Sashe 12
Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana dubanta har sai da ya rage tsayinsa ya kasance sun daidaita da junna a hankali ya ce" ihu zaki yi masa?
Gunjin kukan da take har jijiyoyin wuyanta da kanta sun fito rado rado ya saka shi janyota ya bata kyakyawar runguma
Hakan ya sakata kara sakin kukanta tana mai tambayarsa" shikenan ya tafi ya bar ni?
Idannuwansa ya lumshe yana shafa bayanta, baki daya ta yi jajajir ta rikice
Ta kuma fashewa da kuka ta ce" sai da na hana shi yin wankan nan na dare, ina shafa mai ya shige bayi har yanai min gwalo ya shiga kasan shower ya sakarwa kansa ruwa a kansa
Sai da ya ga raina zai baci ya fito ya bude min
Sai dai tuni jikinsa na rawa hancinsa na zubar da jinni
Fashewa ta kuma yi da kuka tana rike hannunsa da ya tsurawa fuskarta ido yana sauraronta ta ce" shikennan sai ya fara karkarwa sosai da sosai har hakoransa na hadewa waje guda sunna bada sauti hakan ya tsoratani na yi gagawar rufa shi da bargo na je dakinsa na shiga binciko magungunnansa tare da wasu kayan darin dan na saka masa
Ta rushe da kuka tana nunawa ta ce" ina dawowa da na daga shi na ganshi a haka, baya min murmushin, baya cewa" ki yi hakuri Anna
Baya barin jikin shine nace ko summar ce ya kuma yi?
Idannuwansa ya rintse yana jin wani irin yanda yake jin kansa ba karfi ba dabara
A yau ya samu kansa cikin wani tashin hankali mai gigitawa a tarihin rayuwarsa
A mutanen dake makale a cen cikin zuciyarsa yau ya shafe mutun na biyu kennan, bayan shafe idannuwan mahaifinsa da ya yi da kannanun shekarunsa
Hasbunnalahu wani.imal wakim
Sosai ya barta a kirjinsa ta samu kukan ita wanda hakan ya saka ta dan ji saukin zuciyarta
Sai da ta ci kukan har ya so zarce misali kafin ya dago habarta yana kallon fuskarta
A hankali ya kai bakinsa daudai nata, idannuwansa ya rintse kafin ya damki lebunnanta ya shiga tsotsa yana jin zuciyarsa ta yi masa nauyi
Bashi da kalaman da zai nuna mata ta yi shiru
Baya so gawa kwonce ta ringa irin wannan kukan
Sai da ya san ya kashe bakin kukan sannan ya dubeta ido cikin ido cikin yannayin tausasawa domin ita uwa ce, ba wanda zai kaita jin ciwon rabuwa da yaron nan shi ya tabata da hakan, shi yasa yake jin bashi da kalmar da zai iya rarashinta sai dai ya tunatar da ita cewa itama yau ko gobe, ko watarana sunnanta gawa, wannan kira na mahalici ba wanda ya isa a manta da shi ko a yafe masa, an halice mu ba tare da mun roka ba, zamu mutu ba tare da mun shirya ba
Tabas shi daya suka malaka a duniya sai bari biyu da ta yi bayansa, aman kuma wanda ya halice shi ya fita son sa
Dan haka cikin tausasa kalamai da iya yinsa dan gannin shi ya jure ya bata kwarin gwuiwa ya ce" ki daina kuka haka zinaria
Ki yi masa adu'a irin ta bakin uwa na tabata mala'ikun rahama zasu yi rige rigen zuwa amsarsa
Ki yafe masa har cikin zuciyarki tun daga daukan cikinsa, naludarsa, shayar da shi da kika yi, da hakurin tarbiyantar da shi, ki yi kokari daga yanzu idan kin buda bakinki dan ki yi salatin annabi ne sai ko ki yi ta yi masa shinfidar kabari har a kai shi
Wannan ita ce kaunar da zaki iya nuna masa a matsayinki na uwa
Wannan itace babar kaunar da zaki nuna masa zinaria
Kar ki manta *dukan mai rai mamaci ne*
(Allah jikanka babyna😔👏)
Gani take du da ya samu bakin yi mata magangannun nan dan ba shi bane ita
Gani take sam bai san irin zafin ciwon da take ji a kasan zuciyarta ba
Yaya zai hanata kuka da daga murya?
