Sashe 38
Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yan matan ne du suka mimike aman Najeeba sai ta langwabe a jikin Abih ta lumshe idannuwanta tamkar bata san da fitowarsa ba
Da sauri Zahrau ta saka hannayenta ta mikar da ita inda ta sakar mata harare ita kuwa ta jinginar da ita a jikinta
Ya saka wata shigar ce mai birkita lisafin alhazai
Ya gama kashe shigarsa ne cikin shiga mai daraja
Ya fito a sarkinsa ga rawaninsa mai girma mai kayata sarautarsa
Ja ya yi ya tsaya gaban makeken abin turaran wutar da ake yi ana karawa kafin ya kone ake cirewa a zuba wani yana tashi a hankali domin ba garwashi bane a ciki toka ce mai zafin gaske
Hannunsa ya dora saman dokar wace ke dauke da zafin gaske domin ita ke saka turaren hayaki a hankali a hankali
Da yan yatsunsa ya marmatsa turaren dan ya isa haka sannan ya maida dubansa wajen mahaifiyarsa wace ta fi daukan hankalinsa gannin yannayinta
A hankali ya karaso har kusa da ita kafin ya rage tsayinsa sosai kansa sade ya furta" barka da safiya Anmy
Anmy ta dago ta sauke idannuwanta a saman kansa
Hannunsa ta kamo ta rike tana yi masa duba irin na ido cikin ido, a hankali ta ce" na kawo karar yan uwanka, ina so a mana shara'ar cikin gida , ina so ka zaunar da DAYABU MUTALAB tare da kannensa baki daya ka yi masu tambayar a kan me zasu ware daya daga cikinsu?
Najeeba ta lumshe idannuwanta, tabas itama tana son a hana wannan gaba tsakaninsu da yar kanwarsu, yarinyar zata baka tausayi ne idan ta ga daya daga cikinsu tana rarume rarumen ya dauketa tana kukan ya dauketa sai dai ba hali domin maganar dayabu maganar uba ce a wajensu, sai dai a yanzun fa ta ji azalumin nan ne zai yi maganar sai take jin a kan me?
Idannuwansa ya lumshe wanda hakan ke nufin amsarsa ne na ya karbi bukatar mahaifiyarsa
Agogon hannunsa ya duba a hankali ya furta" karfe tara na dare a falon karatu
Abih ya sauke ajiyar zuciya yana mai jin kanwar tasa a ransa, yana godewa Allah a kulun da ya bara masa ita, ita daya ta rage masa sai y'ayansu
Anmy ta dubi yan matan a hankali ta ce" na san ba zaku fadi laifin yayanku ba, kuma ba zaku fadi abinda kuka yi tsakaninku ba, aman ku sani idan kun ga kun samu wariyar kai to kasa ta birni idannuwana ne
Shi dai yana tsaye ne sai da ta gama ya kama hannayenta ya nufi wajen zama da ita
Yana zaunar da ita ya dawo suka gaisa da Abih kafin ya samu waje ya zauna
Du yan matan uku kasa suka kara zubewa
Aman Najeeba sai ta karasa saman kujerar da Anmy ke zaune ta dane gefen kujerar sannan ta dora kanta a kafadarta
Wannan karron kam komai a kan idannuwansa, mamakin yanda aka yi ta mike kan kafafuwanta da sauri haka da mamakin yanda aka yi ta manta gargadinsa da sauri haka suka saka shi tsaida dubansa a kanta
Lebensa na kasa ya dantse da hakoransa kafin a sanyaye ya buda bakinsa bayan ya gama harhada kalaman da zai yi anfani da su ya ce"
[1/30, 7:17 PM] Ummu Sadeeq: 🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
22
Cike da iza ya buda bakinsa ya kai dubansa wajen Abih, a hankali ya ce" Abih, in sha Allah auren Zahrau karshen watan nan na tsayar da shi
Abih ya ringa gyada kansa, tabas ya yarda da abinda ya yanke domin shi din uba ne a wajen yaren baki daya sannan shi da kansa ya isa da shi bale yaren
Sai da ya kara mintunna yana jin sai sanya albarka Abih da Amih suke, yaren kuwa du sun sada kawunansu
Anmy kuwa tana shafa bayan Najeeba, lalabata take domin bata da lafia konda safe da ta farka sai da ta sha maganinta na athsma domin numfashinta ba wai wani daidaituwa ya yi ba
Bakinsa ya buda a karo na biyu ya kaisasa muryarsa ya ce" sai dai ina so hakan ya zamo sirri
Ko da wasa bana so maganar ta fita tsakar gida bale waje domin BINTU kasheta aka yi
Gaba dayansu a zabure suka kale shi
Najeeba kuwa kamar wace aka jefo daga kan Anmy zuwa kasa sai gata ta wuntsilo tana kallonsa a tsorace
Abih ya yi gagawar furta" innalilahi wa ina ilaihi raj'une, wani irin kasheta aka yi? Wa ya kasheta?
