Sashe 130
Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai da ya kara kausasa muryarsa ya ce" du wanda ya farka ya dawo kusa da kujerar nan ya zauna, bana son na ji ihun kuka ko magangannun da basu da tsari, soyaya kuke yiwa yar kanwarku? Ku rakata da adu'a, ita ta bara mana duniyar, da ta tafi bata yi gagawa ba, mu dake raye bamu yi jinkiri ba, du zata dauke mu ne koda kuwa bama so!"
Dubansa ya maida wajen sarkin dogarai cike da juriya dan kar yan uwansa su ga gazawarsa abin ya lalace ya ce" ka bada sanarwar jana'izar NUSAIBA"
Wannan mutuwa ta Nusaiba ta girgiza al'umar damagaram, daga bakin lokacin da aka gama zana'izarta aka dora zaman makoki gidan ya ringa dinkewa da al'umah na nesa da na kusa, mutuwar kankannuwar yarinya ta samu halartuwar jama'a tamkar zasu fasa gidan sarautar
Dangin MARDIYA daga bakin lokacin da suka ji takamaiman abinda ya faru sai kunya ta hade su, mahaifiyarta ta yi kuka, ta yi kuka, ta sanarwa Allah, sun hadu su dukansu sun kai gaisuwa sun kuma nemi afuwa cike da jin kunya kafin mahaifiyarta ta kara yiwa Abih gaisuwa, ta nemi afuwarsa sannan ta dora da fadin" Tabas du wanda ya ce a duniya son ransa zai bi karshensa nadama, yau gashi Mardiya taurin kanta, da jajircewarta dan gannin wani ya halaka ta halaka kanta da kanta, a yau Marfiya ta tashi a banza babu gidan mijin babu yar da zata iya tunata ta yi mata adu'a, kaya, nima tawa kadarar harda haihuwar MARDIYA, ta tsananta kishi, abin ya dawo bakin ciki, ta zamanto bata san alkhairi ba, ta so duniya, duniya ta bata sakamako, tsakanina da ahalin Mutalab sai kyakyawar adu'a, har gobe ni din mai bin ku da kyakyawar adu'a ce" ta karashe tana mai fashewa da kuka, Abih da har yanzu bai samu kukan ba kansa kawai ya ringa dan girgizawa, sai dogarai ke bada amsa a haka suka bar gidan suka koma gidansu dan ba abinda zasu ci da Mardiya, hukunci ya hau kanta, hakan zai zamo ishara ga du wata mai taurin hali irin nata!
Sai da suka dauki sati biyu sunna zaman makokin NUSAIBA kafin kafa ta dauke
A wannan ranar ce Sultan ya bada umarnin UMMU ta fito ta je gidanta
Basu musa ba, ama y'ayan nata yan matan ne kawai suka zauna domin baki daya sauran bin bayanta suka yi suka cika motar DAYABU ya tuka su har sabon gidan
Sunna zuwa DAYABU ya shiga nununa masu kowa wajen da yake nasa, nan ya kara zubar da hawaye a lokacin d aya kawo kan gadon Nusaiba, sai da ya yi mai isarsa sannan ya share hawayensa ya yi mata adu'a
.............morning....................
