Sashe 69
Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hannun abokinsa latif ya rike ya ce" Abdul latif, ka taimaka ka kaini wajen Nadia, ka kaini na ji me na mata a duniya? Walahi du rashin jin maganata na ajiye dan kar Najeeba ta kubuce min, ina nan ina ta neman inda zan ganta kulun a kofar shagonta nake wuni dan na sameta ta yi hakuri da abinda na mata, ni ban yi dan bata ranta ba
Ku shaida ne nan wayarta a hannuna na ringa korar du wani mai kiranta dan bana so idan na zo malakarta wani ya zame min matsala
Kune shaida summar da ni aka yi kan wayarta ni kaina ban san mutumen ba aman shine yau zan ga daurin aurenta?
Shi dai Abdul Latif kama shi ya yi domin kwarai ya san yana son Najeeba da gaske, dan haka bai tsaya yi masa shakiyanci ba ya taimaka masa suka shige mota
Yana shirin tayar da motar docter ya fito yana langwui
Tsayawa ya yi ya dafe habarsa ya furta" kan uba, lale na yarda cewar *MAGE, MAI KWONCIYAR DAUKAN RAI CE NAJEEBA* da ta tashi kawo mana dukan sai ta kawo da wajen da ko mun sha kwaya ba zamu tunkara da salon iskanci ba
Soja ne ya fito har ya zarta ya dawo yana kallon Docter
Daria ce ta kubce masa kafin ya girgiza kansa ya yi gaba, lale ya san yarinyar nan ta fi karfinsa kuma ya yarda Allah ne ya kareta domin matar manya ce, shi irin ya dan yi hira da itama bai samu ba sai dai daga nesa
Da yawa sun ji jiki ciki harda likitan zuciyarta, da ambasador
Ambasador kansa ya sada a cikin masalaci idannuwansa sukai masa wani irin jajajir gashi kuma shi a cikin masalacin yake ba a balbalin masalacin ba bare ya mike ya fita, sai ya zama a lokacin da ya dago dubansa sai da gabansa ya fadi domin yana kallon sarki sai baki daya ya raina kansa, shima shaheed din shi ya kalla kafin ya cire kansa yana sauraron haramar daurin aurensa da Nadia kasan zuciyarsa kuwa haka kawai ta hanna masa sakat, gani yake du inda ya kai dubansa ba zai rasa samarin yarinyar ba, kai da ba dan an masa kwakwaran bincike kan kawar nan tata ba, da ba zai aureta ba, an fada masa cewar yarinyar girman kanta ya saka samari da yawa ke tsoron tunkararta, har fadi ake cewar tana da nauyin jinni, sosai iyayenta ke faman ta tsayar da miji domin kawancen nasu da Najeeba shekara uku ta bata, Nadia na dauke da shekaru ashirin da hudu tana cikin ta da biyar, ita kuwa fitsarariyar na dauke da shekaru ashirin da daya tana cikin da biyu
Idan ya kalli Ambasador ba abinda ke fado masa irin maganar.....ina so na ganki, na zo maki da dukan abubuwan da kika ce kina so na tsarabarki, ina so na ganki ko zaki bani nutsuwa!
Lalle uwa uwa ce
Bai yarda da iyaye a kasar musulmai sun isa da y'ayansu ba sai a kansa
Gashi dai ya kai inda ya kai Alhmdulilah aman kuma gashi a karo na biyu an daura masa aure da zabin da ba nasa ba
Idannuwansa ya kuma lumshewa ya maida hankalinsa wajen da ake kara raraba su goro ne ba kadan ba mutane sunna ta amsa a bokitai anna ta fita da su kafin a shiga haramar wani daurin auren, ga Dayabi, ga ABIH, ga sarkin agadez, ga yarima a kusa da shi sai ya shiga salatin annabi da fatan a watse lafia..........