Yaya zai hanata ihu da birgima?
Yaya yake so yarensa na shiru ya kasance a kanta a irin wannan bakar rana a gareta?
Bai san zafin da take iya ji ba, bata tunanin zai iya sanin karfin zafin da zuciyarta ke mata ba dan ba zai haihu ba kasancewarsa namiji
Wannan lamaru kuwa shi zai sa har ya mutu ba zai ji jrin yanda baki daya zuciyarta ke tsartuwar jinni ba
Zaunar da ita ya kuma yi sannan ya juya cikin irin tafiar nan tasa ta kasaitacen bujimin sarki
Sam bai iya sauri ba , wannan shine saurin nasa domin har yana kokarin kauce sawunsa na kafar gaba
Dakin ya koma,
A hankali ya karasa wajen bed dinsa
Cike da jin lamarin a kasan zuciyarsa ya langwabe kansa yana kallon gawar yaron
Ko jiya har kusan karfe goma yana zaune gefensa, abinda ya fi tsaya masa a rai irin yanda yaron ya nace sai ya ga fuskarsa sai ya cire masa rawaninsa a wajen karatu
Bai barshi ba har sai da ya ga ya fara gyadi gyadi ya dauko shi ya taho da shi nan bangarensa ya shaidawa mahaifiyarsa ta zo ta dauke shi yana jin baci
A lokacin ne kuma ya dauke rawaninsa wanda hakan ya saka yaron yin murmushi yana shafa gefwn fuskar mahaifin nasa sai kuma baci ya dauke shi
Ashe farkawa ya yi har mai afkuwa ta afku da shi?
Cikin nutsuwa ya shiga shirya shi
Yana yi masa wanka ne hawaye ya shiga zarya a saman fuskarsa
Shikenan mutun din kennan, shikenan an kare kana kwonce sai yanda aka juyaka
A hankali ya ringa llaba shi dan raunin fitar rai
A hankali ya gama tsaftace shi ya kimtsa shi
Ruwa ya watsa a jikinsa ya saka farar jalabiya irin ta saudiya sannan ya fito
Hannunsa ya mika ya dauke shi a hannayensa ya rungume shi ya karasa saman bes dinsa da shi ya dora shi
Alkur'ani ya dauko ya zauna ya buda ya shiga karanta masa murya a bude a bayanne
Irin yanda yake karatun zaka gane zuciyarsa a cikin wani yannayi mai rauni da tashin hankali take
Cikin nutsuwa ya samu ya yiwa yaronsa dukan abinda ya dace kowace gawa mai sa'a ta samu, ya samu adu'o'i kamar me
Kiran sallar fari akai a baban masalacin gidan sarki wanda yake cikin gidan
Shiru bai fito ba, a na biyu ne har hankalin liman ya fara tashi sai gashi ya fito
Sallah aka gabatar, ana gamawa ya fadawa liman cewa idan an jima a samu a leko rakiyar yarima, Allah ya yi masa rasuwa
Da mugun mamaki liman ke kallonsa irin yanda ya sanar da rasuwar cike da nutsuwa wada a irin ahekarinsa da yawa zaka same su da rashin nutsuwa har haka
Tabas ya yarda abin sarauta ya gama ratsa sarkin nasu sai fatan Allah ya tsare
Nan da nan ya sanar, wanda rasuwar ta matukar fifita mutane harma aka yi ta kokarin son ganninsa dan gabatar masa da gaisuwa sai dai ya shige da sauri ta kofar da yake shigowa
Direct bangaren mahaifiyarsa ya je
A hankali ya cire takalmansa ya karasa shiga ciki
Tana lazumi zaune saman salayarta, sanye da wata bakar riga mai hade da hijab har kasa rigar kuma budadiya ce sosai wace take sallah ne da ita
Yana karasawa gabanta ya je ya zauna wanda hakan ya sakata saurin dago kanta tana dubansa
Rawanin kansa ya shiga warwarewa a hankali da sauri ta maida dubanta sosai a kansa
Yana gama warwarewa ya kamo tafin hannunta ya dora a gefen fuskar nasa sannan ya lumshe idannuwansa
Da sauri ta kai karshe tana kallonsa , zuciyarta kuwa ta shiga tsintsinkewa
Muryarta na nuna tashin hankali ta ce" me, me ke damunka? Me ya faru a masarauta?
