Sashe 61
Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wayar ya bi ya wawura dan kuma kaiwa kunnansa yana mai zubewa k'asa tamkar yana gaban Shaheed d'in hakama d'an uwansa na ganin wannan lamari yayi tunanin lalle wani babba ne a fadar yayi kira idan ba amintacen sarki ba to fa wani babba ne shi baima kawo cewar sarkin ne ba.
"A kashe , ya kashe, Attahir shikenan, dawama a cikin gidan kurkukun k'urya ya tabbata a garemu, GURNANIN ZAKI ne ya kira wayana da kansa kuma hankulanmu tashe ban duba ba na daga du ya ji abubuwan da muke fad'a."
Zuciyarsa ya dafe cikin tashin hankali yana jin cikinsa na murd'awa dan mad'aukakiyar tashin hankalin da ya hangowa kansu harma bakinsa ya kasa furta komai.
Mik'ewa yayi ya damk'i hannunsa yace " Tashi mu kuma bin waje wajen da ta saba zuwa, dan ina mai rantse maka ba zamu taba komawa fada ba tare da ita ba!"
Murmushi tayi da jus d'in dake ajiye saman lafiyayen table din da aka jera masu kayan k'walam da mak'ulashe.
Cikin wani irin shauk'inta yake , cikin dabara yake d'an k'ara kusanta kansa da ita yana mai kasheta da kallon soyaya.
Cike da farin cikin ganinta yace "Ban san a kan wani dalili yayanmu ya hana mu ganin junna ba, yace min zai waiwayeni har yanzu shiru, Najeeba ina jin tsoron kar a je ya hana min ke?"
Najeeba ta dan yi murmushi bata ce masa komai ba, hankalinta du yana kan agogonta so take ta mike aman kuma kar ya ga tana wulakantashi da yawa bayan uban nacin da ya ringa mata su hadu koda wani wajen ne bukatarsa ya ganta ya yi missing din kyakyawar fuskarta fiye da tunaninta hakan ya sa ta tsara fitarta yau du ta ringa yarda da yan kwaliya da masu gyaran jiki tun safe take cin wahalalen aiki wajen ya rikice sai shiga ake ana fita sannan ta ki kunna fitilar waje, sai da wajen ya zama sun daina duba wanda zai fita ko wada zata shiga tana hankalce da su kafin suka cenza sutura da AIDA ta fice fittt tamkar Aidar ce ta fita dan takan aiki Aidar siyo wani abin
"Lokacin komawarki ya yi ko?" Ya tambayeta cike da kulawa.
Najeeba ta sakar masa murmushi tace " Ka san doka ce, kayi hak'uri ina ji a jikina zai waiwayeka soon."
Murmushi yayi yana mai jin dad'i har abokansa ya gayyata su ganewa idanuwansa dan su yarda cewar shi d'in fa ba k'aramin k'waro bane, yau shine ya kawo NAJEEBA restaurant.
Mik'ewar da tayi da doguwar rigar AIDA jikinta du bata jin dad'in kasancewarta a cikin rigar mutane ya saka shi mik'ewa shima yana kallon table d'in yace "Baby baki ci komai ba fa?"
Najeeba ta d'an girgiza kanta da jus d'in hannunta tace "Ba ga Jus na sha ba? Ka san bana iya cin abu a gaban mutane haka bana jin dad'in ci."
Murmushi yayi ya d'auki wani croissant ya nufi bakinta da shi.
Sai kawai ta kula kamar an yawaita kallonsu ba mazan ba matan wanda bata san dalilin hakan ba ko dan bata saba zuwa irin wajen takanas ta zauna ta ci abinci bane? Takan zo Abusa restaurant aman ba dan ta zauna ba, daga cikin motarta ake mik'o mata dukan abinda ta buk'ata , aman yau ita Najeeba dan ta farantawa saurayi ta shigo d'are d'are ta zauna saman kujera, hakan ya hanna mata nutsuwa jinta take tamkar a saman k'aya du bata fahimtar abubuwan da yake fad'a.
Murmushi yayi, shi baban soyayya ya kai bakinsa ya gutsura ya tauna ya had'iye yace " Ko tsoro kike a je na saka wani abu a ciki?"
Najeeba tayi yak'e tana d'an zama gefe tana d'an waige waige a sanyaye tace "Huzaifa tafia zan yi dare fa ya yi."
Murmushi yayi yace "Dan Allah manta da wani dare yayi, babbar yarinya da ke za'a wani d'ora maki dokar dawowa gida da wuri sai kace wata yar daji?"