Hi mutanen arziki,
Zan yi posting na biyu yanzu, idan kuka fitar da shi za'a janye dokar bibiyu🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
37
Yana langwui ya shige dakin da Nadia ke zaune da kawayenta da auntynta da kuma daidaikun yan uwanta, dakin mai girma ne hakan ya sa kowa ke sha'aninsa an fi raja'a wajen daukan hotunna Nadia ta sha kyau domin aida ce ta zo ta mata mak'up har gida tana shaida mata cewar Najeeba bata fita kwana biyu yayarta ke fita saloon aman da ta fito zata shaida mata, ita kuwa ta dauki niyar ai Sai an nemo mata Najeeba ta tsantsara mata firgitaciyar kwaliyar da zata haukata mata sarkinta
A lokacin tana shirin shan wasu magungunnan hausa ne da auntynta ta dama mata da nono mai tsami, sosai fa Nadia ke amsar tsumi daga wajen iyayenta domin suma wayayun mata ne duda ba'ai mata gyaran jiki ba sun bar hakan a zuwan sai ta tare dan lokaci ya kure yawon neme nemen abubuwansu ya ishe su
Yana zuwa ya zube , mamanta da ta ga yannayinsa ta tsame daga mutane ta yo dakin
Auntynta kuwa tun da ya fashe da kuka ta shiga korar mutane cike da tashin hankali tana kallonsa
Su hudu suka yi saura sai tambayarsa ba'asin kukansa ake
Yana dago kai cike da muryar kuka ya ce" ashe Nadia ta san haka ta barni na yi ta hauka a kan kawarta? Ashe ta san wacece kishiyarta ta kyaleni na ringa barnar zuciyata da dukiyata ina hauka?
Nadia ta ringa kallonsa tana son ta ji abinda yake son fadi
Sai da ya share hawayensa ya ce" Allah ya isa tsakanina da ke Nadia, shine kika kyale ni ina haukan Najeeba ashe da ita za'a daura auren Sultan?
Nadia dake ta kallonsa ta yi wani dan tsam kafin ta taso da sauri ta juyi fuskarsa ta ce" hei dan uwa, me ka ce?
Hannunta ya janye daga fuskarsa cike da jin haushi ya ce" tambayata kike abinda nace? Nace kin ji kunya son kudin naki ya rasa wa zaki cuta sai ni jinnin ki?
Da sauri ta ce " bla bla bla, ba shi din nake son ji ba, auren Najeeba da sultan? Waye sultan kuma?
Lalle kin iyabiskanci Nadia, ya fada
Mamarta ce ta ce" kai Huzaifa wai meye haka? Me kake fada haka?
Huzaifa ya juya wajenta ya ce" mama, ni Nadia zata boyewa Najeeba kawarta ce kishiyarta da za'a daura aure da Sarki yau? Yanzu ina zaune aka daura auren Najeeba da sarki kafin na baro wajen
Nadia ta zazaro ido kafin ta dora hannayenta saman kanta, a rikice ta kara yiwowa kusa da shi ta dafa shi da hannunta da ya kwashi rawa ta ce" yanzu domin Allah me na maka zaka zo min da zancen dake iya halaka ni Huzaifa? NAJEEBA fa tana gida kwonce bata da lafia inji aida da ta zo ta min kwaliya, kai kuwa sai kace wai Najeeba Najeeba Najeeba ce aka daura aurenta da Sarki?
Daria ya fara yana kallonta hade da hawayen dake zuba a idannuwansa
Nunata ya ringa yi da yatsarsa ya ce" wawuya, meye ya tayar maki da hankali? Kema kin san zaki ci kakanki ne? Kema kin rikice ina ni? Kin min bakin ciki yarinya kuma sai Allah ya saka min!