Sai da ya lumshe idannuwansa ya kuma budewa da kyar kafin ya sauke ajiyar zuciya cikin nutsuwa ya ce" ALIYU, ya amsa kiran mahalincinsa
Da wani irin sauri ta zabura tana furta" innalilahi wa.ina ilaihi raj.une
Yaushe? Ciwon ne ya tashi? Ina yake? Innalilahi wa.ina ilaihi raj.une
Sai ga hawaye a kan fuskarta
Cikin matsanancin tausayinsa take kallonsa tana nin mutuwar dan jikan nata, sai kuma lokaci daya ta ce" ina mahaifiyarsa? Ina zinariyar take ne?
Ya salam, wani rudun ta shiga sakamakon tunawa da ta yi irin yanda zinariya ke takama da yaron nan
Takan daki kirji cike da gadara ta furta wata rana itace gimbiyar masarautar nan domin ta rigaya ta haifi magaji
Koda jikin yaron ya motsa takan tirsasa shi fita ya zauna kusa da mahaifinsa wai dan ya koyi yanda ake tafiar da sharia
Akoy ranar da ta yi wata magana a gaban amarya cewa" ya dace a ringa kiran yarima da mai martaba, dan ko a yanzu ba'a iya cire rai da hawansa kujera, bale idan mahaifinsa ya yi kaira da wuri
Wannan magana ta matukar girgiza amarya harma ta kasa riketa take sanarwa Gimbiya
Hannayensa ya saka ya maidota ya zaunar da ita yana dubanta a hankali ya ce" tun wajen karfe biyu da rabi ya rasu Anmy, tana bangarenta ta yi salama da shi na yi mata kiran likita ne ta dubata domin ta fara zubar da jinni sakamakon tashin hankalin da koke koken da ta ringa yi gashi cikin bai yi kwari sosai ba
Sosai mutuwar nan ta daki Gimbiya, ta kara tsoron Allah sannan ta tausayawa mahaifiyar Aliyu da mahaifinsa
Mahaifiyarsa ya kasance tana ta kuka a fili, mahaifinsa kuwa ba wanda ya ga kukansa sai dai ya sada kai sannan ya sauke ajiyar zuciya
Nan da nan masarautar ta cika makil da jama'a, yan uwa da aminan arziki kowa da kararsa
Da wuri wuri aka kaishi makwoncinsa sannan aka shinfida tabarmi dan amsar gaisuwa inda wajen ya cika makil ana ta amsar gaisuwa
Baki daya ahalin gidan Mutalab sunna wajen rasuwar tun da sasafe
Gaba daya matan sunna bangaren Gimbiya, nan du aka taru da yake falon ba karami bane harta Zinariyar nan take da yayarta sunna zaune sai kuka take har bayan magariba sam ta ki ta kwontar da hankalinta ta bi yaron da adu.a, idannuwanta sun kasa gane mata irin suturar da Allah ya yiwa yaron nata irin yanda aka taru ana amsar gaisuwa
Lakada lakadan kafet uku ne shinfide, daya GIMBIYA ce zaune da tarin y'ayanta wato su NAJEEBA
Gunjin kukan da take har jijiyoyin wuyanta da kanta sun fito rado rado ya saka shi janyota ya bata kyakyawar runguma
Hakan ya sakata kara sakin kukanta tana mai tambayarsa" shikenan ya tafi ya bar ni?