D'an tsai tayi tana kallonsa, a k'asan zuciyarta kuwa fad'i take lallai baka da wayo, ai wayewar tawa bata kai wajen da zan iya bijirewa Gimbiya ba, sai ta daki hak'oran banza a zauna k'alau.
Ambatar Gimbiya da tayi ya sakata jin gabanta ya fad'i, firgigita tayi ta shiga wawurar jakarta mai d'auke da wayarta.
Dubawa tayi dan ganin ina wayar? Sai dai cikin ikon Allah bata ciki, hankalinta ne ya tashi ta mik'e da sauri ta kama hanyar fita.
Shima mik'ewar yayi yana mik'awa abokinsa wayarta da ya zare, ya yiwa kansa alk'awarin zai je ya binciki wayarta du wani d'an iskan saurayinta dake mata magana ya d'ud'ura masa ashar da zumar itace sanan ya masa kashedin sake shiga hanyarta, zai shiga wajen hotunanta da vidos dinta ya tura wa'inda sukai masa kafin ya yarda wayar ya siya mata sabuwa _(HATARA dai yan matanmu, waya ta zama balaki, tashin hankali, fitinar dake hanna kwonciyar hankali a wannan zamani, wasu yan matan kan yarda su ringa d'aukan hotunan wasu sasa na jikinsu haka kawai suna bari a cikin wayarsu wasun kuwa samarinsu suke turawa, zaka ga budurwa ta yi hoto rabin nonowanta a fili harshe a waje tamkar wata karya da k'walelen kai a fili tana wani langwab'ewa ita ga kyakyawa ta ajiye a allon wayarta, shin k'anwata, yayata, y'ata idan wayarki ta fad'i a titi ya kasance wani mugu ya tsinceta ya je ya yi anfani da abubuwan dake ciki, ciki kuwa harda munanan hotunan nan naki ina zaki shiga da ranki? Wani saurayin ya zo gidanku ne dan ya lalata tarbiyar iyayenki ya yi tafiarsa, wani ya zo ne dan ya wulakanta ki ya kara gaba, ciki d'aid'aiku ne suka zo dan soyaya idan wayarki ta fad'a hannun wanda kike wulak'antawar nan ya je ya fitar da vidio d'inki kina wasu irin abubuwa ke ba yar bariki ba ke ba mahaukaciya ba yaya kike tunanin zai yi da su? Dan Allah mu rufawa kanmu asiri da lamarin nan, wallahi, wallahi idan wani abu bai tona mana asiri ba wayoyinmu zasu tona mana Allah ya kare mu baki d'aya)._ Bayanta ya biyo da sauri.
Kusan motarsa take tsaye tana son bud'ewa.
Ta bayanta ya zagayo ya rungumeta a jikinsa hakan ya saka gabanta ya yanke ya fad'i harma jikinta ya fara b'ari b'ari.
Da sauri ta ringa kiciniyar k'wacewa hakan yasa ya k'ara ruk'unk'umeta a jikinsa a sanyaye yana furta " Baby meye haka? Ki tsaya na ji d'umin jikinki a jikina, ba wani abu zamu yi da ke ba sai an mana aure aman irin yar rungumar nan ba zan samu ba? Ki duba fa ki ga irin yanda wasu ke tsotsar bakin junna wa'inda basuma kaimu wayewa ba aman ke sai ki ringa guduna?"
"Innalilahi wa'ina ilaihi raj'une ..." Najeeba ta fad'a da k'arfin gaske kafin ta tura shi tayi baya baya ya gamu da jikin motar.
Da sauri ya saketa gannin zata tara masa mutane yana kallonta da mamaki.
Rasa me ma zata yi ta yi, yanzu Huzaifa ne ya ruk'unk'ume mata jiki haka ya d'ora mata kai a wuyanta Idannuwanta ta lumshe tana jin wata tsanarsa na mamaye gurbin birgetan da ya fara.
A sanyaye tace "Wai ko wani namijin ma d'an iska ne, ko dai nice mai sifar yan iskan da bana iya tarayya sai da d'an iska? Wai kowa haka yake soyaya ko matar da zaka aura sai ka nuna mata akuyanci?"
"HUZAIFA." Ta fad'a a sanyaye hawaye tuni ya fara wanke mata fuskarta tace "Dama dan ka d'ana jikina ka shigo jikina har ka saka na kamu da soyayarka?"
Huzaifa yayi gagawar girgiza kansa ya mik'o hannunsa dan tab'a nata aman sai ta kauce da sauri tana kallonsa, shi yama rikice sam bai d'auki haka a matsayin wata damuwa ba, a kan me zata wani damu daga yar runguma, yo yan matan yanzu meye ba'a yi da su? Aman ita daga yar runguma ta kama kuka haka me take nufi da shi?