Anmih ta kafeshi da ido, subahannalah kasheta? Wani irin kasheta? Gaba daya sai ta ji hankalinta ya tashi da maganar sannan ya sako cewar kar a fitar da maganar Zahrau kennan yana cikin tsantsamin wani ne ya yi hakan a tatare da shi?
Ajiyar zuciya ya sauke yana kallon Abih sannan ya kalli Anmih
A hankali ya ce" Allah masani, sai dai kowa ya yi taka tsantsan sawayen kowa a kirge yake
Gaba daya ta sha jinnin jikinta daga zaunen da take kafin ta maida dubanta wajen yan uwanta
Suma yanzun sarkin suke kallo a tsorace su duka
Yana gama magana ya mike tsaye
Baki dayansu suka sada kawunansu, a hankali suke furta" a huta lafia
Anmih cike da kaunar d'an nata kwaya daya da kuma tsantsar tausayin halin da yake ciki itama ta furta" a huta lafia
Sai da ya shige du suka dago da kawunansu
Rarafawa Zahrau ta yi da sauri ta dora kanta saman cinyar Anmih
Muryarta na dan rawa rawa ta ce" anmy, tsoro nake ji, kamar wanda ya kasheta yana iya kashe ni?
Anmy ta yi sauri girgiza kanta a hankali ta ce" ba zai kashe min ke ba, ba zai kashe min ke ba in sha Allahu
Allah zai hana, itama ki kadara lokacinta ne ya yi
A hankali Najeeba ta kama hannunta ta rike a nata itama cike da tunanin da ya gama hadasa mata zufa daga cikin jikinta
Fitar da suka fasa kennan, domin dama ta yi niyar fita da su ne su je wajen likita a kara duba Najeeba sannan su je wajen batuba wace ta yi niyar damka mata shirin Zahrau dan duka duka auren bai fi sati biyu ba
A dole suka koma bangarenta suka hadu ta saka a kawo mata kayayakin shirya amare a boye
Tun a ranar ta shiga baiwa Zahrau shiri irin na gyaran jiki da hade haden tsumi kala daban daban
Sai take jin dadin yannayin, dan ta tuna da, dan haka ta titino abubuwa irin na da wa'inda ta rike wuta sosai a zamanin mahaifin mai martaba ta ringa kawo dukan abin bukata
Kara kayan gyaran jikin ta yi sosai domin tana darzar fatar Zahrau sauran na darzar nasu da kansu
Tsumin nan ne kawai basa sha, sun rufe a falon Anmy na biyu sun shinfida katuwar tabarma sun dora mata leda du sun saka kannanun kaya sai raha suke, itama Anmy din sai daria takewa shirmensu har tsalen itama sai ta shafa suke hadin madara da kurkum fir ta ce ba zata shafa ba
Turaren wuta mai dadin kamshin ne ta zuba a dan kasko ya ringa ratsa jikin Zahrau,
Tana gamawa Ummulkhair ta dauko masu suma suka hadu a cikin abin rufa su uku suka zuba
Anmy ta bisu da da kallo ta yi murmushi tana girgiza kanta, fatanta Allah ya nuna mata nasu suma haka ta kimtsa su
Da sauri Najeeba ta cire abin rufar tana ta numfarfashi sama sama
Ummukulsum ta warce ta kara rufa su tana fadin" ke ja cen zaki wani bude mana dama mai numfashin kadangaru kawai
Najeeba ta matsa tana sauke numfashi, Anmy ta miko mata sansanyar madarar da ta kadawa Zahrau tana mata dariar itama ta ce" idan ba neman magana ba mai ya kaiki saka kanki ke mai cutar huka?
