Sashe 43
Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abih ya saki murmushi a lokacin da yake bayar da auren Zahrau, sai kuma wata nutsuwa da farin ciki ya shiga cikin zuciyarsa a lokacin da ya amshi sadakinta a hannayensa
Daurin aure ya tafi cikin tsarin islama, ya amshi adu'o'in manyan malamai
Lasifikar dake ajiye ce ke sanarwar daurin auren da ya saka zuciyoyi da dama neman tarwatsewa
Daga kwoncen da dake a saman doguwar kujerar falonta daga kasa bayi ne ke yi mata hidima wasu na yi mata tausa wasu na hada mata abin bukatarta ta wuntsilo ta fado daga saman kujerar sannan ta ruruko idannuwanta tana kara kasa kunnayenta dan jin abinda ke fitowa daga spiker masalacin gidan mijinta
Alhamdulilah, Alhamdulilah muryar liman ta furta a lokaci daya ya kuma maimaita kalmar" An daura auren SARKIN GARIN AGADEZ TARE DA GIMBIYA ZAHRAU BISA SADAKIN JAKA HAMSIN TARE DA DOKI MAI KWALIYAR ZINARI WANDA YA ZAMA HALALIYAR GIMBIYA ZAHRAU
wani irin ihu ta saki daga tsayen da take
Bata tsaya ta dauki alkyabarta ba ta juya da gudu ta nufi bangaren Anmy ta biyayiyar hanyarsu
Hanya ce dake boye, wace ba kowa ya san da ita ba aman a yau ta tashi tonata bata tsaya wata wata ba ta bude kofar ta fada falon Anky dake dauke da Anmy da zuga zugan yan matanta da suka fito a gimbiyoyi reras a jere abin ba'a cewa komai
Tana shiga hannayenta saman kanta ta furta" Anmy, me nake ji? An daura auren mahaifina da Zahrau wacece zahrau? A kan me sarki zai yarda a zo garin nan a yiwa mahaifiyata kishiya? Anmy kin san irin yanda Aya ta tsani maganar kishiya shine zai jaza min bakin jinni a wajen mahaifiyata? Walahi ba zai yiwu ba Anmy, Anmy wannan wani irin abu ne bai jima da tozartani ya min kishiya ya bara min abin fade a duniya baki daya ba shine yanzu zai jagoranci tozarcin uwata??
Baki dayansu idannuwansu a kanta suke
Shigar jikinta riga ce diguwa irin ta shan iskar nan domin bata da kauri ko kadan sai malalalen gashin kanta dake daure da dan ribom
Ga cikinta nan ya tasa sosai dan kamar ba cikin watani shida ba sosai ya fito dama alkyaba ke boye shi
Anmy ta cire kanta daga dubanta a hankali ta furta" subahanallah
Zulaihat, auren ne tozarci? Dama auren da mai martaba ya yi tozarci ne a wajenki ke a matsayinki na uwar gidansa? Sannan a yanzu kin ga halin da kike ciki kika fito a haka kina irin magangannun nan muryarki a sama sama tamkar ba ZINARIYAR Sarkin Danagaram ba? Dama haka kuke ko a yau ne abin ya sameki ?
Kallonta Najeeba ta yi ta kuma kalli Anmy ta ga Anmy ta kawar da dubanta wato ita kunyar kallonta take ji a haka ita kuwa ta tsaya kikam sai surfa tambayoyi take da sakin zance haka
Dubanta ne ta kai har wajen cikinta sannan ne ta ga shatin pant din dake cikin jikinta
Itama da sauri ta cire kanta tana kallon Zahrau,
Gani ta yi Zahra'un ta hade hannayenta ta rike da dan karfi
Bata hannata ba, bata kuma yi gigin rarashinta ba, dan bata so tun yanzu ya zamanto ta ringa shiga wani hali bayan bata ga komai ba
Juyawa ta yi ta shige ta bugo kofar da ya saka Anmy dago kanta da sauri ta kai dubanta wajen kofar
Idannuwanta ta lumshe, a hankali take tambayar kanta....shin itane Zulaihat ta bugawa kofa a yau? Lale idan kana raye ba abinda ba zaka gani ba
Yau itane aka bugowa kofa haka
Idannuwanta ta kara rintsewa tana mai taune lebenta na kasa
Aure? Abinda ta kwana da sannin cewa sai an mata shi ita dake auren sarki? Shine zata yi ikirarin an tozartata?
