Sashe 3
Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gashin kanta dake dadaure da tsakiya masu shegen kyau wanda NAJEEBA ta mata kitso kananu sosai ta jera mata su ya ringa shafawa a hankali bai bata amsa ba
Kamar minti biyar har ta yi baci hakan ya saka shi sauke ajiyar zuciya ya kalli ZAHRAU wace ke bi masa ya rage murya ya ce" Zahra yau a dakinki zata kwana dan Allah dan ki kular min da ita, kin ga Abih fa fushi yake da mu baki daya yau ko ita bai nema ba
Kanta ta gyada ta mike da wayarta dake ringin saurayinta ne wanda aka saka masu rana ta duka ta dauke kanwar nata ta nufi dakinta da ita
Tana kaita ta shinfideta ta hade kitson cen sama ta daure shi dan kar ya dameta wajen baci
Ta yi mata adu'ar neman tsari kafin ta tsareta da ido a cikin ranta kuwa fadi take" inama Abih zai maido mahaifiyarki ke, ki tashi da jin dumin uminki a cikin jikin ki, ki rayu irin na kowata yarinya mai shekaru kananu irin naki?
A hankali ta ja abin rufa ta rufe mata daidai kirjinta ta duka ta mana mata kiss a goshinta ta kuma ayanna" ya Allah, kar ka jarabemu da aure aure, wato ka sa dukanmu idan mukai aure ya zama mijinmu shine wanda zai birne mu, Allah kar ka kama mu da halayan mahaifinmu na yawan auri saki, ka sa mu zauna komai rintsi mu rayu da y'ayanmu
Jikinta sanyaye itama sanye da kayan bacinta dogon wando sakake sosai da riga budadiya sosai ta fada saman bed din ta kara rungume kanwar nata kafin ta amsa kiran saurayin nata dake ta maido kiran
Yana nan zaune sai da kowace ta shiga dakinta domin dare ya tsala sosai har sha biyu kafin ya sauke ajiyar zuciya ya mike ya fita ya ja kofar bangarensu ya nufi nasu shi da kanninsa
Tana shiga dakinta ta cire rigar jikinta
Shafafen cikinta da ta gama cin pizza aman sam bai tasa ba ta kala tana shafawa ta ce" Alhamdulilah na koshi
Mika ta yi ta shige bayi
Wani wankan ta sake daurowa da alwallah sannan ta kuskure bakinta
Tana fitowa eigar sallarta ta saka ta yi shafa'i da wutiri ta yi adu'a ta shafa
Cire kayan ta yi ya rage mata daga ita sai pant, ta dauko bras kadai ta saka domin a rayuwarta sam bata iya baci da kaya masu nauyi, ta fefeshe jikinta da turare ta shafa humura
Madarar da ta kwaba da tumatur din danye ta shashafa a fuskarta kafin ta haye saman lafiyayan bed dinta mai sasaukan shinfida
Sama take kallo kanta saman matashin kan dake ajiye dan kar ta goge abin domin bai bushe ba
Gefe daya kuwa wayarta ne ta shiga shating da tarin samarinta wa'inda ita kanta ba zata iya irgasu ba
Dakinsa daya da kanninsa dan sam bai raba daki da shi ba, gadonsu ne dai daban daban
Sai da ya shinfide shi domin ya yi baci
Sannan shima ya shiga bayi ya yi dukan uzurinsa ya fito
Baki daya yayan MUTALAB sunna da wata irin tsafta da kuma rikon adini, shima sai da ya yi raka'a biyu domin ya yi nafilarsa kafin ya kishingida da wayarsa a hannunsa
Message ya tura kamar haka" Allah ya huci zuciyar kanina
Har ya cire rai da zai bashi amsa domin lokacin karfe kusan daya na dare ne, sai dai cen ya ga amsarsa kamar haka" wata biyu ne ka bani DAYABU
Murmushi ya yi dan ya san dama baya so ya kire shi da kanninsa,
Wani message din ya dora kamar haka" na san ba zaka kulaceni da yawa ba idan ka yi duba baki daya kanena tamkar y'ayan cikina na dauke su, ina kokarin basu kariya da dukan karfina....ka gafarce mu
Nanma ya jima sosai kafin ya bashi amsar cewa" Allah ya shirye mu
Da sauri DAYABU ya dora" amen ya Allah
Sai kuma a kasa ya dora" ka yafe mata, yarinta ce, na mata fada ba zata kuma kai hannunta jikin Zinaria ba
Ya buda message din, ya karanta sarai, aman sai ya ki bashi amsa
Hakan ya sa hankalin DAYABU ya kasa kwonciya, yana rike da wayar a hannunsa ya kasa samun baci, yana tsoron yaki yafe mata ya rama ta wani wajen, yana matukar tsoron shirun Sarkin nasu wanda ake kasa gane inda ya dosa
Shi kuwa sarki dama ba sauka yake ba domin sam baya kashe data , wayar ya ajiye gefen abin bed ya koma a hankali ya kwontar da kansa ya lumshe idannuwansa yana tunnani
Murmushi ya yi yana girgiza kai da takaicin yarinyar cinkushe a kasan zuciyarsa
Kwarai ya ga karfin halinta, ya kuma yarda cewa bata da kunya
Ya kara yarda da shawarar da ya yiwa kansa cewa sai ya koya mata hankali a duniyarta
Zinaria dake falo yana jiyo shashekar kukanta, domin yana zuwa zai kwonta ta zo ta tsaya tana kukan a gabansa aka mareta aman ya kasa datse hannun wanda ya maretan?