Wani irin ta kurma hannayenta saman kanta ta zube ta shiga burgima fadi take" mama bilahilazi ku yi kiran baba na fasa, walahi na fasa auren mijin Najeeba, dama Najeeba ce dayar? Mama kin kuwa san Najeeba? Mama Najeeba fa kawata wace muke zuwa nan wani sa'in wace kike cewar yarinyar nan tana birge ki dan bata shafe shafen nan na yan matan zamani gata saliha mai kyan hali
Mama na rantse maki da Allah Najeeba kililin kasau ce, kanta a kasan nan take harbi irin na bakin maciji ko harbawa ba'a yi ake macewa
Mama Najeeba ce fa? Walahi halaka ni zata yi, idan wani bai kashe ni ita zata kashe ni dan na tabata sai ta ci uwani da na auran mata miji! To wai me hadinta da shi bayan a duniya ko maganarsa bata so ina mata, irin idan zance ya kawo zance sam bata so a kawo maganar sarautar garin nan bale sunnansa ? Mama ni ke zaune da Najeeba tun safe har dare a saloon dinta, ni ganau ce ba jiyau ba mama da ubwan waye bata dakuwa idan ka kawo mata simple raini bare ni da zan auri mijinta? Mama ki rufa min asiri tun ina numfashi ki hanna abin nan
Da mamaki mamanta ke binta da kallo hakama auntynta ke tareta tana fadin" ke meye wannan, rage muryarki kar ki sa a fara taruwa mana, ki bari mana
Mamanta ta ce" ke yanzu ai abin murna ne ace Najeebar nan dai da na sani ce kishiyar taki, yarinyar da bata taba gaisheni a tsaye ba sai ta duka, yarinyar da in tsintsiya na dauka zata amshe ta share wajen da nake son kimtsaya? Yarinyar da nan in ta zo sai ta baiwa kannenki abin dadi ni kuwa du da ina aiki sai ta min kyautar kudi masu yawa? Yarinyar abin mangari wace nake fadin da Ibrahim dina ya girma sai na aura masa ita domin a duniya tarbiyarta na birge ni shine ke marar kirki zaki ringa fadin kalamai irin haka munana a kanta? Haba Nadia , Haba Nadia nan abanku baya so kina kawaye aman yarinyar nan da kansa ya furta eh lale wannan tana da tarbiya ya yarda ki yi kawance da ita aman shine Nadia zaki fadi haka a kan yar mutane? Ni walahi sai yanzu hankalina ya kwonta zan fita na ci gaba da bikina cikin farin ciki
Nadia ta zabura ta mike tana neman wayarta a haukace ta ce" ina, ina ba zaki gane ba mama, ba zaki gane ba, a daki kike mama, mama baki fita kin san me duniya take ciki ba, mama a zamaninku babu kililin kasau, kai ko akoy ta yanzu nata salon daban ne, mama ki manta wata maganar cewa wai zan je na shinfida sarauta ko na je na yi tinkaho ko na je na kwace miji a hannun zinariya, walahi walahi sai na zama uwa akuya a gaban Najeeba
Kai ina, a watse, walahi a watse an fasa auren nan
Kokarin fita take dan watsar da taron mamanta da kanwar mamanta suka rikota suka yi ciki da ita sunna fadin Huzaifa ya kama masu
Ku shaida ne nan wayarta a hannuna na ringa korar du wani mai kiranta dan bana so idan na zo malakarta wani ya zame min matsala
Kune shaida summar da ni aka yi kan wayarta ni kaina ban san mutumen ba aman shine yau zan ga daurin aurenta?
Shi dai Abdul Latif kama shi ya yi domin kwarai ya san yana son Najeeba da gaske, dan haka bai tsaya yi masa shakiyanci ba ya taimaka masa suka shige mota
Yana shirin tayar da motar docter ya fito yana langwui
Tsayawa ya yi ya dafe habarsa ya furta" kan uba, lale na yarda cewar *MAGE, MAI KWONCIYAR DAUKAN RAI CE NAJEEBA* da ta tashi kawo mana dukan sai ta kawo da wajen da ko mun sha kwaya ba zamu tunkara da salon iskanci ba
Soja ne ya fito har ya zarta ya dawo yana kallon Docter
Daria ce ta kubce masa kafin ya girgiza kansa ya yi gaba, lale ya san yarinyar nan ta fi karfinsa kuma ya yarda Allah ne ya kareta domin matar manya ce, shi irin ya dan yi hira da itama bai samu ba sai dai daga nesa
Da yawa sun ji jiki ciki harda likitan zuciyarta, da ambasador
Ambasador kansa ya sada a cikin masalaci idannuwansa sukai masa wani irin jajajir gashi kuma shi a cikin masalacin yake ba a balbalin masalacin ba bare ya mike ya fita, sai ya zama a lokacin da ya dago dubansa sai da gabansa ya fadi domin yana kallon sarki sai baki daya ya raina kansa, shima shaheed din shi ya kalla kafin ya cire kansa yana sauraron haramar daurin aurensa da Nadia kasan zuciyarsa kuwa haka kawai ta hanna masa sakat, gani yake du inda ya kai dubansa ba zai rasa samarin yarinyar ba, kai da ba dan an masa kwakwaran bincike kan kawar nan tata ba, da ba zai aureta ba, an fada masa cewar yarinyar girman kanta ya saka samari da yawa ke tsoron tunkararta, har fadi ake cewar tana da nauyin jinni, sosai iyayenta ke faman ta tsayar da miji domin kawancen nasu da Najeeba shekara uku ta bata, Nadia na dauke da shekaru ashirin da hudu tana cikin ta da biyar, ita kuwa fitsarariyar na dauke da shekaru ashirin da daya tana cikin da biyu
Idan ya kalli Ambasador ba abinda ke fado masa irin maganar.....ina so na ganki, na zo maki da dukan abubuwan da kika ce kina so na tsarabarki, ina so na ganki ko zaki bani nutsuwa!