Amsa ta yi ta kafa kanta ta shanye tas sannan ta kalli anmy ta ce"Anmy ina son na turara jikina nima
Anmy ta ce" to zo nan
Mikewa ta yi ta karasa wajen da aka yiwa Zahrau
Zama ta yi saman kujerar Anmy ta rufa mata bargon aman kanta a waje ta zuba mata turaran mai sanyin kanshi ya shiga bin jikinta
Kafafuwanta ta wara cikin dabara ta kara matsa turaren wajen sosai harda rintse ido dan zafi ta ji na dukan wajen domin da pant a jikinta, tana ji su Nadia na fadin aba turara wajen da turaren wuta ko a yi matsi, to ita me hadinta da matsin? Aman wannan kam sai ta yi ((😲))
Sun jima a wajen kafin suke fitowa shima yama ta yi suka fito dan amsar baki
Bayan salar isha'i yaya Dayabu ya shigo tare da NAJEEB,
Sunna sanye da shada ne a jikinsu wando da riga iri daya sun yi tsaf da su
Ya gaishe da Anmy yana dan murmushi irin yana neman gyaran nan, sai Anmy ta hade fuskarta ta kawar da kai
Murmushi ya yi a kasan zuciyarsa, bai ce komai ba
Sai da lokacin ya yi du suka nufi bangaren harda kananen
Ta lungun da zai sada su da dakin karatun suka bi suka karasa dakin karatun
A dakin nabar kujera daya tak ce sai shinfidun cafet na alfarma
Sai manyan kur'anai, da alo manya
Maka makan tableau ne dauke da sunnanyen Allah da ayatul kursiyu, da sunnan Muhammad (sallalahu alaihi wa salam), su Alhamdu
Ac hudu ne a dakin sai manyan panka tafka tafka dake kunne suma sunna aikinsu
Tun kafin su Zauna muryar Abih ta shigo da salama
Ba shi daya bane tare yake da matarsa hakan ya sa Anmy kallonsa da kallo irin na me ya sa zai zo da ita?
Kawar da kansa ya yi ya nemi waje ya zauna
Yanda aka yi zaman Abih ya zauna ne tare da Dayabu da Najeeb a bangare guda
Gefen daya kuwa Anmy ce tare da yan matanta kananun du sun dadane mata jiki da yan kananun alkuabarsu sun yi tsaf kamar ka sace su ka gudu
Manyan kuwa kowace na gefe gefenta , su kam yanzun basa sanye da Alkyaba sai zumbula zumbulan hijabai har kasa irin mai habar nan
Da sauri Zahrau ta saka hannayenta ta mikar da ita inda ta sakar mata harare ita kuwa ta jinginar da ita a jikinta
Ya saka wata shigar ce mai birkita lisafin alhazai
Ya gama kashe shigarsa ne cikin shiga mai daraja
Ya fito a sarkinsa ga rawaninsa mai girma mai kayata sarautarsa
Ja ya yi ya tsaya gaban makeken abin turaran wutar da ake yi ana karawa kafin ya kone ake cirewa a zuba wani yana tashi a hankali domin ba garwashi bane a ciki toka ce mai zafin gaske
Hannunsa ya dora saman dokar wace ke dauke da zafin gaske domin ita ke saka turaren hayaki a hankali a hankali
Da yan yatsunsa ya marmatsa turaren dan ya isa haka sannan ya maida dubansa wajen mahaifiyarsa wace ta fi daukan hankalinsa gannin yannayinta
A hankali ya karaso har kusa da ita kafin ya rage tsayinsa sosai kansa sade ya furta" barka da safiya Anmy
Anmy ta dago ta sauke idannuwanta a saman kansa
Hannunsa ta kamo ta rike tana yi masa duba irin na ido cikin ido, a hankali ta ce" na kawo karar yan uwanka, ina so a mana shara'ar cikin gida , ina so ka zaunar da DAYABU MUTALAB tare da kannensa baki daya ka yi masu tambayar a kan me zasu ware daya daga cikinsu?
Najeeba ta lumshe idannuwanta, tabas itama tana son a hana wannan gaba tsakaninsu da yar kanwarsu, yarinyar zata baka tausayi ne idan ta ga daya daga cikinsu tana rarume rarumen ya dauketa tana kukan ya dauketa sai dai ba hali domin maganar dayabu maganar uba ce a wajensu, sai dai a yanzun fa ta ji azalumin nan ne zai yi maganar sai take jin a kan me?