Hannunsa kawai ya daga mata ya yi mata nuni da ta tafi, domin sam baya iya hakurin jiyo koke koken nan
Wani murmushin ya yi a kasan zuciyarsa ya ayanna" bayan batawa zuri.armu sunna da take faman yi a cikin garina, yana jaza mani zagi dan kawai mahaifiyata na kanwar mahaifinta ana kiranta da kanwata na zuba mata ido tana tabara, irin yanda wasu ke tunanin samun dagin kafa dan sunna soyaya ko watsewa da ita, shine yau zata nuna gwarjinina baya kaiwa gareta? Shine yau zata nunan ita jinnin shuwa arab ce ta hanyar daga hannunta ta mari matana a gabana?
Kansa aya girgiza yaumshe idannuwansa yana tunanin tafiar da zai yi ya kai yaronsa waje, Aliyu bashi da lafia yana fama da rashin lafia mai tsanani mai tashi lokaci zuwa lokaci
Yaron kan fita a hayacinsa ya mimike ya ringa wani irin zabura wani sa'in harma ya sume
Yaron na fama sosai yana jin jiki wanda hakan ke matukar dagwa mahaifin nasa hankali da kuma mahaifiyarsa wace ta dora dukan so da isarta a kansa cewa yarima ne mai jiran gado.....................
DAYABU kam sai da ya gaji da zaman jiran amsa ya fara gyangyadi ya ajiye wayar bayan ya kasheta ya kwonta a hannunsa na dama da tunanin da izinin Allah gobe daga wajen aiki zai koma cikin baban gidan ya same shi ya bashi hakuri
Tun da asuba kiran sallar fari mahaifinsu ya ringa bi daki daki yana dokawa da karfin gaske
Baya tsayawa su bude yake yin gaba domin yana cikin fushi da su, da da ne sai ya shiga ya ga tashinsu sun dauro alwallah yake barin wajen
Haka kowace ta dauro alwallah suka fito falonsu suka tayar da sallah
Bayan sun gama sun yi adu'o'insu du suka mike suka yi bangaren mahaifinsu zuwa lokacin har karfe bakwai ta yi
Du zama suka yi kamar yanda suka tarar da yayansu kansa sade
A hankali suka shiga gaishe shi, sai dai sam baya amsa masu yana ta danna carbinsa ya kure waje daya da ido
DAYABU ya sauke ajiyar zuciya a hankali ya ce" ABIH fushi zaka yi ta yi da mu ne? Ba zaka yafe mana ba bayan ka san bamu da inda zamu nufa mu ji sanyi?
Da haushi haushi ya dago ya kale shi ya ce" makaryaci! Makaryaci kawai, karya ne , ni zan matse maku waje ku kai karana a saka min laya? Ba ruwana da ku ba ruwana ku je ku tafiarku
Yar karamar cikinsu ce ta mike da dan karamin hijab dinta cikus cikus tana takawa ta je jikin mahaifin nata ta dora kanta a jikinsa ta yi luff tana sauke ajiyar zuciya
Shima hannunsa ya sa a hankali yana dan talabeta sannan yana bin y'ayan nasa da harara wa'inda suka sasada kawunansu kowane bai ce komai ba
Cen matarsa ta shigo ta dauki kwaliyar safe hannunta dauke da wani irin plat mai yannayin kifi marar nauyi mai kyan gaske da natsakaicin girma
Cikinsa gasashen kifi ne da soyayan dankalin turawa ta rufe shi da farar leda irin yanda ake nadewar nan
Cike da kissa ta duka ta ajiye gaban Abih
Ta koma wajen frij ta dauko ruwa ta dawo ta kuma ajiye masa tana ta takama irin ga matar ubansun nan ta zauna tana kokarin bude masa
Da kallo du suke binta ciki kuwa harda shi da kallon mamaki yake binta
Tsarin gidansa a irin wannan lokacin da y'ayansa ke zuwa gaishe shi a lokacin ake gabatar da kayan karin kumalon da ma'aikatan gidan ke girkawa tun da asuba
Nan suke haduwa su karya kafin du su watse kowane ya je ya shiga shirin tafia wajen aikinsa ko karatunsa
A hankali ya ce" ama yaya haka na ga iya wannan?
