← Book details Mage Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 117 OF 138

Sashe 117

Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Baki daya ya kwalalo idanniwansa yana kallon ikon Allah, a hankali ta ringa matsowa kusan shi tana mai bin wakar nan a sanyaye sannan da hannunta na dama tana mai nuna masa kan ya matso gareta tana dan tare wayar kar ta fado da kanta bata sana hannu ba hakan ya sa idannuwansa ke yawon binta du inda ta dan juya, uwa uba da gaya sai kawai ta dan juya ta kara kada mutanen da kyam sai ya bi su da kallo sannan ta juyo har ta idasa zuwa daf da shi

A hankali ta dan kara tsayinta ta yo dadage duda bata kamo tsayinsa ba sai kawai ta dora yar yatsarta tun daga saman goahinsa kamar yanda ya yi mata a jiya ta shiga yawo da ita har ta kawo wajen lebunnansa, a hankali ta zazagaya lebunnan nasa sai kawai ta saka dayan hannun ta dan kamo bayan keyarsa ta yo kasa kadan da fuskarsa
A hankali ta kusanta tata fuskar kusa da tashi, baki daya ya sakankance ya gama shiryawa harta da bakinsa ya saki tsabar masifafen mamakin dake shirin kaishi kiyama bai shirya ba sai kawai ta kawar da lebunnanta daga daf da fuskar tasa ta mana masa peck a kunci sannan ta yi wani irin zabura ta yar da wayar a nan ta shige bayi a guje wanda a lokacin da ta yi hakan bai san inda kansa yake ba ya sakankance ne jira kawai yake

Baki daya ya kara kwalalo idannuwansa, murya a shake ya bi inda ta shige da kallo

Hasbunnalahu wani'imal wakim ya fada a bayane yana dafe kirjinsa dake wani irin dokawa fat fat fat tamkar zai ballo ya fito masa

A hankali ya ja kafafuwansa da sukai masa nauyi ya karasa kusa da bayin ya dan dora kansa a jikin kofar, muryarsa cen ciki ya ce" open the door Beebah "

NAJEEBA ta dan zaro ido, sai kuma ta makale kafadunta kamar yana ganninta tama ki yin magana kwata kwata

A sanyaye ya kara furta" plz "

Bakinta ta dan tabe , sam ta ki nuna da ita a wajen

SHAHEED ya kara dora kansa sosai , muryarsa na kara bacewa sai sanyin dake neman lulube shi , hannayensa na bari kadan kadan ya dora saman abin budewar muryarsa har rawa take ya furta" kina son kashe ni ne? "

Tabatawar da ta yi ta kile kuma ta bar kys din a jiki ya sakata matsawa ta cire pant dinta ta haye masai abinta ta gyara zamanta

SHAHEED ya dora hannunsa da dan karfi ya ce" ki bude min BEEBAh, ki bude min kar ki ilatani i beg u "

Dan idannuwanta ta zaro jin muryarsa ta fara baci, ta kara gyara zama a hankali ta ce" ehem "
Irin gyaran muryar nan idan kana bayi

SHAHEED ya lumshe idannuwansa yana jin yanda kansa ke sarawa haka kuma bugun zuciyarsa na kara girmama, a sanyaye ya ce" idan har na shiga bayin nan, sai nai maki fila fila BEEBAhhhhhhh "

Bakinta ta tabe tana kara kallon wajen da ta kile ta ci gaba da neman uzurinta ah tom

Ransa a bace ya budi baki da karfi ya ce"

Oh gidan nan, jama'a wani dan abu ne ya rike ni😭😭😭😭🙄🙄🙄

[3/31, 11:30 PM] BAK'A CE: 🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻

*Na*

*SAJIDA*

💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝

☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_

59

Ransa a bace ya budi baki da dan karfi ya ce" BEEBAHHHHHHHHHHHH "

Sai da ta dan zabura a hankali ta ce " Um? "

Shaheed ya dan sasauta muryarsa ya ce" Bude min kin ji? "

NAJEEBA ta makale kafadarta, a hankali ta ce" to ban gama ba ai "

" Me kike yi? " ya tambaya idannuwansa a lumshe

Ido ta zaro, sai kuma ta shiga guna guni Kasa kasa ta ce" kuma sai kawai na ce maka ga abinda nake yi fisabililahi SHAHEED , to wai idan na fitoma me zan maka ne da sanyin safiyar nan? "

Shiru ya yi, shiru mai dauke da ma'anoni, sannan yana sauraron irin yanda zuciyarsa ke doka masa dan wani takaici

A hankali ya juya ya shiga jan kafafuwansa yana dan dama bai shigo dakin nan ba, da da ya ji kidan nan daga kofa ya tsaya ya yi magana, aman sai kawai ya wani shigo kansa tsaye
Tabas shi din ya jima da yin aure, ya jima da sannin mace, sai dai fa wani baban lamari na rayuwarsa a kalmar mace ba wai macen da zai yi wasa da daria da fahimtar junna da komai bace, aa , shi ya sa a yanzun da wannan yar ta AMMI ta masa wannan lamari sai ya shige shi ba haufi,

Ya jima yana kai kawo a dakinsa kafin ya nufi bayi ya shiga kintsa kansa domin kuwa zai je fada ne yau su yi zama na musaman da baki daya fadawa , zaman da ya saja kowa ya amsa kira a kan lokaci idan ba haka ba komai zai iya samun wanda bai amsa kiran ba daga hukuncin cikin fada