Idannuwansa ya lumshe wanda hakan ke nufin amsarsa ne na ya karbi bukatar mahaifiyarsa
Agogon hannunsa ya duba a hankali ya furta" karfe tara na dare a falon karatu
Abih ya sauke ajiyar zuciya yana mai jin kanwar tasa a ransa, yana godewa Allah a kulun da ya bara masa ita, ita daya ta rage masa sai y'ayansu
Anmy ta dubi yan matan a hankali ta ce" na san ba zaku fadi laifin yayanku ba, kuma ba zaku fadi abinda kuka yi tsakaninku ba, aman ku sani idan kun ga kun samu wariyar kai to kasa ta birni idannuwana ne
Shi dai yana tsaye ne sai da ta gama ya kama hannayenta ya nufi wajen zama da ita
Yana zaunar da ita ya dawo suka gaisa da Abih kafin ya samu waje ya zauna
Du yan matan uku kasa suka kara zubewa
Aman Najeeba sai ta karasa saman kujerar da Anmy ke zaune ta dane gefen kujerar sannan ta dora kanta a kafadarta
Wannan karron kam komai a kan idannuwansa, mamakin yanda aka yi ta mike kan kafafuwanta da sauri haka da mamakin yanda aka yi ta manta gargadinsa da sauri haka suka saka shi tsaida dubansa a kanta
Lebensa na kasa ya dantse da hakoransa kafin a sanyaye ya buda bakinsa bayan ya gama harhada kalaman da zai yi anfani da su ya ce"
[1/30, 7:17 PM] Ummu Sadeeq: 🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
22
Cike da iza ya buda bakinsa ya kai dubansa wajen Abih, a hankali ya ce" Abih, in sha Allah auren Zahrau karshen watan nan na tsayar da shi
Abih ya ringa gyada kansa, tabas ya yarda da abinda ya yanke domin shi din uba ne a wajen yaren baki daya sannan shi da kansa ya isa da shi bale yaren
Sai da ya kara mintunna yana jin sai sanya albarka Abih da Amih suke, yaren kuwa du sun sada kawunansu
Anmy kuwa tana shafa bayan Najeeba, lalabata take domin bata da lafia konda safe da ta farka sai da ta sha maganinta na athsma domin numfashinta ba wai wani daidaituwa ya yi ba
Bakinsa ya buda a karo na biyu ya kaisasa muryarsa ya ce" sai dai ina so hakan ya zamo sirri
Ko da wasa bana so maganar ta fita tsakar gida bale waje domin BINTU kasheta aka yi
Gaba dayansu a zabure suka kale shi
Najeeba kuwa kamar wace aka jefo daga kan Anmy zuwa kasa sai gata ta wuntsilo tana kallonsa a tsorace
Abih ya yi gagawar furta" innalilahi wa ina ilaihi raj'une, wani irin kasheta aka yi? Wa ya kasheta?
Anmih ta kafeshi da ido, subahannalah kasheta? Wani irin kasheta? Gaba daya sai ta ji hankalinta ya tashi da maganar sannan ya sako cewar kar a fitar da maganar Zahrau kennan yana cikin tsantsamin wani ne ya yi hakan a tatare da shi?
Ajiyar zuciya ya sauke yana kallon Abih sannan ya kalli Anmih
A hankali ya ce" Allah masani, sai dai kowa ya yi taka tsantsan sawayen kowa a kirge yake
Gaba daya ta sha jinnin jikinta daga zaunen da take kafin ta maida dubanta wajen yan uwanta
Suma yanzun sarkin suke kallo a tsorace su duka
Yana gama magana ya mike tsaye
Baki dayansu suka sada kawunansu, a hankali suke furta" a huta lafia
Anmih cike da kaunar d'an nata kwaya daya da kuma tsantsar tausayin halin da yake ciki itama ta furta" a huta lafia
Sai da ya shige du suka dago da kawunansu
Rarafawa Zahrau ta yi da sauri ta dora kanta saman cinyar Anmih
Muryarta na dan rawa rawa ta ce" anmy, tsoro nake ji, kamar wanda ya kasheta yana iya kashe ni?
