Sashe 81
Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Iskar da ta fesar me ta ci gaba da fadin" idan har ciwom cikin ya yi wani mugun tsanani ne a kirayi likita sannan a fada mana mana mu sai mu zo mu kula da ita baku daya aman sai ka yarda da maganar Najeeba cewar ta sadaukar da satinta a wajen aminiyarta dan kawai bata da lafia kai ne kadai zaka iya kula da ita ko me?
Idannuwansa ya buda daga lumshewar da yake ya kurawa waje daya ido
Haka ta fada? Ya tambayi kansa, maganarsa da sarkin Agadez ce ta fado masa a rai inda yake fadin" da kyar in zan iya baci, ban taba sannin darajar mace mai fatar Zahrau ba sai da na hadu da zahrau, lalle zan ringa begenta na lokutan da ta dauka
Sultan, ka riki matarka, ina mai tabatar maka zaka yi bayani
Saurin korar zancen ya yi yana tunanin meye kuma na tuna zancen?
Wayar ya duba ya ga ba'a kashe ba, wato dai a kunne Anmy take kan karyar y'arta?
Murmushi ya yi a sanyaye ya furta" Allah ya huci zuciyar Anmy
Anmy ta girgiza kanta kawai tana kashe wayar ta dubi Ummu dake sauraron du abinda ya faru ta shiga yi mata bayani
To a wannan darema ya rabu da Nadia, ya rabu da n'imarta, sun raya daren duda ita din damuwarta daya ce daga ta ga alamu sai ta kama hawaye da magiya
......................................
A haka suka ringa raya darensu tare,
A daren da ya kama na biyar a garesu ya yi kokarin kunna fitila dan kallon Nadia a fili
Idannuwansa ya mayar ya lumshe da sauri sai kawai kamaninta suka fito a fatar idannuwan nasa
Tun daga kanta har kafafuwanta ne suka saka shi saurin buda idannuwan nasa daga lumshe yana kallon waje guda
A hankali ya mike tsaye ya nufi bayi cikin zuciyarsa yana dauke da adu'ar kore shetan
Baki dayama sai ya dauro alwallah ya fito daga bayin ya nufi darduma
Ya raya daren ne a nafila kafin ya nem8 wajen hutawa ya kwonta
Washe gari, ahine ranar da zasu kuma haduwa a bangarensa baki daya
Ranar ya kasamce kwana shida da farin kwanan daya a bangarensa kwana akwai kuma da daurin aurensu
Tun karfe bakwai ta shige daki da niyar kimtsawa ta cewa iyayenta tana zuwa wa'inda suka shiga hada hadar fitar da suturar da zata saka dan wannan rana.............
A ci weekend lafia🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
42
Ba wata kwaliya ta yi ba, ko daya bata sakawa fuskarta wani lamari na kwaliya ba sai gashin idon da ta zauna ta dora shi das a idanuwanta kafin ta idasa gyara fuskarta ta hanyar gyara sajen gefe da gefen fuskar nata ta hade gashinta waje daya ta d'aure.
Sket da riga na shada color blue mai duhu ne suka ciro mata
Ta zo saka sket din ya shige aman zif d'in da k'yar ya janyu har Anmy na fadin ko a cenza wasu ne?
Rigar ta saka mai dogon hannu budade sosai an yiwa rigar gidan mama dan ko bra bata saka ba kafin ta d'auki dan kwali ta sasauta gashinta kasa sosai ta d'ora masa daurin Zarah buhari das das a saman kanta.
Wata yar siririyar sarka da dan kunne siraru ne aka bata ta saka kafin ta amshi alkyabar da aka miko mata ruwan pink domin zubin jikin shadarma ruwan pink din ne.
Takalma masu tsini sosai ta saka a kafarta kafin a wanketa da turare mai k'amshin gaske.
Murmushi ta yiwa Su UMMU dake biye da ita sunna hira kasa kasa , ba komai suke son sanni ba sai wai yaya kamaninsa suke?
A daidai kofar shiga ta juyo tana kallonsu ta ce" dan Allah ku tsayani mana? Kun ji An ce k'arfe takwas ake zaman , na tabata ba za'a jima ba ni na tsani ina bin hanyar nan ana wani gaisheni uwa wata shugabar kasa.
Ummulkhair ta ce" aa, ke kuwa wani irin jira tsakani da Allah? Ki rufa mana asiri kar a je a ganmu tsaye a kofar nan a zata wani abin ne."
Murmushi ta yi ta dan tura kofar mai dauke da maduban da ba"a hango na ciki aman tun tsayuwarsu su suna ganinsu daga ciki.