ZULAIHAT kar ki saka ni zarginki mana?
Zaihat kar ki saka zuciyata kin aminta da ke mana bayan hakan bai dace ba zato zunubi ne
Zulaihat a kan auren ne kike aikata haka?
Idannuwanta ta lumshe ta ji zuciyarta na furta mata" *MAI DAMAGARAM ZAI YI AURE, ZAI SAKE WANI AUREN KWANA KUSA KUWA ZULAHAT DOMIN NA IN DAI YARON YA GAJI MAHAIFINSA TO BA ZAI IYA ZAMA DA KWAYA DAYA TAK BA*
Gaba daya hargitsewa gidan ya yi da hayaniya da gude gude da murna domin sai da aka daura auren ne aka shiga shigowa da abubuwan yanka ana yin waje da su dan za'a yi sadaka ne da su
Ba'a jima ba gidan ya kwashi shiru sakamakon dogaren da suka fitar da kowa aka saki hanya aka kara gyara hanya
Cike da nutsuwa da kasauta suke takowa har suka idasa shiga bangaren Anmy
Tunda suka shigo gaba daya yan matan suka zube kasa kawunansu a kasa cike da girmamawa
Waje suka samu suka zazauna kafin suke amsa gaisuwar Anmy
Sai da wajen ya dan dauki shiru kafin cike da muryarsa mai nagarta ya buda bakinsa cikin nutsuwa ya koro adu'a
Ya yi fatan alkhairi kafin ya dora da wata zazafar nasiha wace ta kare a aure bauta ne, zaman raya sunna ta je,
Ya karashe da kausasa muryarsa yana fadin" kar na ji, kar na ga abinda zai saka ni taka kasar garin agadez ba da sunnan zumunci ba ya Zahrau
Kanta dake kasa tana ta hawaye ta kara sadawa tana dan gyadawa
Anmy ta yi musmushi da dan guntun hawaye a gurbin idannuwanta
Najeeba ta kara rike hannunta dan zuwa lokacin hannunta daya a cikin na Najeeba dayan kuwa a cikin na Ummu
Ajiyar zuciya ya sauke a sanyaye ya furta" ANMY, zan kaita da kaina ne
Anmy ta gyada kanta ta sanyaya muryarta ta furta" zan so a je da yan uwanta su yi mata kwana biyu Allah ya ja da kwanakinka
Kai tsaye ya furta" zamu je da UMMULKHAIR da UMMUKULSUM
ANMY ta tsare shi da kallo da mamakin jin abinda ya fada, Abihma dake cen gefe yana amsa waya kasa kasa hankalinsa na kan yaren nasa, sai ya kebance da su sun zanta tare da yayansu, Dayabu kuwa yana zaune dan nesa da su shima a kasa ya tankwashe kafafuwansa
ANMY ta ce" ai su uku ne, akoy NAJEEBA
dubansa ya kara kaiwa wajen Anmy, da duba irin na kar ki min haka, kafin ya zafafa dubansa zuwa ga Najeeba wace tun da ya nuna banda ita ta dago da mamaki tana kallonsa itama cike da jin haushin kalamansa
Irin duban da yake mata na tsananin tsana da wanda ta masa wanda tsaf duba me mai hade da harara kafin ta sada kanta tsaf a idannuwan Anmy
Da mamaki ta kara dubansa ta kuma kalli Najeeba
Murmushi ne ya kubuce mata kafin itama ta maida kanta ta sada tana jin wani tunani na son ta yi shi yanzu yanzu
Muryar sakin Agadez cike da kamala ya furta" Allah ya ja da ran mai Damagaram, zan so a je da kanwata domin na tabata zata debewa Gimbiya kewa
Yana fada ne yana nuna Najeeba hakan kuwa sai ya baiwa kowa mamaki ciki harda ita kanta Najeebar
Yaya aka yi kike da farin jinni a wajen manyan mutane bayan ke din baki dace da samun hakan ba *MAGE?*
Ya ayanna a ransa kafin yake cire dubansa daga kanta ya maida wajen Abih dake dawowa yana dan murmushi, shifa yau wani fayau yake jinsa, yau wani farin ciki yake ji mai girman gaske, yau ya aurar da daya
Tun dazu yake samun kiran mahaifiyarta da kuma Mardiya wace ya ajiyeta gefe ya yi watsi da ita