A sanyaye yace "Najeeba, ba fa wani abu na maki ba, rungumeki na yi a jikina wanda yanzu hakan ba wani abu bane , Najeeba aurenki fa zan yi ko kin manta?"
Najeeba ta d'an lumshe idanuwanta tana d'an girgiza kanta a hankali tace "Da ace ina yarda da rungume rungumen nan da baka tardo ni a haka ba, Huzaifa da ace ban d'auki irin haka a bakin komai ba da ina ga cikin biyu an yi d'aya, ko duniya ta d'ad'a ni da k'asa ko kuwa ina wani wajen da kai baka isa ka hango ni ba, dan na rantse maka tun ina da shekara goma sha hud'u nake tara samari, Huzaifa da ace na biyewa samari mun ringa soyayar zamanin da kake fad'a da na tara y'aya da yawa a duniya, duniyar ta gama yayina ko na zama rik'ak'iyar yar barikin da ba dai k'ananun yara ba sai manya." Tana gama fad'a ta juya a hankali ta shiga tafia a k'afarta.
Huzaifa ya waiga ya ga abokansa biyu na lek'e hakan ya saka ya ji kamar ya k'urma ihu a wajen ( kai, ta zo maka da sauki baka sha mari ba?)
Me ya sa ta masa haka? Shi sam bai ga wani abinda yayi na laifi ba, koda yake zai je ya gama aiyukan da zai yi a wayarta sannan ya je saloon dinta gobe ya shiga koda da gudu ne ya bata hak'uri, zata sauko ne abinda ta fad'a da bakinta cewar ta kamu da son sa?.
Sam bai bi bayanta ba, itama hakan ya fi mata alkhairi tana tafe tana share hawaye ta bi ta gaban comisaria ta kama tudun poste a k'afarta tana tafe tana had'a hanya tamkar zata fad'i k'asa.
Ficewarsu biyu ta hanyar da take bi aman sun kasa ganeta, sai da suka dawo da wani irin gudu suka lura da budurwar dake tafe tana had'a layi kasancewar hanyar itane hanyarta ta bi kullum idan zata koma fada.
Wani irin birki suka ci a gabanta, da sauri d'ayan ya fito hankalinsa tashe ganninta tana ta hawaye gashi ba kayanta ne a jikinta ba.
"A kashe , ya kashe, Attahir shikenan, dawama a cikin gidan kurkukun k'urya ya tabbata a garemu, GURNANIN ZAKI ne ya kira wayana da kansa kuma hankulanmu tashe ban duba ba na daga du ya ji abubuwan da muke fad'a."
Zuciyarsa ya dafe cikin tashin hankali yana jin cikinsa na murd'awa dan mad'aukakiyar tashin hankalin da ya hangowa kansu harma bakinsa ya kasa furta komai.
Mik'ewa yayi ya damk'i hannunsa yace " Tashi mu kuma bin waje wajen da ta saba zuwa, dan ina mai rantse maka ba zamu taba komawa fada ba tare da ita ba!"
Murmushi tayi da jus d'in dake ajiye saman lafiyayen table din da aka jera masu kayan k'walam da mak'ulashe.
Cikin wani irin shauk'inta yake , cikin dabara yake d'an k'ara kusanta kansa da ita yana mai kasheta da kallon soyaya.
Cike da farin cikin ganinta yace "Ban san a kan wani dalili yayanmu ya hana mu ganin junna ba, yace min zai waiwayeni har yanzu shiru, Najeeba ina jin tsoron kar a je ya hana min ke?"
Najeeba ta dan yi murmushi bata ce masa komai ba, hankalinta du yana kan agogonta so take ta mike aman kuma kar ya ga tana wulakantashi da yawa bayan uban nacin da ya ringa mata su hadu koda wani wajen ne bukatarsa ya ganta ya yi missing din kyakyawar fuskarta fiye da tunaninta hakan ya sa ta tsara fitarta yau du ta ringa yarda da yan kwaliya da masu gyaran jiki tun safe take cin wahalalen aiki wajen ya rikice sai shiga ake ana fita sannan ta ki kunna fitilar waje, sai da wajen ya zama sun daina duba wanda zai fita ko wada zata shiga tana hankalce da su kafin suka cenza sutura da AIDA ta fice fittt tamkar Aidar ce ta fita dan takan aiki Aidar siyo wani abin
"Lokacin komawarki ya yi ko?" Ya tambayeta cike da kulawa.
