiyar kujerar dake nan ta zauna hakan ya kasance Zahrau na zaune kusa da kafarta ne
Sai da ta sada kanta a hankali ta gaishe da Anmy, sannan ta juya ta yiwa sarakan gaisuwar tare domin ba wanda zata fara gaishewa ta bar daya dan rabonta da mijin nata kusan kwana uku kennan
Sarki SHAHEED ne ya dubi dogaran dake tsatsaye kansu dan su san maganar tasu ce
Da yatsunsa ya yi masu nuni kan su fita
Da sauri suka ringa zagayowa sai su zube har kasa su kara neman afuwa sannan su fice a haka har ya zama daga su sai su a dakin
Kanta dake kasa ta dan dago ta dubi mahaifinta dake dan nesa da ita
A hankali ta saki kukan da ta aura harma ya zama abokin yinta ba dare ba rana kan rasuwar yaron nata
Mahaifinta yana gannin yanda Anmy ta girgiza kai ta sada kanta hakan ya saka shi yin gyaran murya yana kallonta
A nitse ya ce" shin baki yarda ba a maido maki yaronki ne ZULAIHAT?
Da sauri ta sada kanta dan a kausashe ya yi maganar wace ke nuna ransa ya baci da irin kukan nata, wanda ya tabata kafin ya zo sarakuwarta da mijinta ba zasu kasa rarashinta ba harma su nuna mata adu'a ya fi bukata ba kuka ba
Muryarsa ya kuma budewa a dake wanda hakan ya saka yan matan Anmy baki daya dagowa suka zuba masa ido wanda idan sarki baba na magana haka du kowa kansa yake sadawa
Da sauri Anmy ke saka kafarta tana dan zungurinsu, ta hakan suke tunnawa sunna mayar da dubansu kasa
Sai dai Zahrau haka kawai ta kara kure rawaninsa da kallo kafin ta sada kan nata
Cikin wata kakausar muryar ya ce" wannan ai aikin banza ne bayan kema kin san idan yanzu wanda ya halice ki ya yi kiranki koda duka duniya ne gatanki bamu isa mu tare maki ko mu hanna ki ba ko a dadaure ko a nitse sai kin amsa dan shi ya amsa zaki auri kuka ki ringa yi masa kina hanna shi sukuni a inda yake, shin a kanki aka fara rasa yaro ne ZULAIHAT?
A hankali , cikin tatausar murya Anmy ta ce" Zulaihat na neman afuwa Allah ya huci zuciyar sarki mai adalci
Dubanta ta kai wajen Shaheed wanda ya dace ya nema mata afuwa aman ya yi biris, san hararansa Anmy ta yi hakan ya sa ya kawar da dubansa daga kanta