Sai da ta juya idannuwanta masu girma da kyau sannan ta ce" iya shi na basu umarnin dafawa
Da wani mamakin ya ce" aman ina abincin *Y'AYANA?*
Itama da wani irin mamaki ta kale shi kafin ta budi bakinta ta ce" y'ayanka fa Habiby? Y'ayan naka da suka kaika suka baka laya a gaban jama.a suka tozarta ka suka wulakanta ka? Y'ayan naka da basa tsoronka basa yi mani biyaya a matsayina na matar ubansu wato uwarsu? Na gaji da wahalar zuwa kicin ina ta faman fadin kowane irin abinda yake kari da shi, na gaji da jido masu kayan kari na kawo masu tun daga kicin su karya kulun, na gaji da rashin kunyar y'ayanka Habiby!
Da mamaki yake kallonta, ransa ne ya shiga tsale yana kunna, y'ayansa ne ta yi tsaye tana wulakantawa dan kawai an samu wannan yar matsalar? Ba ita zata dafa ba, ba kuma ita zata kawo din ba domin daga bakin bangarensa suke kawo mata ita sai ta idaso da shi ciki dan ba yar aikin dake shiga bangarensa
A hankali ya rintse idannuwansa yana kokarin control din haushin da ya kama zuciyarsa domin so yake ya nunawa y'ayan nasa fushinsa a fili dan ko gaba su kiyaye irin abin tozarcin nan da suka yiwa kansu da kansu wanda idan duniya ta ji su za'a zaga bale su matan da suka fi yawa harma suka kawo mizalin aure
Kamar minti biyar har ta yi baci hakan ya saka shi sauke ajiyar zuciya ya kalli ZAHRAU wace ke bi masa ya rage murya ya ce" Zahra yau a dakinki zata kwana dan Allah dan ki kular min da ita, kin ga Abih fa fushi yake da mu baki daya yau ko ita bai nema ba
Kanta ta gyada ta mike da wayarta dake ringin saurayinta ne wanda aka saka masu rana ta duka ta dauke kanwar nata ta nufi dakinta da ita
Tana kaita ta shinfideta ta hade kitson cen sama ta daure shi dan kar ya dameta wajen baci
Ta yi mata adu'ar neman tsari kafin ta tsareta da ido a cikin ranta kuwa fadi take" inama Abih zai maido mahaifiyarki ke, ki tashi da jin dumin uminki a cikin jikin ki, ki rayu irin na kowata yarinya mai shekaru kananu irin naki?