Sosai ya sha shirinsa ya bayana dawisunsa sai baza kamshi yake abinsa duda dan haushin yar gidan AMMI da ta rikita masa lisafi da sasafen nan, lebensa na kasa ya cije yana kallon kofar a ransa ya ayana 'zaki yi bayani ne' ya yi kwafa ya ci gaba da tafiarsa hankali kwonce ya fice

Najeeba kam sai da ta tabatar sahu ya dauke sannan ta sauka ta yi wankanta tsaf tsaf abinta

Akwatinta ta buda ta ringa dubawa da kyar ta samu atampa sket da riga, du sai aka zuba mata wasu manyan kaya shada, lesh, da alkyaba, sai kayan baci, da kyar ta iya ciro atampa

Wajen turaren nan ta koma har washe baki take ta dildila abinta a jikinta sannan ta saka riga da sket dinta suka zauna dasss a jikinta
Zuwa yanzun tafiarta ta daidaita sannan ta samu nishadin safiar nan abin ba'a cewa komai hakan ya sa ta kashe daurin zarah buhari mai hade da ture ka ga tsiya sannan ta zauna da wayar ta danna kira

ZAHRAU kamar jira take, cikin kamilaliyar muryarta da a yanzu ita take magana da ita wa kowa ba sai iya mijinta ba ta amsa salamar NAJEEBA

NAJEEBA ta ringa mata daria tana fadin "Aunty ba salama, hala wai ko kayanki baki dauka ba? "

Zahrau ta yi dariar itama dan a yanda take shakiyancin sai da ta sakata dariar dole, ZAHRAU ta ce" ke ina Ummu suke ? "

Najeeba ta ce" yanzu zan tarda su mu yita ta kare, rabonsu da ni tun da na farka na ganni a dakin SHAHEED, shine basu leko ni ba, ba waya har yanzu, irin sun manta da ni din nan ko sun goge ni a layin kanwarsu ko? "

ZAHRAU ta ce" NAJEEBA yaya Sultan din ne kike kama sunnansa kai tsaye haka? Idan ya ji ki zaki yabawa aya zakinta "

Najeeba ta yi yar daria , aman bata sanar mata sirrin abinda ta gama masa yanzu ba, sai dai kawai ta ce" Ba abinda zai min domin ni a Shaheed na san shi, ya buga kwalo da ni, ya ci namana , ya kwacen ice cream dina, dan haka sunnansa SHAHEED "

Murmushi ZAHRAU ta yi itama, a hankali ta ce" Ke yarima fa yana aeroport, kuma su UMMU basu sani ba, hasalima ko mahaifiyarsa bata sani ba, mahaifinsa dai ya sani sai kuma ni, jiya har kusan karfe goma ya nemi izinin son ganninsa, to yana bangarena shine ya same mu a nan ya duka har kasa ya kara neman gafara sannan ya nuna ya gaji, ya kasa iya hakuri , shifa ba abinda ya zuba a jikinta da za'a ce sai an ga idan bata da komai na wata uku, shi a bashi matarsa , yana son ya kara neman yafiyarta gashi ga ita, tabas tana amsa sakonsa ba laifi yanzun aman shi ba haka yake so ba, magana sak yake so su ringa yi ta fahimta, shi kam a bashi damar zuwa zance , Walahi Najeeba baki ji yanda kunya ta titsiyeni ba, aman mahaifinsa sai ya ringa sakin murmushi harda su gyara zama ya wani ce" ka je abinka, ka lalabata Allah ya sanya alkhairi " , maganar da nake maki dai yanzun yana aeroport shi ke jiran jirgin da zai yi damagaran da shi, yau babuma jirgi fa aman na sojawa zai bi tsabar ya saka rigima a ransa "

Murmushi NAJEEBA ke saki tana dan dage girarta, ta ce " muna jiransa, yanzu kuwa zan je na same su , baki san wani abu ba, ashe amintace maci amana ne ?"

Ai kuwa Najeeba ta kora mata labarin yanda aka yi, wanda hakan ya matukar girgiza Zahrau, ta yi mamaki sosai, sannan ta masu fatan shiriya, ta jinjina karfin sarautar garin damagaran da rashin tsoron SHAHEED da ya iya yanke hukunci a kan yar sarki, jikar sarki kai tsaye haka, ta ji tausayin NADIA matuka, harma ta baiwa kanwarta shawarar dan Allah kar ta yi fada da Nadia

NAJEEBA ta sauke ajiyar zuciya bata ce komai ba har suka kashe

Sai bayan sun kashe ta yi shiru tana nanata sunnan Nadia a saman lebenta
Bakinta ta dan tabe ta mike ta dauki hijab ta saka ta kashe komai ta nufi bangaren AMMI hankali kwonce ko kari bata tsaya dubawa ba da ake ajiyewa karfe takwas

Ai kau tana zuwa ta tarar da su yau a saman cafet suke sunna cin abinci hankali kwonce

Gaishe da iyayen ta yi cike da kulawa suka amsata, ta cire hijab din ta yi wuli da shi saman kujera ta zauna hankali kwonce sannan ta zuba abinci a plate ta kai dubanta wajen yayunta ta ce " An gaishe ku "

Daria suka saka kasa kasa jin irin gaisuwar nan ta bosawa wai An gaishe ku

Sai dai basu gama dariar ba, da murya na yi mata rawa ta ce" iiina kwana NAJEEBA "
Chapter 117 · 0% Book details