Idannuwansa ya lumshe yana shafa bayanta, baki daya ta yi jajajir ta rikice
Ta kuma fashewa da kuka ta ce" sai da na hana shi yin wankan nan na dare, ina shafa mai ya shige bayi har yanai min gwalo ya shiga kasan shower ya sakarwa kansa ruwa a kansa
Sai da ya ga raina zai baci ya fito ya bude min
Sai dai tuni jikinsa na rawa hancinsa na zubar da jinni
Fashewa ta kuma yi da kuka tana rike hannunsa da ya tsurawa fuskarta ido yana sauraronta ta ce" shikennan sai ya fara karkarwa sosai da sosai har hakoransa na hadewa waje guda sunna bada sauti hakan ya tsoratani na yi gagawar rufa shi da bargo na je dakinsa na shiga binciko magungunnansa tare da wasu kayan darin dan na saka masa
Ta rushe da kuka tana nunawa ta ce" ina dawowa da na daga shi na ganshi a haka, baya min murmushin, baya cewa" ki yi hakuri Anna
Baya barin jikin shine nace ko summar ce ya kuma yi?
Idannuwansa ya rintse yana jin wani irin yanda yake jin kansa ba karfi ba dabara
A yau ya samu kansa cikin wani tashin hankali mai gigitawa a tarihin rayuwarsa
A mutanen dake makale a cen cikin zuciyarsa yau ya shafe mutun na biyu kennan, bayan shafe idannuwan mahaifinsa da ya yi da kannanun shekarunsa
Hasbunnalahu wani.imal wakim
Sosai ya barta a kirjinsa ta samu kukan ita wanda hakan ya saka ta dan ji saukin zuciyarta
Sai da ta ci kukan har ya so zarce misali kafin ya dago habarta yana kallon fuskarta
A hankali ya kai bakinsa daudai nata, idannuwansa ya rintse kafin ya damki lebunnanta ya shiga tsotsa yana jin zuciyarsa ta yi masa nauyi
Bashi da kalaman da zai nuna mata ta yi shiru
Baya so gawa kwonce ta ringa irin wannan kukan
Sai da ya san ya kashe bakin kukan sannan ya dubeta ido cikin ido cikin yannayin tausasawa domin ita uwa ce, ba wanda zai kaita jin ciwon rabuwa da yaron nan shi ya tabata da hakan, shi yasa yake jin bashi da kalmar da zai iya rarashinta sai dai ya tunatar da ita cewa itama yau ko gobe, ko watarana sunnanta gawa, wannan kira na mahalici ba wanda ya isa a manta da shi ko a yafe masa, an halice mu ba tare da mun roka ba, zamu mutu ba tare da mun shirya ba
Tabas shi daya suka malaka a duniya sai bari biyu da ta yi bayansa, aman kuma wanda ya halice shi ya fita son sa
Dan haka cikin tausasa kalamai da iya yinsa dan gannin shi ya jure ya bata kwarin gwuiwa ya ce" ki daina kuka haka zinaria
Ki yi masa adu'a irin ta bakin uwa na tabata mala'ikun rahama zasu yi rige rigen zuwa amsarsa
Ki yafe masa har cikin zuciyarki tun daga daukan cikinsa, naludarsa, shayar da shi da kika yi, da hakurin tarbiyantar da shi, ki yi kokari daga yanzu idan kin buda bakinki dan ki yi salatin annabi ne sai ko ki yi ta yi masa shinfidar kabari har a kai shi
Wannan ita ce kaunar da zaki iya nuna masa a matsayinki na uwa
Wannan itace babar kaunar da zaki nuna masa zinaria
Kar ki manta *dukan mai rai mamaci ne*
(Allah jikanka babyna😔👏)
Gani take du da ya samu bakin yi mata magangannun nan dan ba shi bane ita
Gani take sam bai san irin zafin ciwon da take ji a kasan zuciyarta ba
Yaya zai hanata kuka da daga murya?