Najeeba ta sakar masa murmushi tace " Ka san doka ce, kayi hak'uri ina ji a jikina zai waiwayeka soon."
Murmushi yayi yana mai jin dad'i har abokansa ya gayyata su ganewa idanuwansa dan su yarda cewar shi d'in fa ba k'aramin k'waro bane, yau shine ya kawo NAJEEBA restaurant.
Mik'ewar da tayi da doguwar rigar AIDA jikinta du bata jin dad'in kasancewarta a cikin rigar mutane ya saka shi mik'ewa shima yana kallon table d'in yace "Baby baki ci komai ba fa?"
Najeeba ta d'an girgiza kanta da jus d'in hannunta tace "Ba ga Jus na sha ba? Ka san bana iya cin abu a gaban mutane haka bana jin dad'in ci."
Murmushi yayi ya d'auki wani croissant ya nufi bakinta da shi.
Sai kawai ta kula kamar an yawaita kallonsu ba mazan ba matan wanda bata san dalilin hakan ba ko dan bata saba zuwa irin wajen takanas ta zauna ta ci abinci bane? Takan zo Abusa restaurant aman ba dan ta zauna ba, daga cikin motarta ake mik'o mata dukan abinda ta buk'ata , aman yau ita Najeeba dan ta farantawa saurayi ta shigo d'are d'are ta zauna saman kujera, hakan ya hanna mata nutsuwa jinta take tamkar a saman k'aya du bata fahimtar abubuwan da yake fad'a.
Murmushi yayi, shi baban soyayya ya kai bakinsa ya gutsura ya tauna ya had'iye yace " Ko tsoro kike a je na saka wani abu a ciki?"
Najeeba tayi yak'e tana d'an zama gefe tana d'an waige waige a sanyaye tace "Huzaifa tafia zan yi dare fa ya yi."
Murmushi yayi yace "Dan Allah manta da wani dare yayi, babbar yarinya da ke za'a wani d'ora maki dokar dawowa gida da wuri sai kace wata yar daji?"
D'an tsai tayi tana kallonsa, a k'asan zuciyarta kuwa fad'i take lallai baka da wayo, ai wayewar tawa bata kai wajen da zan iya bijirewa Gimbiya ba, sai ta daki hak'oran banza a zauna k'alau.
Ambatar Gimbiya da tayi ya sakata jin gabanta ya fad'i, firgigita tayi ta shiga wawurar jakarta mai d'auke da wayarta.
Dubawa tayi dan ganin ina wayar? Sai dai cikin ikon Allah bata ciki, hankalinta ne ya tashi ta mik'e da sauri ta kama hanyar fita.
Shima mik'ewar yayi yana mik'awa abokinsa wayarta da ya zare, ya yiwa kansa alk'awarin zai je ya binciki wayarta du wani d'an iskan saurayinta dake mata magana ya d'ud'ura masa ashar da zumar itace sanan ya masa kashedin sake shiga hanyarta, zai shiga wajen hotunanta da vidos dinta ya tura wa'inda sukai masa kafin ya yarda wayar ya siya mata sabuwa _(HATARA dai yan matanmu, waya ta zama balaki, tashin hankali, fitinar dake hanna kwonciyar hankali a wannan zamani, wasu yan matan kan yarda su ringa d'aukan hotunan wasu sasa na jikinsu haka kawai suna bari a cikin wayarsu wasun kuwa samarinsu suke turawa, zaka ga budurwa ta yi hoto rabin nonowanta a fili harshe a waje tamkar wata karya da k'walelen kai a fili tana wani langwab'ewa ita ga kyakyawa ta ajiye a allon wayarta, shin k'anwata, yayata, y'ata idan wayarki ta fad'i a titi ya kasance wani mugu ya tsinceta ya je ya yi anfani da abubuwan dake ciki, ciki kuwa harda munanan hotunan nan naki ina zaki shiga da ranki? Wani saurayin ya zo gidanku ne dan ya lalata tarbiyar iyayenki ya yi tafiarsa, wani ya zo ne dan ya wulakanta ki ya kara gaba, ciki d'aid'aiku ne suka zo dan soyaya idan wayarki ta fad'a hannun wanda kike wulak'antawar nan ya je ya fitar da vidio d'inki kina wasu irin abubuwa ke ba yar bariki ba ke ba mahaukaciya ba yaya kike tunanin zai yi da su? Dan Allah mu rufawa kanmu asiri da lamarin nan, wallahi, wallahi idan wani abu bai tona mana asiri ba wayoyinmu zasu tona mana Allah ya kare mu baki d'aya)._ Bayanta ya biyo da sauri.