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
66
A hankali UMMU ta idasa bakin bed din da Abih ke kwonce, royal bed ne rantsatse wanda ya amsa sunnansa, idannuwansa a rufe suke tamkar mai baci, sai dai ba baci yake yi ba,
Cikin nutsuwa ta saka hannunta ta janyo farar takardar dake ciki
Warwareta ta yi ta karanta,
Fuskarta dauke da yannayi na rashin jin dadi ta ajiye nan gefe domin igiya dayar da ta yi saura tsakaninsa da Mardiya ne ya tsinke
Sannu sannu ta haura saman gadon
Hannunsa daya dake kusa da idannuwansa ta kamo cikin nata, a hankali ta furta" Gani na zo Aban Dayabu, ka buda idannuwanka , ka fada min dukan abubuwan da suka faru da kai tsayin shekarun nan, ka fada min wanda ya bata maka ni kuwa zan je mu gwada karfi da shi komai girman tsayinsa da karfinsa"
A hankali ya ringa sauke ajiyar zuciya kafin ya kamo hannunta ya dora gefen fuskarsa yana mai kurawa fuskarta ido, sannan yana mai jin sanyi na ratsa dukan zuciyarta da tunaninsa, muryarsa a shake ya ce" Ki dawama da ni har karshen numfashina NANA, ki zame mana uwa baki daya Nana, walahi na ga rayuwa, ba zan sake fade fade ba Nana "
Idannuwanta ta lumshe a hankali ta kara matsawa kusa da shi kafin ta shige jikinsa ta lumshe idannuwanta bata ce da shi komai ba
Shima idannuwan nasa ya lumshe dan ya amsar kennan, wato ta aminta, kuma ta dawo gare shin kennan, baci ya shiga nema domin rabonsa da bacin har ya manta sai barawon dake fuzgarsa ya dan taba ya farka tsabar damuwa
A washe gari aka tafi da MARDIYA, domin koda kuwa labarin mutuwar ya nuna ba da gangan ta kashe y'arta ba hukuma ta ki aminta da haka, sun tafi da ita sai yanda hali ya yi (Ku mu saba da dane zuciyoyinmu, ku mu ringa yiwa kawunnanmu adu'a kan Allah ya sa mu fi karfin zukatanmu)
A hankali abubuwa suka fara komawa gurbinsu, du mutane suka kama gabansu ciki harda Zahrau da yarima da dayar kishiyarta
Sosai yayan Ammi suka yi sanyi da rayuwa, barema Ummulkhair, ta jima tana nisa cewar a bayanta Nusaiba ta rasu, sai Najeeba da take dan fama da zazabin dare da kewar kanwarta
Nadia a wajen take wuni sai dare take tafia bangarenta
Sultan kam ido ya kawo ya zubawa ikon Allahn Najeeba, rabonsa da wani kusanci tsakaninsa da ita tun shinfidetan da ya yi a kan babar kujera
Ya rasa ina take shiga da idannuwansa suke gaza ganninta, kwata kwata ta yiwa ganninsa tsada, yakan sauke ajiyar zuciya ya dan girgiza kansa kawai, domin yana yiwa al'amuranta uzuri, lalle tana da tata hujar
Ita kanta Nadiar lokaci ya barta har ta kara warwarewa, iyayenta sun zo sosai haka kanwar mamanta na nan har zuwa lokacin
A hankali komai ya dawo normal, ya rage samun mutane a kai a kai na gaisuwa
Ya zamanta ya koma rayuwa yanda yake yi, a hankali komai ya ringa daidaituwa har du wani tunani nasa ya dawo jikinsa
Sannu sannu rashinta a kusa da shi ya fara tasiri
Sati uku kennan da rasuwar Nusaiba abin ya gama kama jinni da jikinsa
Bilhaki a yanzun kewarta yake, idan ya tuna magangannunsu da ita kuwa irin furucinta yakan ji tamkar an dake shi da karfe mai karfi a dukan gabobin jikinsa, da ace zata kasance mai yi masa uzuri da ta gane ta taka matsayin da ba wace ta taba takawa a duniya, da ace zata iya ganewa da ta ture du wani abin sun zauna, bai je mata da wata magana ba sai dan ya yaba, bai je mata da rokon ta gyara kawarta kuma yar uwarta ba sai dan ya jita daban, ba cin fuska bane, yabo ne
Yakan girgiza kansa, a hankali ya furta" Ban yi haka da sanina ba BEEBAH "
Sai ya shafa gemun dake habarsa a hankali ya ce" da ace zaki yarda, da na furta maki irin ilar da kika gama yiwa rayuwata Beebah, kin kai wajen da nakan ji a kasan zuciyata cewar ba zan iya babu ke ba"