Yaya zai hanata ihu da birgima?
Yaya yake so yarensa na shiru ya kasance a kanta a irin wannan bakar rana a gareta?
Bai san zafin da take iya ji ba, bata tunanin zai iya sanin karfin zafin da zuciyarta ke mata ba dan ba zai haihu ba kasancewarsa namiji
Wannan lamaru kuwa shi zai sa har ya mutu ba zai ji jrin yanda baki daya zuciyarta ke tsartuwar jinni ba
Zaunar da ita ya kuma yi sannan ya juya cikin irin tafiar nan tasa ta kasaitacen bujimin sarki
Sam bai iya sauri ba , wannan shine saurin nasa domin har yana kokarin kauce sawunsa na kafar gaba
Dakin ya koma,
A hankali ya karasa wajen bed dinsa
Cike da jin lamarin a kasan zuciyarsa ya langwabe kansa yana kallon gawar yaron
Ko jiya har kusan karfe goma yana zaune gefensa, abinda ya fi tsaya masa a rai irin yanda yaron ya nace sai ya ga fuskarsa sai ya cire masa rawaninsa a wajen karatu
Bai barshi ba har sai da ya ga ya fara gyadi gyadi ya dauko shi ya taho da shi nan bangarensa ya shaidawa mahaifiyarsa ta zo ta dauke shi yana jin baci
A lokacin ne kuma ya dauke rawaninsa wanda hakan ya saka yaron yin murmushi yana shafa gefwn fuskar mahaifin nasa sai kuma baci ya dauke shi
Ashe farkawa ya yi har mai afkuwa ta afku da shi?
Cikin nutsuwa ya shiga shirya shi
Yana yi masa wanka ne hawaye ya shiga zarya a saman fuskarsa
Shikenan mutun din kennan, shikenan an kare kana kwonce sai yanda aka juyaka
A hankali ya ringa llaba shi dan raunin fitar rai
A hankali ya gama tsaftace shi ya kimtsa shi
Ruwa ya watsa a jikinsa ya saka farar jalabiya irin ta saudiya sannan ya fito
Hannunsa ya mika ya dauke shi a hannayensa ya rungume shi ya karasa saman bes dinsa da shi ya dora shi
Alkur'ani ya dauko ya zauna ya buda ya shiga karanta masa murya a bude a bayanne
Irin yanda yake karatun zaka gane zuciyarsa a cikin wani yannayi mai rauni da tashin hankali take
Cikin nutsuwa ya samu ya yiwa yaronsa dukan abinda ya dace kowace gawa mai sa'a ta samu, ya samu adu'o'i kamar me
Kiran sallar fari akai a baban masalacin gidan sarki wanda yake cikin gidan
Shiru bai fito ba, a na biyu ne har hankalin liman ya fara tashi sai gashi ya fito
Sallah aka gabatar, ana gamawa ya fadawa liman cewa idan an jima a samu a leko rakiyar yarima, Allah ya yi masa rasuwa
Da mugun mamaki liman ke kallonsa irin yanda ya sanar da rasuwar cike da nutsuwa wada a irin ahekarinsa da yawa zaka same su da rashin nutsuwa har haka
Tabas ya yarda abin sarauta ya gama ratsa sarkin nasu sai fatan Allah ya tsare
Nan da nan ya sanar, wanda rasuwar ta matukar fifita mutane harma aka yi ta kokarin son ganninsa dan gabatar masa da gaisuwa sai dai ya shige da sauri ta kofar da yake shigowa
Direct bangaren mahaifiyarsa ya je
A hankali ya cire takalmansa ya karasa shiga ciki
Tana lazumi zaune saman salayarta, sanye da wata bakar riga mai hade da hijab har kasa rigar kuma budadiya ce sosai wace take sallah ne da ita
Yana karasawa gabanta ya je ya zauna wanda hakan ya sakata saurin dago kanta tana dubansa
Rawanin kansa ya shiga warwarewa a hankali da sauri ta maida dubanta sosai a kansa
Yana gama warwarewa ya kamo tafin hannunta ya dora a gefen fuskar nasa sannan ya lumshe idannuwansa
Da sauri ta kai karshe tana kallonsa , zuciyarta kuwa ta shiga tsintsinkewa
Muryarta na nuna tashin hankali ta ce" me, me ke damunka? Me ya faru a masarauta?