Lalle uwa uwa ce
Bai yarda da iyaye a kasar musulmai sun isa da y'ayansu ba sai a kansa
Gashi dai ya kai inda ya kai Alhmdulilah aman kuma gashi a karo na biyu an daura masa aure da zabin da ba nasa ba
Idannuwansa ya kuma lumshewa ya maida hankalinsa wajen da ake kara raraba su goro ne ba kadan ba mutane sunna ta amsa a bokitai anna ta fita da su kafin a shiga haramar wani daurin auren, ga Dayabi, ga ABIH, ga sarkin agadez, ga yarima a kusa da shi sai ya shiga salatin annabi da fatan a watse lafia..........
Hi mutanen arziki,
Zan yi posting na biyu yanzu, idan kuka fitar da shi za'a janye dokar bibiyu🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
37
Yana langwui ya shige dakin da Nadia ke zaune da kawayenta da auntynta da kuma daidaikun yan uwanta, dakin mai girma ne hakan ya sa kowa ke sha'aninsa an fi raja'a wajen daukan hotunna Nadia ta sha kyau domin aida ce ta zo ta mata mak'up har gida tana shaida mata cewar Najeeba bata fita kwana biyu yayarta ke fita saloon aman da ta fito zata shaida mata, ita kuwa ta dauki niyar ai Sai an nemo mata Najeeba ta tsantsara mata firgitaciyar kwaliyar da zata haukata mata sarkinta
A lokacin tana shirin shan wasu magungunnan hausa ne da auntynta ta dama mata da nono mai tsami, sosai fa Nadia ke amsar tsumi daga wajen iyayenta domin suma wayayun mata ne duda ba'ai mata gyaran jiki ba sun bar hakan a zuwan sai ta tare dan lokaci ya kure yawon neme nemen abubuwansu ya ishe su
Yana zuwa ya zube , mamanta da ta ga yannayinsa ta tsame daga mutane ta yo dakin
Auntynta kuwa tun da ya fashe da kuka ta shiga korar mutane cike da tashin hankali tana kallonsa
Su hudu suka yi saura sai tambayarsa ba'asin kukansa ake
Yana dago kai cike da muryar kuka ya ce" ashe Nadia ta san haka ta barni na yi ta hauka a kan kawarta? Ashe ta san wacece kishiyarta ta kyaleni na ringa barnar zuciyata da dukiyata ina hauka?
Nadia ta ringa kallonsa tana son ta ji abinda yake son fadi
Sai da ya share hawayensa ya ce" Allah ya isa tsakanina da ke Nadia, shine kika kyale ni ina haukan Najeeba ashe da ita za'a daura auren Sultan?
Nadia dake ta kallonsa ta yi wani dan tsam kafin ta taso da sauri ta juyi fuskarsa ta ce" hei dan uwa, me ka ce?
Hannunta ya janye daga fuskarsa cike da jin haushi ya ce" tambayata kike abinda nace? Nace kin ji kunya son kudin naki ya rasa wa zaki cuta sai ni jinnin ki?
Da sauri ta ce " bla bla bla, ba shi din nake son ji ba, auren Najeeba da sultan? Waye sultan kuma?
Lalle kin iyabiskanci Nadia, ya fada
Mamarta ce ta ce" kai Huzaifa wai meye haka? Me kake fada haka?