Anmy ta yi sauri girgiza kanta a hankali ta ce" ba zai kashe min ke ba, ba zai kashe min ke ba in sha Allahu
Allah zai hana, itama ki kadara lokacinta ne ya yi
A hankali Najeeba ta kama hannunta ta rike a nata itama cike da tunanin da ya gama hadasa mata zufa daga cikin jikinta
Fitar da suka fasa kennan, domin dama ta yi niyar fita da su ne su je wajen likita a kara duba Najeeba sannan su je wajen batuba wace ta yi niyar damka mata shirin Zahrau dan duka duka auren bai fi sati biyu ba
A dole suka koma bangarenta suka hadu ta saka a kawo mata kayayakin shirya amare a boye
Tun a ranar ta shiga baiwa Zahrau shiri irin na gyaran jiki da hade haden tsumi kala daban daban
Sai take jin dadin yannayin, dan ta tuna da, dan haka ta titino abubuwa irin na da wa'inda ta rike wuta sosai a zamanin mahaifin mai martaba ta ringa kawo dukan abin bukata
Kara kayan gyaran jikin ta yi sosai domin tana darzar fatar Zahrau sauran na darzar nasu da kansu
Tsumin nan ne kawai basa sha, sun rufe a falon Anmy na biyu sun shinfida katuwar tabarma sun dora mata leda du sun saka kannanun kaya sai raha suke, itama Anmy din sai daria takewa shirmensu har tsalen itama sai ta shafa suke hadin madara da kurkum fir ta ce ba zata shafa ba
Turaren wuta mai dadin kamshin ne ta zuba a dan kasko ya ringa ratsa jikin Zahrau,
Tana gamawa Ummulkhair ta dauko masu suma suka hadu a cikin abin rufa su uku suka zuba
Anmy ta bisu da da kallo ta yi murmushi tana girgiza kanta, fatanta Allah ya nuna mata nasu suma haka ta kimtsa su
Da sauri Najeeba ta cire abin rufar tana ta numfarfashi sama sama
Ummukulsum ta warce ta kara rufa su tana fadin" ke ja cen zaki wani bude mana dama mai numfashin kadangaru kawai
Najeeba ta matsa tana sauke numfashi, Anmy ta miko mata sansanyar madarar da ta kadawa Zahrau tana mata dariar itama ta ce" idan ba neman magana ba mai ya kaiki saka kanki ke mai cutar huka?
Amsa ta yi ta kafa kanta ta shanye tas sannan ta kalli anmy ta ce"Anmy ina son na turara jikina nima
Anmy ta ce" to zo nan
Mikewa ta yi ta karasa wajen da aka yiwa Zahrau
Zama ta yi saman kujerar Anmy ta rufa mata bargon aman kanta a waje ta zuba mata turaran mai sanyin kanshi ya shiga bin jikinta
Kafafuwanta ta wara cikin dabara ta kara matsa turaren wajen sosai harda rintse ido dan zafi ta ji na dukan wajen domin da pant a jikinta, tana ji su Nadia na fadin aba turara wajen da turaren wuta ko a yi matsi, to ita me hadinta da matsin? Aman wannan kam sai ta yi ((😲))
Sun jima a wajen kafin suke fitowa shima yama ta yi suka fito dan amsar baki
Bayan salar isha'i yaya Dayabu ya shigo tare da NAJEEB,
Sunna sanye da shada ne a jikinsu wando da riga iri daya sun yi tsaf da su
Ya gaishe da Anmy yana dan murmushi irin yana neman gyaran nan, sai Anmy ta hade fuskarta ta kawar da kai
Murmushi ya yi a kasan zuciyarsa, bai ce komai ba
Sai da lokacin ya yi du suka nufi bangaren harda kananen
Ta lungun da zai sada su da dakin karatun suka bi suka karasa dakin karatun
A dakin nabar kujera daya tak ce sai shinfidun cafet na alfarma
Sai manyan kur'anai, da alo manya
Maka makan tableau ne dauke da sunnanyen Allah da ayatul kursiyu, da sunnan Muhammad (sallalahu alaihi wa salam), su Alhamdu
Ac hudu ne a dakin sai manyan panka tafka tafka dake kunne suma sunna aikinsu
Tun kafin su Zauna muryar Abih ta shigo da salama
Ba shi daya bane tare yake da matarsa hakan ya sa Anmy kallonsa da kallo irin na me ya sa zai zo da ita?
Kawar da kansa ya yi ya nemi waje ya zauna
Yanda aka yi zaman Abih ya zauna ne tare da Dayabu da Najeeb a bangare guda
Gefen daya kuwa Anmy ce tare da yan matanta kananun du sun dadane mata jiki da yan kananun alkuabarsu sun yi tsaf kamar ka sace su ka gudu
Manyan kuwa kowace na gefe gefenta , su kam yanzun basa sanye da Alkyaba sai zumbula zumbulan hijabai har kasa irin mai habar nan