Kusan motarsa take tsaye tana son bud'ewa.
Ta bayanta ya zagayo ya rungumeta a jikinsa hakan ya saka gabanta ya yanke ya fad'i harma jikinta ya fara b'ari b'ari.
Da sauri ta ringa kiciniyar k'wacewa hakan yasa ya k'ara ruk'unk'umeta a jikinsa a sanyaye yana furta " Baby meye haka? Ki tsaya na ji d'umin jikinki a jikina, ba wani abu zamu yi da ke ba sai an mana aure aman irin yar rungumar nan ba zan samu ba? Ki duba fa ki ga irin yanda wasu ke tsotsar bakin junna wa'inda basuma kaimu wayewa ba aman ke sai ki ringa guduna?"
"Innalilahi wa'ina ilaihi raj'une ..." Najeeba ta fad'a da k'arfin gaske kafin ta tura shi tayi baya baya ya gamu da jikin motar.
Da sauri ya saketa gannin zata tara masa mutane yana kallonta da mamaki.
Rasa me ma zata yi ta yi, yanzu Huzaifa ne ya ruk'unk'ume mata jiki haka ya d'ora mata kai a wuyanta Idannuwanta ta lumshe tana jin wata tsanarsa na mamaye gurbin birgetan da ya fara.
A sanyaye tace "Wai ko wani namijin ma d'an iska ne, ko dai nice mai sifar yan iskan da bana iya tarayya sai da d'an iska? Wai kowa haka yake soyaya ko matar da zaka aura sai ka nuna mata akuyanci?"
"HUZAIFA." Ta fad'a a sanyaye hawaye tuni ya fara wanke mata fuskarta tace "Dama dan ka d'ana jikina ka shigo jikina har ka saka na kamu da soyayarka?"
Huzaifa yayi gagawar girgiza kansa ya mik'o hannunsa dan tab'a nata aman sai ta kauce da sauri tana kallonsa, shi yama rikice sam bai d'auki haka a matsayin wata damuwa ba, a kan me zata wani damu daga yar runguma, yo yan matan yanzu meye ba'a yi da su? Aman ita daga yar runguma ta kama kuka haka me take nufi da shi?
A sanyaye yace "Najeeba, ba fa wani abu na maki ba, rungumeki na yi a jikina wanda yanzu hakan ba wani abu bane , Najeeba aurenki fa zan yi ko kin manta?"
Najeeba ta d'an lumshe idanuwanta tana d'an girgiza kanta a hankali tace "Da ace ina yarda da rungume rungumen nan da baka tardo ni a haka ba, Huzaifa da ace ban d'auki irin haka a bakin komai ba da ina ga cikin biyu an yi d'aya, ko duniya ta d'ad'a ni da k'asa ko kuwa ina wani wajen da kai baka isa ka hango ni ba, dan na rantse maka tun ina da shekara goma sha hud'u nake tara samari, Huzaifa da ace na biyewa samari mun ringa soyayar zamanin da kake fad'a da na tara y'aya da yawa a duniya, duniyar ta gama yayina ko na zama rik'ak'iyar yar barikin da ba dai k'ananun yara ba sai manya." Tana gama fad'a ta juya a hankali ta shiga tafia a k'afarta.
Huzaifa ya waiga ya ga abokansa biyu na lek'e hakan ya saka ya ji kamar ya k'urma ihu a wajen ( kai, ta zo maka da sauki baka sha mari ba?)
Me ya sa ta masa haka? Shi sam bai ga wani abinda yayi na laifi ba, koda yake zai je ya gama aiyukan da zai yi a wayarta sannan ya je saloon dinta gobe ya shiga koda da gudu ne ya bata hak'uri, zata sauko ne abinda ta fad'a da bakinta cewar ta kamu da son sa?.
Sam bai bi bayanta ba, itama hakan ya fi mata alkhairi tana tafe tana share hawaye ta bi ta gaban comisaria ta kama tudun poste a k'afarta tana tafe tana had'a hanya tamkar zata fad'i k'asa.
Ficewarsu biyu ta hanyar da take bi aman sun kasa ganeta, sai da suka dawo da wani irin gudu suka lura da budurwar dake tafe tana had'a layi kasancewar hanyar itane hanyarta ta bi kullum idan zata koma fada.
Wani irin birki suka ci a gabanta, da sauri d'ayan ya fito hankalinsa tashe ganninta tana ta hawaye gashi ba kayanta ne a jikinta ba.