Huzaifa ya juya wajenta ya ce" mama, ni Nadia zata boyewa Najeeba kawarta ce kishiyarta da za'a daura aure da Sarki yau? Yanzu ina zaune aka daura auren Najeeba da sarki kafin na baro wajen
Nadia ta zazaro ido kafin ta dora hannayenta saman kanta, a rikice ta kara yiwowa kusa da shi ta dafa shi da hannunta da ya kwashi rawa ta ce" yanzu domin Allah me na maka zaka zo min da zancen dake iya halaka ni Huzaifa? NAJEEBA fa tana gida kwonce bata da lafia inji aida da ta zo ta min kwaliya, kai kuwa sai kace wai Najeeba Najeeba Najeeba ce aka daura aurenta da Sarki?
Daria ya fara yana kallonta hade da hawayen dake zuba a idannuwansa
Nunata ya ringa yi da yatsarsa ya ce" wawuya, meye ya tayar maki da hankali? Kema kin san zaki ci kakanki ne? Kema kin rikice ina ni? Kin min bakin ciki yarinya kuma sai Allah ya saka min!
Wani irin ta kurma hannayenta saman kanta ta zube ta shiga burgima fadi take" mama bilahilazi ku yi kiran baba na fasa, walahi na fasa auren mijin Najeeba, dama Najeeba ce dayar? Mama kin kuwa san Najeeba? Mama Najeeba fa kawata wace muke zuwa nan wani sa'in wace kike cewar yarinyar nan tana birge ki dan bata shafe shafen nan na yan matan zamani gata saliha mai kyan hali
Mama na rantse maki da Allah Najeeba kililin kasau ce, kanta a kasan nan take harbi irin na bakin maciji ko harbawa ba'a yi ake macewa
Mama Najeeba ce fa? Walahi halaka ni zata yi, idan wani bai kashe ni ita zata kashe ni dan na tabata sai ta ci uwani da na auran mata miji! To wai me hadinta da shi bayan a duniya ko maganarsa bata so ina mata, irin idan zance ya kawo zance sam bata so a kawo maganar sarautar garin nan bale sunnansa ? Mama ni ke zaune da Najeeba tun safe har dare a saloon dinta, ni ganau ce ba jiyau ba mama da ubwan waye bata dakuwa idan ka kawo mata simple raini bare ni da zan auri mijinta? Mama ki rufa min asiri tun ina numfashi ki hanna abin nan
Da mamaki mamanta ke binta da kallo hakama auntynta ke tareta tana fadin" ke meye wannan, rage muryarki kar ki sa a fara taruwa mana, ki bari mana
Mamanta ta ce" ke yanzu ai abin murna ne ace Najeebar nan dai da na sani ce kishiyar taki, yarinyar da bata taba gaisheni a tsaye ba sai ta duka, yarinyar da in tsintsiya na dauka zata amshe ta share wajen da nake son kimtsaya? Yarinyar da nan in ta zo sai ta baiwa kannenki abin dadi ni kuwa du da ina aiki sai ta min kyautar kudi masu yawa? Yarinyar abin mangari wace nake fadin da Ibrahim dina ya girma sai na aura masa ita domin a duniya tarbiyarta na birge ni shine ke marar kirki zaki ringa fadin kalamai irin haka munana a kanta? Haba Nadia , Haba Nadia nan abanku baya so kina kawaye aman yarinyar nan da kansa ya furta eh lale wannan tana da tarbiya ya yarda ki yi kawance da ita aman shine Nadia zaki fadi haka a kan yar mutane? Ni walahi sai yanzu hankalina ya kwonta zan fita na ci gaba da bikina cikin farin ciki
Nadia ta zabura ta mike tana neman wayarta a haukace ta ce" ina, ina ba zaki gane ba mama, ba zaki gane ba, a daki kike mama, mama baki fita kin san me duniya take ciki ba, mama a zamaninku babu kililin kasau, kai ko akoy ta yanzu nata salon daban ne, mama ki manta wata maganar cewa wai zan je na shinfida sarauta ko na je na yi tinkaho ko na je na kwace miji a hannun zinariya, walahi walahi sai na zama uwa akuya a gaban Najeeba
Kai ina, a watse, walahi a watse an fasa auren nan
Kokarin fita take dan watsar da taron mamanta da kanwar mamanta suka rikota suka yi ciki da ita sunna fadin Huzaifa ya kama masu