Wayarsa ya dauko a karo na bakwai kennan da zai tura mata mesage ba amsa, shi kansa tun abin na bashi mamaki har ya dawo ya daina bashi mamaki irin yanda yake da naci a kan lamarinta, shine zaune da aikin yiwa mace message, shi da ko aurenki zai yi mai zuwa ya masa zancen daban shi kawai sai an kawo ki zaku hade, dan murmushi ya yi
A hankali ya dora dogayen yatsutsansa ya shiga taping din message kamar haka" Kin manta da bawan Allah ne? Ki bani amsa alfarmar rasululah S.A.W "
Sai da ta amsa da sallalahu alaihi wa salam, kafin ta tura masa da salama
Ajiyar zuciya ya yi yana kallon salamar kamar wani dogon message mai dadi kafin ya dora da fadin" Ina muradin gannin matata, ko zan samu wannan alfarmar? "
Bata maida masa da amsa ba sai kurawa Nadia ido da ta yi wace ke ta ciye ciye abinta, sam yanzun ta sake da mutanen gidan tana cudanya da su tamkar yan uwanta na jinni, sannan ko tsakaninta da Najeebar sukan taba hira, maganar sirri ce ta kau, basa wani sirrin junna irin na da
Mikewa ta yi ta shige ciki
Katon hijab ta sanyo hade da nikaf ta fito
Wajen Ammi ta je ta dan duka ta yi mata magana sannan ta mike ta yi gaba
Saloon dinta ta nufa
Tana shiga ta je ta zauna su Aida suka saki aikin da suke yi suka bita dakin da ta shige
Umarnin su gama ta basu sannan ta fara tsife kitson kanta da ya tsufa
Sai bayan sun gama ne suka rufu a kanta, wasu na tsifar kan, wasu na wanke mata kafa da akaifu, daya na gyara mata akaifun hannu , mai kunshi na hada kunshin da zata yi mata dan kadan ba mai yawa ba iya hannayenta
Ba ita ta bar saloon din nan ba sai da yama sosai kafin ta koma bangaren AMMI
A cenma wanka ta shige cikin nutsuwa ta gama kimtsa jikinta cikin lalausan lesh ja mai adon baki a jikinsa kafin ta fito hannunta rike da dan mayafi ruwan baki sidik mai shara shara
Ido kawai AMMI ta zuba mata, kalar fatar jikinta wani sheki take kara yi tamkar ta rihana, a yanzun sai ta kara budewa ko dan abinda suke zargin tana dauke da shi ne?
Kiraye kirayen salar isha ya sakata daukan hijab din AMMI ta gabatar da sallar sannan ta zauna nan sunna dan taba hira
Sai da karfe tara ta yi ne Ammi ta kuma kallonta a karro na ba adadi , muryarta sanyaye ta ce" NAJEEBA, tashi ki tafi mana "
NAJEEBA ta dan yi murmushin, ita kanta ta kusan minti ashirin tana saka ta tashin to sai ta kasa tashin, dan haka ta mike
Har ta fara tafia AMMI ta ce" Kar ki manta, k8 fada masa gobe in sha Allah zaki koma bangarenki kin ji? "
Dubansa ya maida wajen sarkin dogarai cike da juriya dan kar yan uwansa su ga gazawarsa abin ya lalace ya ce" ka bada sanarwar jana'izar NUSAIBA"
Wannan mutuwa ta Nusaiba ta girgiza al'umar damagaram, daga bakin lokacin da aka gama zana'izarta aka dora zaman makoki gidan ya ringa dinkewa da al'umah na nesa da na kusa, mutuwar kankannuwar yarinya ta samu halartuwar jama'a tamkar zasu fasa gidan sarautar
Dangin MARDIYA daga bakin lokacin da suka ji takamaiman abinda ya faru sai kunya ta hade su, mahaifiyarta ta yi kuka, ta yi kuka, ta sanarwa Allah, sun hadu su dukansu sun kai gaisuwa sun kuma nemi afuwa cike da jin kunya kafin mahaifiyarta ta kara yiwa Abih gaisuwa, ta nemi afuwarsa sannan ta dora da fadin" Tabas du wanda ya ce a duniya son ransa zai bi karshensa nadama, yau gashi Mardiya taurin kanta, da jajircewarta dan gannin wani ya halaka ta halaka kanta da kanta, a yau Marfiya ta tashi a banza babu gidan mijin babu yar da zata iya tunata ta yi mata adu'a, kaya, nima tawa kadarar harda haihuwar MARDIYA, ta tsananta kishi, abin ya dawo bakin ciki, ta zamanto bata san alkhairi ba, ta so duniya, duniya ta bata sakamako, tsakanina da ahalin Mutalab sai kyakyawar adu'a, har gobe ni din mai bin ku da kyakyawar adu'a ce" ta karashe tana mai fashewa da kuka, Abih da har yanzu bai samu kukan ba kansa kawai ya ringa dan girgizawa, sai dogarai ke bada amsa a haka suka bar gidan suka koma gidansu dan ba abinda zasu ci da Mardiya, hukunci ya hau kanta, hakan zai zamo ishara ga du wata mai taurin hali irin nata!