A hankali ta ja abin rufa ta rufe mata daidai kirjinta ta duka ta mana mata kiss a goshinta ta kuma ayanna" ya Allah, kar ka jarabemu da aure aure, wato ka sa dukanmu idan mukai aure ya zama mijinmu shine wanda zai birne mu, Allah kar ka kama mu da halayan mahaifinmu na yawan auri saki, ka sa mu zauna komai rintsi mu rayu da y'ayanmu
Jikinta sanyaye itama sanye da kayan bacinta dogon wando sakake sosai da riga budadiya sosai ta fada saman bed din ta kara rungume kanwar nata kafin ta amsa kiran saurayin nata dake ta maido kiran
Yana nan zaune sai da kowace ta shiga dakinta domin dare ya tsala sosai har sha biyu kafin ya sauke ajiyar zuciya ya mike ya fita ya ja kofar bangarensu ya nufi nasu shi da kanninsa
Tana shiga dakinta ta cire rigar jikinta
Shafafen cikinta da ta gama cin pizza aman sam bai tasa ba ta kala tana shafawa ta ce" Alhamdulilah na koshi
Mika ta yi ta shige bayi
Wani wankan ta sake daurowa da alwallah sannan ta kuskure bakinta
Tana fitowa eigar sallarta ta saka ta yi shafa'i da wutiri ta yi adu'a ta shafa
Cire kayan ta yi ya rage mata daga ita sai pant, ta dauko bras kadai ta saka domin a rayuwarta sam bata iya baci da kaya masu nauyi, ta fefeshe jikinta da turare ta shafa humura
Madarar da ta kwaba da tumatur din danye ta shashafa a fuskarta kafin ta haye saman lafiyayan bed dinta mai sasaukan shinfida
Sama take kallo kanta saman matashin kan dake ajiye dan kar ta goge abin domin bai bushe ba
Gefe daya kuwa wayarta ne ta shiga shating da tarin samarinta wa'inda ita kanta ba zata iya irgasu ba
Dakinsa daya da kanninsa dan sam bai raba daki da shi ba, gadonsu ne dai daban daban
Sai da ya shinfide shi domin ya yi baci
Sannan shima ya shiga bayi ya yi dukan uzurinsa ya fito
Baki daya yayan MUTALAB sunna da wata irin tsafta da kuma rikon adini, shima sai da ya yi raka'a biyu domin ya yi nafilarsa kafin ya kishingida da wayarsa a hannunsa
Message ya tura kamar haka" Allah ya huci zuciyar kanina
Har ya cire rai da zai bashi amsa domin lokacin karfe kusan daya na dare ne, sai dai cen ya ga amsarsa kamar haka" wata biyu ne ka bani DAYABU
Murmushi ya yi dan ya san dama baya so ya kire shi da kanninsa,
Wani message din ya dora kamar haka" na san ba zaka kulaceni da yawa ba idan ka yi duba baki daya kanena tamkar y'ayan cikina na dauke su, ina kokarin basu kariya da dukan karfina....ka gafarce mu
Nanma ya jima sosai kafin ya bashi amsar cewa" Allah ya shirye mu
Da sauri DAYABU ya dora" amen ya Allah
Sai kuma a kasa ya dora" ka yafe mata, yarinta ce, na mata fada ba zata kuma kai hannunta jikin Zinaria ba
Ya buda message din, ya karanta sarai, aman sai ya ki bashi amsa
Hakan ya sa hankalin DAYABU ya kasa kwonciya, yana rike da wayar a hannunsa ya kasa samun baci, yana tsoron yaki yafe mata ya rama ta wani wajen, yana matukar tsoron shirun Sarkin nasu wanda ake kasa gane inda ya dosa
Shi kuwa sarki dama ba sauka yake ba domin sam baya kashe data , wayar ya ajiye gefen abin bed ya koma a hankali ya kwontar da kansa ya lumshe idannuwansa yana tunnani
Murmushi ya yi yana girgiza kai da takaicin yarinyar cinkushe a kasan zuciyarsa
Kwarai ya ga karfin halinta, ya kuma yarda cewa bata da kunya
Ya kara yarda da shawarar da ya yiwa kansa cewa sai ya koya mata hankali a duniyarta
Zinaria dake falo yana jiyo shashekar kukanta, domin yana zuwa zai kwonta ta zo ta tsaya tana kukan a gabansa aka mareta aman ya kasa datse hannun wanda ya maretan?
Hannunsa kawai ya daga mata ya yi mata nuni da ta tafi, domin sam baya iya hakurin jiyo koke koken nan
Wani murmushin ya yi a kasan zuciyarsa ya ayanna" bayan batawa zuri.armu sunna da take faman yi a cikin garina, yana jaza mani zagi dan kawai mahaifiyata na kanwar mahaifinta ana kiranta da kanwata na zuba mata ido tana tabara, irin yanda wasu ke tunanin samun dagin kafa dan sunna soyaya ko watsewa da ita, shine yau zata nuna gwarjinina baya kaiwa gareta? Shine yau zata nunan ita jinnin shuwa arab ce ta hanyar daga hannunta ta mari matana a gabana?
Kansa aya girgiza yaumshe idannuwansa yana tunanin tafiar da zai yi ya kai yaronsa waje, Aliyu bashi da lafia yana fama da rashin lafia mai tsanani mai tashi lokaci zuwa lokaci
Yaron kan fita a hayacinsa ya mimike ya ringa wani irin zabura wani sa'in harma ya sume
Yaron na fama sosai yana jin jiki wanda hakan ke matukar dagwa mahaifin nasa hankali da kuma mahaifiyarsa wace ta dora dukan so da isarta a kansa cewa yarima ne mai jiran gado.....................