Yana karasowa shima kansa ya sada a gabansu, domin koda kuwa yana uba a wajen SHAHEED sannan siriki a wajen sarkin Agadez to fa shi din yana kasa da su ne daga indalah, Allah ya umarceshi da ya yi masu biyaya a matsayinsu na shuwagabanin kasarsa
A hankali ya buda bakinsa yana kallon Abih ya ce"""""🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
25
Cenxa harshensa ya yi zuwa harshen larabci, ya tausasa muryarsa ya kara sada kansa yana kallon yayan mahaifiyar tasa wanda ke zaune kusa da y'ayan nasa mata shima zuwa lokacin yannayin rashin son rabuwa da su ya bayana a tatare da shi
A hankali ya furta" Allah ya saka da alkhairi Abih, Allah ya biya da dukan bukatu na alkhairi ya kara girma ya kara rufa asiri
Yanda ka bani ragamar komai Allah ya fitar da ni da kai da kowa kunya a lamarin
Kuma dagowa ta yi da mamakin jin irin yanda larabcinsa ke son yi mata wahalar fahimta bayan larabcin yarenta ne, kasancewar larabci ya shiga cikin junna sai ya yi anfani da baban mai wahalar wanda shi Abih din shi ya koya masa shi ya yi magana, a ciki abu kalilan ne ta fahimta
Abih ya yi murmushi shima ya dauki yaren wanda ya tabata ko Anmy bata iya shi ba, shima kasancewar a saudiya ya yi karatu tun yana karami ya kasance yaren larabci kala biyu yake ji, da na wajen mahaifiyarsa da kuma wanda ya zame masa na makaranta ya bashi amsa kamar haka" nagartarka ta shaida kanta, bayan kasancewarka sarki sai kuma kyawawan halayenka suka sayan maka biyaya daga wajenmu iyayenka, Allah ya yi maka albarka, ya baka zuri'a dayiba
A kasan zuciyarsa ya amsa da amen amen amen
Kasa kasa ya yiwa Anmy bayanin ta inda zasu fito su shiga motar da zata sada su da aeroport nan da minti talatin
Mikewa suka yi suka fita ta hanyar da suka shigo
Anmy kuwa ta mike da sauri ta shiga hada hadar harhada mata dukan abubuwan bukata
A lokacin ne Abih ya samu damar kadaicewa da su baki daya
Daurin aure ya tafi cikin tsarin islama, ya amshi adu'o'in manyan malamai
Lasifikar dake ajiye ce ke sanarwar daurin auren da ya saka zuciyoyi da dama neman tarwatsewa
Daga kwoncen da dake a saman doguwar kujerar falonta daga kasa bayi ne ke yi mata hidima wasu na yi mata tausa wasu na hada mata abin bukatarta ta wuntsilo ta fado daga saman kujerar sannan ta ruruko idannuwanta tana kara kasa kunnayenta dan jin abinda ke fitowa daga spiker masalacin gidan mijinta
Alhamdulilah, Alhamdulilah muryar liman ta furta a lokaci daya ya kuma maimaita kalmar" An daura auren SARKIN GARIN AGADEZ TARE DA GIMBIYA ZAHRAU BISA SADAKIN JAKA HAMSIN TARE DA DOKI MAI KWALIYAR ZINARI WANDA YA ZAMA HALALIYAR GIMBIYA ZAHRAU
wani irin ihu ta saki daga tsayen da take
Bata tsaya ta dauki alkyabarta ba ta juya da gudu ta nufi bangaren Anmy ta biyayiyar hanyarsu
Hanya ce dake boye, wace ba kowa ya san da ita ba aman a yau ta tashi tonata bata tsaya wata wata ba ta bude kofar ta fada falon Anky dake dauke da Anmy da zuga zugan yan matanta da suka fito a gimbiyoyi reras a jere abin ba'a cewa komai
Tana shiga hannayenta saman kanta ta furta" Anmy, me nake ji? An daura auren mahaifina da Zahrau wacece zahrau? A kan me sarki zai yarda a zo garin nan a yiwa mahaifiyata kishiya? Anmy kin san irin yanda Aya ta tsani maganar kishiya shine zai jaza min bakin jinni a wajen mahaifiyata? Walahi ba zai yiwu ba Anmy, Anmy wannan wani irin abu ne bai jima da tozartani ya min kishiya ya bara min abin fade a duniya baki daya ba shine yanzu zai jagoranci tozarcin uwata??
