Sashe 64
Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ummukulsumma ta dawo gefenta na hagu ta hau ta kwonta itama ta rike hannunta na hagu a cikin nata
Tamkar wasu kannanun yara sai da ya masu adu'ar tsari , ya kara tsayawa a wajensu har ya ga ta daina kukan baki bude sai hawaye dake bin gefen kumatunta, sosai abin ke damunsa aman zai jure dan idan bai nuna mata ba wani abu dan tana kuka ba tabas zata rikita su
Sai da ya sauke ajiyar zuciya sannan ya fita ya ja kofar yana kara sauke ajiyar zuciya tare da goge hawayensa
Cikin nutsuwa ya yiwa su Anmy bayanin cewa a ci gaba da shirye shirye!
Nan take Anmy ta dauki wayarta ta koma gefe ta yi kiran mutanen da ita suke jura, mutanen da ta yiwa wannan lokacin tanadi, wa'inda zasu saka Najeeba daka har sai lokacin ya yi su fito, mutanen dake kula da gimbiyar saudiya, tun da aka fadi maganar ta kakabe dukiyarta ta shiga shirye shirye, ta dauko su ta sauke su a wani tankamemen gidan SULTAN, jiran yau suke dama su taho
Tun da suka zube kawunnansu ke kasa jikinsu ke bari basu iya dagowa ba haka kuma bakinsu bai daina furta kalmomin ban hakuri da neman afuwar saken da suka yi har ta bace masu
Amintacensa ne ke fada tamkar zai kai masu bugu tare da nuni cewar zai cenza su ya maida su filin horon dogarai domin a irin abinda suka nuna ba za'a iya bugun kirji da su ba a filin daga ba!
Sai da ya kara lashe lebensa na kasa da yake jin a yau ya cika bushe masa kafin ya buda bakinsa a hankali ya ce" a ina kuka hadu da ita? Tana cikin wani yannayi? A ina ta cenza suturar da ta fita da ita?
Baban ne ya kara sada kansa ya nemi afuwa sosai kafin ya kora bayanin abinda suka sanni da inda suka ganta da kukan da take
Komawa ya yi ya jinginar da bayansa jikin kujerar da yake zaune ya mayar da idannuwansa ya lumshe
Da yan yatsunsa ya yi masu nuni cewar su tafi
Da sauri suka kara dukawa kamar zasu kwonta sunna ta neman afuwa kafin su fito daga falon
Kara zubewa Amintace ya yi kansa kasa ya shiga neman afuwar Sultan , domin du horon dogarai na gidan nan a hannunsa yake haka kuma idan suka aikata laifi yana da baban kaso a ciki
Idannuwansa da suka kara yi masa nauyi ya buda da kyar yana kallonsa
Sai da ya furzar da huci mai zafi kafin ya ce" daga yau, bata da wani mai tsaronta sai kai, du inda zata saka kafarta ka saka, du abinda zata ci ka fara tabawa, du wanda zai mu'amalanceta ka hana
Da mamaki kansa a kasa yake amsawa, ya cika da matsanancin mamakin jin cewar shi, shine zai tsare wannan yarinyar? shi rantsatsen mai baiwa Sarki tsaro ne, ko Gimbiya bai taba baiwa tsaro ba baban yaronsa ke bata tsaro aman yau shine aka wakilta da maganar baiwa wannan yarinyar tsaro?
Kara tasowa ya yi daga jikin kujerar yana kara dunkule hannunsa ya kara kakausa muryarsa ya ce" *hukunci zai hau wuyanka ne daga bakin lokacin da ta zile maka ka nemeta ka rasa, shu'uma ce, zata iya shiga duban mutane ka lalubeta ka rasa, hakan zai wanzar da tashin hankali a rayuwarka!*
Yana gama fada ya mike tsaye ya shiga takawa shi kuwa amintacensa kansa a sade a kasa yana fadin" Allah ya huci zuciyar mai damagaram, Allah ya huci zuciyar zaki, namu sarkin sarakaine na gida da dawa, Allah ya kara maka lafia da nisan kwana
Dakatawa ya yi, bai juyo ba daga inda yake ya furta" ka saka a binciki wacece *NADIA MOCTAR a UNIVERSITY*
Daga haka ya shige ciki yana jin wani irin al'amari mai girman gaske dake damunsa
Ta ina zai bi ya horata?