Sai da suka dauki sati biyu sunna zaman makokin NUSAIBA kafin kafa ta dauke
A wannan ranar ce Sultan ya bada umarnin UMMU ta fito ta je gidanta
Basu musa ba, ama y'ayan nata yan matan ne kawai suka zauna domin baki daya sauran bin bayanta suka yi suka cika motar DAYABU ya tuka su har sabon gidan
Sunna zuwa DAYABU ya shiga nununa masu kowa wajen da yake nasa, nan ya kara zubar da hawaye a lokacin d aya kawo kan gadon Nusaiba, sai da ya yi mai isarsa sannan ya share hawayensa ya yi mata adu'a
.............morning....................
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
66
A hankali UMMU ta idasa bakin bed din da Abih ke kwonce, royal bed ne rantsatse wanda ya amsa sunnansa, idannuwansa a rufe suke tamkar mai baci, sai dai ba baci yake yi ba,
Cikin nutsuwa ta saka hannunta ta janyo farar takardar dake ciki
Warwareta ta yi ta karanta,
Fuskarta dauke da yannayi na rashin jin dadi ta ajiye nan gefe domin igiya dayar da ta yi saura tsakaninsa da Mardiya ne ya tsinke
Sannu sannu ta haura saman gadon
Hannunsa daya dake kusa da idannuwansa ta kamo cikin nata, a hankali ta furta" Gani na zo Aban Dayabu, ka buda idannuwanka , ka fada min dukan abubuwan da suka faru da kai tsayin shekarun nan, ka fada min wanda ya bata maka ni kuwa zan je mu gwada karfi da shi komai girman tsayinsa da karfinsa"
A hankali ya ringa sauke ajiyar zuciya kafin ya kamo hannunta ya dora gefen fuskarsa yana mai kurawa fuskarta ido, sannan yana mai jin sanyi na ratsa dukan zuciyarta da tunaninsa, muryarsa a shake ya ce" Ki dawama da ni har karshen numfashina NANA, ki zame mana uwa baki daya Nana, walahi na ga rayuwa, ba zan sake fade fade ba Nana "
Idannuwanta ta lumshe a hankali ta kara matsawa kusa da shi kafin ta shige jikinsa ta lumshe idannuwanta bata ce da shi komai ba
Shima idannuwan nasa ya lumshe dan ya amsar kennan, wato ta aminta, kuma ta dawo gare shin kennan, baci ya shiga nema domin rabonsa da bacin har ya manta sai barawon dake fuzgarsa ya dan taba ya farka tsabar damuwa
A washe gari aka tafi da MARDIYA, domin koda kuwa labarin mutuwar ya nuna ba da gangan ta kashe y'arta ba hukuma ta ki aminta da haka, sun tafi da ita sai yanda hali ya yi (Ku mu saba da dane zuciyoyinmu, ku mu ringa yiwa kawunnanmu adu'a kan Allah ya sa mu fi karfin zukatanmu)
A hankali abubuwa suka fara komawa gurbinsu, du mutane suka kama gabansu ciki harda Zahrau da yarima da dayar kishiyarta
Sosai yayan Ammi suka yi sanyi da rayuwa, barema Ummulkhair, ta jima tana nisa cewar a bayanta Nusaiba ta rasu, sai Najeeba da take dan fama da zazabin dare da kewar kanwarta
Nadia a wajen take wuni sai dare take tafia bangarenta
Sultan kam ido ya kawo ya zubawa ikon Allahn Najeeba, rabonsa da wani kusanci tsakaninsa da ita tun shinfidetan da ya yi a kan babar kujera
Ya rasa ina take shiga da idannuwansa suke gaza ganninta, kwata kwata ta yiwa ganninsa tsada, yakan sauke ajiyar zuciya ya dan girgiza kansa kawai, domin yana yiwa al'amuranta uzuri, lalle tana da tata hujar
Ita kanta Nadiar lokaci ya barta har ta kara warwarewa, iyayenta sun zo sosai haka kanwar mamanta na nan har zuwa lokacin
A hankali komai ya dawo normal, ya rage samun mutane a kai a kai na gaisuwa
Ya zamanta ya koma rayuwa yanda yake yi, a hankali komai ya ringa daidaituwa har du wani tunani nasa ya dawo jikinsa