Baki dayansu idannuwansu a kanta suke
Shigar jikinta riga ce diguwa irin ta shan iskar nan domin bata da kauri ko kadan sai malalalen gashin kanta dake daure da dan ribom
Ga cikinta nan ya tasa sosai dan kamar ba cikin watani shida ba sosai ya fito dama alkyaba ke boye shi
Anmy ta cire kanta daga dubanta a hankali ta furta" subahanallah
Zulaihat, auren ne tozarci? Dama auren da mai martaba ya yi tozarci ne a wajenki ke a matsayinki na uwar gidansa? Sannan a yanzu kin ga halin da kike ciki kika fito a haka kina irin magangannun nan muryarki a sama sama tamkar ba ZINARIYAR Sarkin Danagaram ba? Dama haka kuke ko a yau ne abin ya sameki ?
Kallonta Najeeba ta yi ta kuma kalli Anmy ta ga Anmy ta kawar da dubanta wato ita kunyar kallonta take ji a haka ita kuwa ta tsaya kikam sai surfa tambayoyi take da sakin zance haka
Dubanta ne ta kai har wajen cikinta sannan ne ta ga shatin pant din dake cikin jikinta
Itama da sauri ta cire kanta tana kallon Zahrau,
Gani ta yi Zahra'un ta hade hannayenta ta rike da dan karfi
Bata hannata ba, bata kuma yi gigin rarashinta ba, dan bata so tun yanzu ya zamanto ta ringa shiga wani hali bayan bata ga komai ba
Juyawa ta yi ta shige ta bugo kofar da ya saka Anmy dago kanta da sauri ta kai dubanta wajen kofar
Idannuwanta ta lumshe, a hankali take tambayar kanta....shin itane Zulaihat ta bugawa kofa a yau? Lale idan kana raye ba abinda ba zaka gani ba
Yau itane aka bugowa kofa haka
Idannuwanta ta kara rintsewa tana mai taune lebenta na kasa
Aure? Abinda ta kwana da sannin cewa sai an mata shi ita dake auren sarki? Shine zata yi ikirarin an tozartata?
ZULAIHAT kar ki saka ni zarginki mana?
Zaihat kar ki saka zuciyata kin aminta da ke mana bayan hakan bai dace ba zato zunubi ne
Zulaihat a kan auren ne kike aikata haka?
Idannuwanta ta lumshe ta ji zuciyarta na furta mata" *MAI DAMAGARAM ZAI YI AURE, ZAI SAKE WANI AUREN KWANA KUSA KUWA ZULAHAT DOMIN NA IN DAI YARON YA GAJI MAHAIFINSA TO BA ZAI IYA ZAMA DA KWAYA DAYA TAK BA*
Gaba daya hargitsewa gidan ya yi da hayaniya da gude gude da murna domin sai da aka daura auren ne aka shiga shigowa da abubuwan yanka ana yin waje da su dan za'a yi sadaka ne da su
Ba'a jima ba gidan ya kwashi shiru sakamakon dogaren da suka fitar da kowa aka saki hanya aka kara gyara hanya
Cike da nutsuwa da kasauta suke takowa har suka idasa shiga bangaren Anmy
Tunda suka shigo gaba daya yan matan suka zube kasa kawunansu a kasa cike da girmamawa
Waje suka samu suka zazauna kafin suke amsa gaisuwar Anmy
Sai da wajen ya dan dauki shiru kafin cike da muryarsa mai nagarta ya buda bakinsa cikin nutsuwa ya koro adu'a
Ya yi fatan alkhairi kafin ya dora da wata zazafar nasiha wace ta kare a aure bauta ne, zaman raya sunna ta je,
Ya karashe da kausasa muryarsa yana fadin" kar na ji, kar na ga abinda zai saka ni taka kasar garin agadez ba da sunnan zumunci ba ya Zahrau
Kanta dake kasa tana ta hawaye ta kara sadawa tana dan gyadawa
Anmy ta yi musmushi da dan guntun hawaye a gurbin idannuwanta
Najeeba ta kara rike hannunta dan zuwa lokacin hannunta daya a cikin na Najeeba dayan kuwa a cikin na Ummu
Ajiyar zuciya ya sauke a sanyaye ya furta" ANMY, zan kaita da kaina ne
Anmy ta gyada kanta ta sanyaya muryarta ta furta" zan so a je da yan uwanta su yi mata kwana biyu Allah ya ja da kwanakinka
Kai tsaye ya furta" zamu je da UMMULKHAIR da UMMUKULSUM