Ya je ya zubar da kansa ya shiga jikinta dan ya samu kusancin da zai kamata tsamo tsamo da laifin da take aikatawa sai gashi a lokacin da ta aminta ta bashi numberta harma suka fara sakarwa junna fuska ta hanyar yin yar doguwar hira da junna shine za'a katse? Shi ne zai auri yarinyar nan, nan da kwana goma?
Kansa ya daga ya kai wajen agogo,
Idannuwansa ya lumshe a lokacin da ya ga har karfe goma sha biyu ta gifta a ransa ya furta *aa ba kwana goma bane, kwana tara ne*
Lebensa ya kara cijewa na kasa yana mai ajiye rawaninsa
Hannunsa mai cike da yannayin karfi ya daga yana yamutsa summar kansa da ta taru wace yake so ya shiga ya aske kayansa da kansa
Idannuwansa ya kuma budewa a kasan zuciyarsa yake furta" da ace kin kilace kanki, da ke din babar harka ce da ba dai yaro ba sai dai baban yaro
Sai gashi kin banzatar da kanki,
Idannuwansa da suka dauki kalar ja dan bacin rai ya kara budawa yana furta"
Zaki zama matana ne, sai dai rayuwarki zata zama cikin kunci
Abinda kika saba da shi, kina ji kina ganni zai gagare ki, sai ya zame maki fiye da zinari domin zaki nema ruwa a jalo ki rasa shi, zan saka maki matakan tsaron da ko dan jaririn namiji ba zaki gani ba bale ki hadiyi yawunki a kansa
Zan kasance maki fitinar da baki taba tunanin zata shigo ratuwarki ba! (Ma ji ma gani)
Sai da ya shige sannan ya dago kansa
Ransa bace ya mike ya fita daga falon yana cike da matsanancin bacin rai
Du darajarsa? Du girmansa za'ace yanzu an nada shi kula da yarinya karama irin wannan?
To wai, meye girman darajarta da za'a nada shi, shi ya bata kula?
Meye tsakaninta da shi?
Sai kuma maganar Nadia Moctar, ta ina zai fara bincikenta? Nadiar nawa ce a cikin University?
Dole zai dauki wayarsa ya yi aikin, tunani yake me hadinsa da wata Nadia?
Wani murmushi ya yi yana girgiza kansa, wani auren zaka sake? Halitarka ba ta mace daya bace,
Kansa ya girgiza yana kara wani murmushin a kasan zuciyarsa ya furta
*Ga fili, ga mai doki*
Idannuwanta bude suke har goshin asuba
Ta kasa yarda cewa itane haka ke shirin faruwa da ita
Ta kasa tsayar da takamaimai abinda zata yi da rayuwarta
elle n'arrive pas a y croire (ta kasa yarda), cewar ita Najeeba, itane haka ke shirin faruwa da ita
Lokaci daya ta ringa da ta sannin rayuwa
Ashe du irin tara samarin nata zata kare a auren dole ne bata sani ba?
Sai kuma ta ji zuciyarta ta raunata, a hankali zuciyarta ta ringa kara rufeta da fada kamar haka" dole Allah ya kama ki Najeeba, ke ce zalinci wancen, yiwa wannan karya, cin kudin wancen, mazan da kika saka hawaye yawa ne da su ashe ke banza bami san cewa haka zaki kare ba? Ta tabata idan har ya yarda ya amshi aurenta ba dan wani bane sai kawai dan ya idasa nufinsa na son kasheta
Wani irin shakarsa take ji a kasan zuciyarta, zata iya rantsewa rabonta da ta shiga harkar matarsa ko shi din kansa tun da ta ganni ido da ido yana rike wuyan maciji harma ya saka yar yatsarsa a wajen bakinsa ya ringa fitar da wani ruwa mai duhun gaske
Tana kallonsa yana kallonta ya yi mata wanka da ruwa masu sanyin gaske bayan ya san tana fama da cutar athsma
A haka, bata yi masa komai ba ina da ta yi masan?
Sai goshin asuba barci mai wani irin nauyi ya kwasheta wanda sam bashi da dadi sai mafarkai mararsa dadi sosai a cikinsa
Da duhu duhu mata shida suka shigo har dakin da yan matan Anmy suke, wa'inda suke saman salaya sun gama sallah aman sun raba adu'a sunna yi dan Allah ya tankwasa yar uwarsu
Saman bed din Anmy ta kai dubanta bayan ta amsa gaisuwarsu
A hankali ta furta" bata yi baci ba jiya?