DAYABU kam sai da ya gaji da zaman jiran amsa ya fara gyangyadi ya ajiye wayar bayan ya kasheta ya kwonta a hannunsa na dama da tunanin da izinin Allah gobe daga wajen aiki zai koma cikin baban gidan ya same shi ya bashi hakuri
Tun da asuba kiran sallar fari mahaifinsu ya ringa bi daki daki yana dokawa da karfin gaske
Baya tsayawa su bude yake yin gaba domin yana cikin fushi da su, da da ne sai ya shiga ya ga tashinsu sun dauro alwallah yake barin wajen
Haka kowace ta dauro alwallah suka fito falonsu suka tayar da sallah
Bayan sun gama sun yi adu'o'insu du suka mike suka yi bangaren mahaifinsu zuwa lokacin har karfe bakwai ta yi
Du zama suka yi kamar yanda suka tarar da yayansu kansa sade
A hankali suka shiga gaishe shi, sai dai sam baya amsa masu yana ta danna carbinsa ya kure waje daya da ido
DAYABU ya sauke ajiyar zuciya a hankali ya ce" ABIH fushi zaka yi ta yi da mu ne? Ba zaka yafe mana ba bayan ka san bamu da inda zamu nufa mu ji sanyi?
Da haushi haushi ya dago ya kale shi ya ce" makaryaci! Makaryaci kawai, karya ne , ni zan matse maku waje ku kai karana a saka min laya? Ba ruwana da ku ba ruwana ku je ku tafiarku
Yar karamar cikinsu ce ta mike da dan karamin hijab dinta cikus cikus tana takawa ta je jikin mahaifin nata ta dora kanta a jikinsa ta yi luff tana sauke ajiyar zuciya
Shima hannunsa ya sa a hankali yana dan talabeta sannan yana bin y'ayan nasa da harara wa'inda suka sasada kawunansu kowane bai ce komai ba
Cen matarsa ta shigo ta dauki kwaliyar safe hannunta dauke da wani irin plat mai yannayin kifi marar nauyi mai kyan gaske da natsakaicin girma
Cikinsa gasashen kifi ne da soyayan dankalin turawa ta rufe shi da farar leda irin yanda ake nadewar nan
Cike da kissa ta duka ta ajiye gaban Abih
Ta koma wajen frij ta dauko ruwa ta dawo ta kuma ajiye masa tana ta takama irin ga matar ubansun nan ta zauna tana kokarin bude masa
Da kallo du suke binta ciki kuwa harda shi da kallon mamaki yake binta
Tsarin gidansa a irin wannan lokacin da y'ayansa ke zuwa gaishe shi a lokacin ake gabatar da kayan karin kumalon da ma'aikatan gidan ke girkawa tun da asuba
Nan suke haduwa su karya kafin du su watse kowane ya je ya shiga shirin tafia wajen aikinsa ko karatunsa
A hankali ya ce" ama yaya haka na ga iya wannan?
Sai da ta juya idannuwanta masu girma da kyau sannan ta ce" iya shi na basu umarnin dafawa
Da wani mamakin ya ce" aman ina abincin *Y'AYANA?*
Itama da wani irin mamaki ta kale shi kafin ta budi bakinta ta ce" y'ayanka fa Habiby? Y'ayan naka da suka kaika suka baka laya a gaban jama.a suka tozarta ka suka wulakanta ka? Y'ayan naka da basa tsoronka basa yi mani biyaya a matsayina na matar ubansu wato uwarsu? Na gaji da wahalar zuwa kicin ina ta faman fadin kowane irin abinda yake kari da shi, na gaji da jido masu kayan kari na kawo masu tun daga kicin su karya kulun, na gaji da rashin kunyar y'ayanka Habiby!
Da mamaki yake kallonta, ransa ne ya shiga tsale yana kunna, y'ayansa ne ta yi tsaye tana wulakantawa dan kawai an samu wannan yar matsalar? Ba ita zata dafa ba, ba kuma ita zata kawo din ba domin daga bakin bangarensa suke kawo mata ita sai ta idaso da shi ciki dan ba yar aikin dake shiga bangarensa
A hankali ya rintse idannuwansa yana kokarin control din haushin da ya kama zuciyarsa domin so yake ya nunawa y'ayan nasa fushinsa a fili dan ko gaba su kiyaye irin abin tozarcin nan da suka yiwa kansu da kansu wanda idan duniya ta ji su za'a zaga bale su matan da suka fi yawa harma suka kawo mizalin aure