Sannu sannu rashinta a kusa da shi ya fara tasiri
Sati uku kennan da rasuwar Nusaiba abin ya gama kama jinni da jikinsa
Bilhaki a yanzun kewarta yake, idan ya tuna magangannunsu da ita kuwa irin furucinta yakan ji tamkar an dake shi da karfe mai karfi a dukan gabobin jikinsa, da ace zata kasance mai yi masa uzuri da ta gane ta taka matsayin da ba wace ta taba takawa a duniya, da ace zata iya ganewa da ta ture du wani abin sun zauna, bai je mata da wata magana ba sai dan ya yaba, bai je mata da rokon ta gyara kawarta kuma yar uwarta ba sai dan ya jita daban, ba cin fuska bane, yabo ne
Yakan girgiza kansa, a hankali ya furta" Ban yi haka da sanina ba BEEBAH "
Sai ya shafa gemun dake habarsa a hankali ya ce" da ace zaki yarda, da na furta maki irin ilar da kika gama yiwa rayuwata Beebah, kin kai wajen da nakan ji a kasan zuciyata cewar ba zan iya babu ke ba"
Wayarsa ya dauko a karo na bakwai kennan da zai tura mata mesage ba amsa, shi kansa tun abin na bashi mamaki har ya dawo ya daina bashi mamaki irin yanda yake da naci a kan lamarinta, shine zaune da aikin yiwa mace message, shi da ko aurenki zai yi mai zuwa ya masa zancen daban shi kawai sai an kawo ki zaku hade, dan murmushi ya yi
A hankali ya dora dogayen yatsutsansa ya shiga taping din message kamar haka" Kin manta da bawan Allah ne? Ki bani amsa alfarmar rasululah S.A.W "
Sai da ta amsa da sallalahu alaihi wa salam, kafin ta tura masa da salama
Ajiyar zuciya ya yi yana kallon salamar kamar wani dogon message mai dadi kafin ya dora da fadin" Ina muradin gannin matata, ko zan samu wannan alfarmar? "
Bata maida masa da amsa ba sai kurawa Nadia ido da ta yi wace ke ta ciye ciye abinta, sam yanzun ta sake da mutanen gidan tana cudanya da su tamkar yan uwanta na jinni, sannan ko tsakaninta da Najeebar sukan taba hira, maganar sirri ce ta kau, basa wani sirrin junna irin na da
Mikewa ta yi ta shige ciki
Katon hijab ta sanyo hade da nikaf ta fito
Wajen Ammi ta je ta dan duka ta yi mata magana sannan ta mike ta yi gaba
Saloon dinta ta nufa
Tana shiga ta je ta zauna su Aida suka saki aikin da suke yi suka bita dakin da ta shige
Umarnin su gama ta basu sannan ta fara tsife kitson kanta da ya tsufa
Sai bayan sun gama ne suka rufu a kanta, wasu na tsifar kan, wasu na wanke mata kafa da akaifu, daya na gyara mata akaifun hannu , mai kunshi na hada kunshin da zata yi mata dan kadan ba mai yawa ba iya hannayenta
Ba ita ta bar saloon din nan ba sai da yama sosai kafin ta koma bangaren AMMI
A cenma wanka ta shige cikin nutsuwa ta gama kimtsa jikinta cikin lalausan lesh ja mai adon baki a jikinsa kafin ta fito hannunta rike da dan mayafi ruwan baki sidik mai shara shara
Ido kawai AMMI ta zuba mata, kalar fatar jikinta wani sheki take kara yi tamkar ta rihana, a yanzun sai ta kara budewa ko dan abinda suke zargin tana dauke da shi ne?
Kiraye kirayen salar isha ya sakata daukan hijab din AMMI ta gabatar da sallar sannan ta zauna nan sunna dan taba hira
Sai da karfe tara ta yi ne Ammi ta kuma kallonta a karro na ba adadi , muryarta sanyaye ta ce" NAJEEBA, tashi ki tafi mana "
NAJEEBA ta dan yi murmushin, ita kanta ta kusan minti ashirin tana saka ta tashin to sai ta kasa tashin, dan haka ta mike
Har ta fara tafia AMMI ta ce" Kar ki manta, k8 fada masa gobe in sha Allah zaki koma bangarenki kin ji? "