Ummulkhair ta gyada kanta kafin ta sada kanta
Matan nan fararen larabawa ne, kusan su duka farare ne tas tas sai wani irin shu'umin kamshi suke ga fatarsu kamar ka kali kanka a ciki
Anmy ta kai dubanta kansu a sanyaye ta ce" ban san ta inda zamu fara ba, bana iya yi mata tsawa ko na rufeta da fada, abinda na sani idan ta farka ta ganni zata so tayar da rigima, gashi dole a yau za'a sakata dakin dumin cen da gyara ku kanku ba zaku kuma fitowa ba bale ita sai ana gobe daurin auren, ban san ta yaya zata amince da abubuwan nan ba, ga wajen aikinta, ga ..................
Hannunta da datijuwar ciki ta rike ya saka Anmy sauke numfashi a maganarta tana ta lumshe idannuwanta domin sam bata so ta ga Najeebar a cikin wani yannayi na rashin jin dadi
Cikin harshen larabci ta ce" kin san cewar wannan ranar mun ci alwashinta, muna jiranta ko? Kin fi kowa sannin mun shiryawa wannan ranar ko? Kukanta, ko ihunta, ko summarta ba zai hanna mu wanketa ciki da bai ba, domin kuwa shinfidar da zata taka mai daraja ce! Dole zata koyi rayuwa da yanda zata tafiar da sarkin mu! Mace na iya shanye wuyar nakuda, hawayen da zata zubar sune samun sasauci a zuciyarta! Maganar so kuwa
Murmushi ta yi ta kai dubanta wajen Najeeba dake kwonce ta rungume fillow a jikinta gashinta ya warwatsu ko'ina, rigar aida ce a jikinta har yanzu sai shaf din pant da kafafuwanta masu tsananin hasken tafin kafa da wani shap a jikinsu ta maido dubanta kan Anmy ta kara sakin murmushi a hankali ta ce" lokaci zai nuna mana idan har ta isa ta kaucewa zuciyar *GURNANIN ZAKI*
..................salam alll........🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
35
Ajiyar zuciya Anmy ta kuma saukewa ta koma gefe tana kallon su
Karasawa babar cikinsu ta yi ta saka hannunta a hankali ta yi bismillah
Sauran du dukar da kawunnansu suka yi har sai da ta saka hannayen nata cike da kula ta talabo Najeeba
Idannuwanta ta buda a hankali kafin ta ware su da sauri tana kallon matar
Tamkar wasu kannanun yara sai da ya masu adu'ar tsari , ya kara tsayawa a wajensu har ya ga ta daina kukan baki bude sai hawaye dake bin gefen kumatunta, sosai abin ke damunsa aman zai jure dan idan bai nuna mata ba wani abu dan tana kuka ba tabas zata rikita su
Sai da ya sauke ajiyar zuciya sannan ya fita ya ja kofar yana kara sauke ajiyar zuciya tare da goge hawayensa
Cikin nutsuwa ya yiwa su Anmy bayanin cewa a ci gaba da shirye shirye!
Nan take Anmy ta dauki wayarta ta koma gefe ta yi kiran mutanen da ita suke jura, mutanen da ta yiwa wannan lokacin tanadi, wa'inda zasu saka Najeeba daka har sai lokacin ya yi su fito, mutanen dake kula da gimbiyar saudiya, tun da aka fadi maganar ta kakabe dukiyarta ta shiga shirye shirye, ta dauko su ta sauke su a wani tankamemen gidan SULTAN, jiran yau suke dama su taho
Tun da suka zube kawunnansu ke kasa jikinsu ke bari basu iya dagowa ba haka kuma bakinsu bai daina furta kalmomin ban hakuri da neman afuwar saken da suka yi har ta bace masu
Amintacensa ne ke fada tamkar zai kai masu bugu tare da nuni cewar zai cenza su ya maida su filin horon dogarai domin a irin abinda suka nuna ba za'a iya bugun kirji da su ba a filin daga ba!
Sai da ya kara lashe lebensa na kasa da yake jin a yau ya cika bushe masa kafin ya buda bakinsa a hankali ya ce" a ina kuka hadu da ita? Tana cikin wani yannayi? A ina ta cenza suturar da ta fita da ita?