Sai da ya lumshe idannuwansa ya kuma budewa da kyar kafin ya sauke ajiyar zuciya cikin nutsuwa ya ce" ALIYU, ya amsa kiran mahalincinsa
Da wani irin sauri ta zabura tana furta" innalilahi wa.ina ilaihi raj.une
Yaushe? Ciwon ne ya tashi? Ina yake? Innalilahi wa.ina ilaihi raj.une
Sai ga hawaye a kan fuskarta
Cikin matsanancin tausayinsa take kallonsa tana nin mutuwar dan jikan nata, sai kuma lokaci daya ta ce" ina mahaifiyarsa? Ina zinariyar take ne?
Ya salam, wani rudun ta shiga sakamakon tunawa da ta yi irin yanda zinariya ke takama da yaron nan
Takan daki kirji cike da gadara ta furta wata rana itace gimbiyar masarautar nan domin ta rigaya ta haifi magaji
Koda jikin yaron ya motsa takan tirsasa shi fita ya zauna kusa da mahaifinsa wai dan ya koyi yanda ake tafiar da sharia
Akoy ranar da ta yi wata magana a gaban amarya cewa" ya dace a ringa kiran yarima da mai martaba, dan ko a yanzu ba'a iya cire rai da hawansa kujera, bale idan mahaifinsa ya yi kaira da wuri
Wannan magana ta matukar girgiza amarya harma ta kasa riketa take sanarwa Gimbiya
Hannayensa ya saka ya maidota ya zaunar da ita yana dubanta a hankali ya ce" tun wajen karfe biyu da rabi ya rasu Anmy, tana bangarenta ta yi salama da shi na yi mata kiran likita ne ta dubata domin ta fara zubar da jinni sakamakon tashin hankalin da koke koken da ta ringa yi gashi cikin bai yi kwari sosai ba
Sosai mutuwar nan ta daki Gimbiya, ta kara tsoron Allah sannan ta tausayawa mahaifiyar Aliyu da mahaifinsa
Mahaifiyarsa ya kasance tana ta kuka a fili, mahaifinsa kuwa ba wanda ya ga kukansa sai dai ya sada kai sannan ya sauke ajiyar zuciya
Nan da nan masarautar ta cika makil da jama'a, yan uwa da aminan arziki kowa da kararsa
Da wuri wuri aka kaishi makwoncinsa sannan aka shinfida tabarmi dan amsar gaisuwa inda wajen ya cika makil ana ta amsar gaisuwa
Baki daya ahalin gidan Mutalab sunna wajen rasuwar tun da sasafe
Gaba daya matan sunna bangaren Gimbiya, nan du aka taru da yake falon ba karami bane harta Zinariyar nan take da yayarta sunna zaune sai kuka take har bayan magariba sam ta ki ta kwontar da hankalinta ta bi yaron da adu.a, idannuwanta sun kasa gane mata irin suturar da Allah ya yiwa yaron nata irin yanda aka taru ana amsar gaisuwa
Lakada lakadan kafet uku ne shinfide, daya GIMBIYA ce zaune da tarin y'ayanta wato su NAJEEBA