ANMY ta tsare shi da kallo da mamakin jin abinda ya fada, Abihma dake cen gefe yana amsa waya kasa kasa hankalinsa na kan yaren nasa, sai ya kebance da su sun zanta tare da yayansu, Dayabu kuwa yana zaune dan nesa da su shima a kasa ya tankwashe kafafuwansa
ANMY ta ce" ai su uku ne, akoy NAJEEBA
dubansa ya kara kaiwa wajen Anmy, da duba irin na kar ki min haka, kafin ya zafafa dubansa zuwa ga Najeeba wace tun da ya nuna banda ita ta dago da mamaki tana kallonsa itama cike da jin haushin kalamansa
Irin duban da yake mata na tsananin tsana da wanda ta masa wanda tsaf duba me mai hade da harara kafin ta sada kanta tsaf a idannuwan Anmy
Da mamaki ta kara dubansa ta kuma kalli Najeeba
Murmushi ne ya kubuce mata kafin itama ta maida kanta ta sada tana jin wani tunani na son ta yi shi yanzu yanzu
Muryar sakin Agadez cike da kamala ya furta" Allah ya ja da ran mai Damagaram, zan so a je da kanwata domin na tabata zata debewa Gimbiya kewa
Yana fada ne yana nuna Najeeba hakan kuwa sai ya baiwa kowa mamaki ciki harda ita kanta Najeebar
Yaya aka yi kike da farin jinni a wajen manyan mutane bayan ke din baki dace da samun hakan ba *MAGE?*
Ya ayanna a ransa kafin yake cire dubansa daga kanta ya maida wajen Abih dake dawowa yana dan murmushi, shifa yau wani fayau yake jinsa, yau wani farin ciki yake ji mai girman gaske, yau ya aurar da daya
Tun dazu yake samun kiran mahaifiyarta da kuma Mardiya wace ya ajiyeta gefe ya yi watsi da ita
Yana karasowa shima kansa ya sada a gabansu, domin koda kuwa yana uba a wajen SHAHEED sannan siriki a wajen sarkin Agadez to fa shi din yana kasa da su ne daga indalah, Allah ya umarceshi da ya yi masu biyaya a matsayinsu na shuwagabanin kasarsa
A hankali ya buda bakinsa yana kallon Abih ya ce"""""🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
25
Cenxa harshensa ya yi zuwa harshen larabci, ya tausasa muryarsa ya kara sada kansa yana kallon yayan mahaifiyar tasa wanda ke zaune kusa da y'ayan nasa mata shima zuwa lokacin yannayin rashin son rabuwa da su ya bayana a tatare da shi
A hankali ya furta" Allah ya saka da alkhairi Abih, Allah ya biya da dukan bukatu na alkhairi ya kara girma ya kara rufa asiri
Yanda ka bani ragamar komai Allah ya fitar da ni da kai da kowa kunya a lamarin
Kuma dagowa ta yi da mamakin jin irin yanda larabcinsa ke son yi mata wahalar fahimta bayan larabcin yarenta ne, kasancewar larabci ya shiga cikin junna sai ya yi anfani da baban mai wahalar wanda shi Abih din shi ya koya masa shi ya yi magana, a ciki abu kalilan ne ta fahimta
Abih ya yi murmushi shima ya dauki yaren wanda ya tabata ko Anmy bata iya shi ba, shima kasancewar a saudiya ya yi karatu tun yana karami ya kasance yaren larabci kala biyu yake ji, da na wajen mahaifiyarsa da kuma wanda ya zame masa na makaranta ya bashi amsa kamar haka" nagartarka ta shaida kanta, bayan kasancewarka sarki sai kuma kyawawan halayenka suka sayan maka biyaya daga wajenmu iyayenka, Allah ya yi maka albarka, ya baka zuri'a dayiba
A kasan zuciyarsa ya amsa da amen amen amen
Kasa kasa ya yiwa Anmy bayanin ta inda zasu fito su shiga motar da zata sada su da aeroport nan da minti talatin
Mikewa suka yi suka fita ta hanyar da suka shigo
Anmy kuwa ta mike da sauri ta shiga hada hadar harhada mata dukan abubuwan bukata
A lokacin ne Abih ya samu damar kadaicewa da su baki daya