Baban ne ya kara sada kansa ya nemi afuwa sosai kafin ya kora bayanin abinda suka sanni da inda suka ganta da kukan da take
Komawa ya yi ya jinginar da bayansa jikin kujerar da yake zaune ya mayar da idannuwansa ya lumshe
Da yan yatsunsa ya yi masu nuni cewar su tafi
Da sauri suka kara dukawa kamar zasu kwonta sunna ta neman afuwa kafin su fito daga falon
Kara zubewa Amintace ya yi kansa kasa ya shiga neman afuwar Sultan , domin du horon dogarai na gidan nan a hannunsa yake haka kuma idan suka aikata laifi yana da baban kaso a ciki
Idannuwansa da suka kara yi masa nauyi ya buda da kyar yana kallonsa
Sai da ya furzar da huci mai zafi kafin ya ce" daga yau, bata da wani mai tsaronta sai kai, du inda zata saka kafarta ka saka, du abinda zata ci ka fara tabawa, du wanda zai mu'amalanceta ka hana
Da mamaki kansa a kasa yake amsawa, ya cika da matsanancin mamakin jin cewar shi, shine zai tsare wannan yarinyar? shi rantsatsen mai baiwa Sarki tsaro ne, ko Gimbiya bai taba baiwa tsaro ba baban yaronsa ke bata tsaro aman yau shine aka wakilta da maganar baiwa wannan yarinyar tsaro?
Kara tasowa ya yi daga jikin kujerar yana kara dunkule hannunsa ya kara kakausa muryarsa ya ce" *hukunci zai hau wuyanka ne daga bakin lokacin da ta zile maka ka nemeta ka rasa, shu'uma ce, zata iya shiga duban mutane ka lalubeta ka rasa, hakan zai wanzar da tashin hankali a rayuwarka!*
Yana gama fada ya mike tsaye ya shiga takawa shi kuwa amintacensa kansa a sade a kasa yana fadin" Allah ya huci zuciyar mai damagaram, Allah ya huci zuciyar zaki, namu sarkin sarakaine na gida da dawa, Allah ya kara maka lafia da nisan kwana
Dakatawa ya yi, bai juyo ba daga inda yake ya furta" ka saka a binciki wacece *NADIA MOCTAR a UNIVERSITY*
Daga haka ya shige ciki yana jin wani irin al'amari mai girman gaske dake damunsa
Ta ina zai bi ya horata?
Ya je ya zubar da kansa ya shiga jikinta dan ya samu kusancin da zai kamata tsamo tsamo da laifin da take aikatawa sai gashi a lokacin da ta aminta ta bashi numberta harma suka fara sakarwa junna fuska ta hanyar yin yar doguwar hira da junna shine za'a katse? Shi ne zai auri yarinyar nan, nan da kwana goma?
Kansa ya daga ya kai wajen agogo,
Idannuwansa ya lumshe a lokacin da ya ga har karfe goma sha biyu ta gifta a ransa ya furta *aa ba kwana goma bane, kwana tara ne*
Lebensa ya kara cijewa na kasa yana mai ajiye rawaninsa
Hannunsa mai cike da yannayin karfi ya daga yana yamutsa summar kansa da ta taru wace yake so ya shiga ya aske kayansa da kansa
Idannuwansa ya kuma budewa a kasan zuciyarsa yake furta" da ace kin kilace kanki, da ke din babar harka ce da ba dai yaro ba sai dai baban yaro
Sai gashi kin banzatar da kanki,
Idannuwansa da suka dauki kalar ja dan bacin rai ya kara budawa yana furta"
Zaki zama matana ne, sai dai rayuwarki zata zama cikin kunci
Abinda kika saba da shi, kina ji kina ganni zai gagare ki, sai ya zame maki fiye da zinari domin zaki nema ruwa a jalo ki rasa shi, zan saka maki matakan tsaron da ko dan jaririn namiji ba zaki gani ba bale ki hadiyi yawunki a kansa
Zan kasance maki fitinar da baki taba tunanin zata shigo ratuwarki ba! (Ma ji ma gani)
Sai da ya shige sannan ya dago kansa
Ransa bace ya mike ya fita daga falon yana cike da matsanancin bacin rai
Du darajarsa? Du girmansa za'ace yanzu an nada shi kula da yarinya karama irin wannan?
To wai, meye girman darajarta da za'a nada shi, shi ya bata kula?
Meye tsakaninta da shi?
Sai kuma maganar Nadia Moctar, ta ina zai fara bincikenta? Nadiar nawa ce a cikin University?
Dole zai dauki wayarsa ya yi aikin, tunani yake me hadinsa da wata Nadia?
Wani murmushi ya yi yana girgiza kansa, wani auren zaka sake? Halitarka ba ta mace daya bace,
Kansa ya girgiza yana kara wani murmushin a kasan zuciyarsa ya furta
*Ga fili, ga mai doki*
Idannuwanta bude suke har goshin asuba
Ta kasa yarda cewa itane haka ke shirin faruwa da ita
Ta kasa tsayar da takamaimai abinda zata yi da rayuwarta
elle n'arrive pas a y croire (ta kasa yarda), cewar ita Najeeba, itane haka ke shirin faruwa da ita
Lokaci daya ta ringa da ta sannin rayuwa
Ashe du irin tara samarin nata zata kare a auren dole ne bata sani ba?
Sai kuma ta ji zuciyarta ta raunata, a hankali zuciyarta ta ringa kara rufeta da fada kamar haka" dole Allah ya kama ki Najeeba, ke ce zalinci wancen, yiwa wannan karya, cin kudin wancen, mazan da kika saka hawaye yawa ne da su ashe ke banza bami san cewa haka zaki kare ba? Ta tabata idan har ya yarda ya amshi aurenta ba dan wani bane sai kawai dan ya idasa nufinsa na son kasheta
Wani irin shakarsa take ji a kasan zuciyarta, zata iya rantsewa rabonta da ta shiga harkar matarsa ko shi din kansa tun da ta ganni ido da ido yana rike wuyan maciji harma ya saka yar yatsarsa a wajen bakinsa ya ringa fitar da wani ruwa mai duhun gaske
Tana kallonsa yana kallonta ya yi mata wanka da ruwa masu sanyin gaske bayan ya san tana fama da cutar athsma
A haka, bata yi masa komai ba ina da ta yi masan?
Sai goshin asuba barci mai wani irin nauyi ya kwasheta wanda sam bashi da dadi sai mafarkai mararsa dadi sosai a cikinsa
Da duhu duhu mata shida suka shigo har dakin da yan matan Anmy suke, wa'inda suke saman salaya sun gama sallah aman sun raba adu'a sunna yi dan Allah ya tankwasa yar uwarsu
Saman bed din Anmy ta kai dubanta bayan ta amsa gaisuwarsu
A hankali ta furta" bata yi baci ba jiya?
Ummulkhair ta gyada kanta kafin ta sada kanta
Matan nan fararen larabawa ne, kusan su duka farare ne tas tas sai wani irin shu'umin kamshi suke ga fatarsu kamar ka kali kanka a ciki
Anmy ta kai dubanta kansu a sanyaye ta ce" ban san ta inda zamu fara ba, bana iya yi mata tsawa ko na rufeta da fada, abinda na sani idan ta farka ta ganni zata so tayar da rigima, gashi dole a yau za'a sakata dakin dumin cen da gyara ku kanku ba zaku kuma fitowa ba bale ita sai ana gobe daurin auren, ban san ta yaya zata amince da abubuwan nan ba, ga wajen aikinta, ga ..................
Hannunta da datijuwar ciki ta rike ya saka Anmy sauke numfashi a maganarta tana ta lumshe idannuwanta domin sam bata so ta ga Najeebar a cikin wani yannayi na rashin jin dadi
Cikin harshen larabci ta ce" kin san cewar wannan ranar mun ci alwashinta, muna jiranta ko? Kin fi kowa sannin mun shiryawa wannan ranar ko? Kukanta, ko ihunta, ko summarta ba zai hanna mu wanketa ciki da bai ba, domin kuwa shinfidar da zata taka mai daraja ce! Dole zata koyi rayuwa da yanda zata tafiar da sarkin mu! Mace na iya shanye wuyar nakuda, hawayen da zata zubar sune samun sasauci a zuciyarta! Maganar so kuwa
Murmushi ta yi ta kai dubanta wajen Najeeba dake kwonce ta rungume fillow a jikinta gashinta ya warwatsu ko'ina, rigar aida ce a jikinta har yanzu sai shaf din pant da kafafuwanta masu tsananin hasken tafin kafa da wani shap a jikinsu ta maido dubanta kan Anmy ta kara sakin murmushi a hankali ta ce" lokaci zai nuna mana idan har ta isa ta kaucewa zuciyar *GURNANIN ZAKI*
..................salam alll........🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
35
Ajiyar zuciya Anmy ta kuma saukewa ta koma gefe tana kallon su
Karasawa babar cikinsu ta yi ta saka hannunta a hankali ta yi bismillah
Sauran du dukar da kawunnansu suka yi har sai da ta saka hannayen nata cike da kula ta talabo Najeeba
Idannuwanta ta buda a hankali kafin ta ware su da sauri tana kallon matar