Sai da ta dan shige kadan kafin ta saka hannunta ta cire alkyabar nan ta jefowa Ummukulsum da ta fi kusa da ita tana daria ta juya kasa kasa ta ce" sai ku tafin ai na gani."
D'ago idanuwanta da take suka sauka a saman fuskokinsu.
Sai da gabanta ya kwonci kwonci ya fadi kafin da sauri NADIA ta sada kanta tana jin gabanta na dukan sitin sitin.
A hankali ta yi kasa kasa da dubanta kafin ta cije ta kuma dago idannuwanta tar ta sauke a cikin nasa
A hankali ta ringa takowa, kafarta sanye da takalminta bata cire , sannan idannuwanta a cikin nasa
Murmushi ne yake kokarin subuce masa sannan tar yana mai kallon idannuwan nata yana son ganin iya gudun ruwanta.
Ji take kamar za'a dauketa a nanata da kasa , ji take ta fara jin wata irin juwa mai karfin gaske sanadiyar kallon junnan da suke
Ji take idannuwansa na zama kamar wani mashi sunna son sukar nata
A hankali ta ji kwalah na taruwa a cikin idannuwan nata
A hankali ta lumshe su domin ta yarda , idannuwansa sunna dauke da wani sirri na daban sai dai gagar jikinta ba zata tsaya daga kusantarsa ba
Sai da ta kusa gareshi kafin ta cire dubanta daga wajensa ta maida wajen Nadia
Murmushi ta kakaro a hankali ta furta" *Asalamu alaikum*
Da sauri Nadia ta dago dan duban fuskarta, kuma sada kanta ta yi kasa sosai dan jin tsoronta take har ranta
Muryarta na rawa ta furta" Amen wa alaiki salam
Dubansa ya cire daga kan NAJEEBAR ya kai wajen Nadia , kwarai ya yi mamakin yanda a bayane take barin jikin tsoron kalonta, kuma kallon NAJEEBA ya zo yo a tunaninsa stil tana tsaye somin kamshin turarenta na nan, sai dai ya ga ta je wajen zama ta zauna, kafafuwanta ya bi da kallo, takalman dake jikinsu ya bi da kallo
Neman izinin shigowar da ake ne ya saka shi lumshe idannuwansa ya maida dubansa bakin hanyar
Sai da aka dauki minutes kamar biyu kafin ya yi gyaran murya.
Jakadiya ce ta bayanna a duke sosai ta furta" ALLAH ya taimake ka, ZINARIA na kwonce zazabi ke damunta, shine GIMBIYA ta umarceni na isar da sakon gaisuwa sannan na shaida cewar ba zata samu halartar taron yau ba, tana neman alfarmar a matsa shi zuwa gaba
Kansa ya maida ya jinginar jikin kujerar da yake zaune,
Idannuwansa ya lumshe a kasan zuciyarsa yana furta" Ba zata kwontar da hankalinta ba?, me ya sa ta cika daukan lamarin duniya da zafi? Shi bai ga abin tada hankali dan an maka kishiya ba, kishiyoyinma yara kanana zata wani fitini kanta, zuwansa biyu da kansa har bangarenta, sai tarota yan uwanta suke ta saka sun tare bayan du da mazajensu aman sun kasa tafia domin nunawa take kamar zata mutu,
Idannuwansa ya bude da yan yatsunsa ya salameta hakan ya sa ta yi ta godiya kafin ta tafi.
Sai da ta zauna ta ji wata irin kunya ta lulube zuciyarta hakan ya sa ta kama lebenta na kasa ta lumshe idannuwanta tana dan tsotsa
Jin shirun ya yi yawa ya saka Nadia dago dubanta
A kan Najeeba ta fara dorawa
Lale ita tana dauke da farar fata, Najeeba kuwa bakar fata aman bata taba gannin kalar fatar dake birgeta irin ta Najeeba ba, yanzun sai take gannin Fatar tata ta kara wani fasowa
Inama ace zata saurareta? Inama ace zata iya samun kwarin gwuiwar tunkararta?
A hankali ta kai dubanta wajen Sultan,
Ita kam rayuwar sarauta ta fara bata wahala ba magana, shiru d'in nan na menene? Tana kai dubanta ta ga idannuwansa kamar a lumshe suke aman kasa kasa a kan Najeeba suke, wannan kallon, wannan kallon shine kallon da Najeeba ke yawan fadi cewar yana tsareta da kallon tsana ko wani kallo ne daban? Ita sai take fasara kallon nan a matsayin irin kallon da yake mata idan yana cikin hali na zai je gareta
Kanta ta k'ara sadawa ganin daga yanda yake, idanuwan nasa a kan Najeebar ya budi bakinsa a hankali ya furta" *Zaman yau ba zai yiwu ba, sai dai zuwa lokacin da Zinaria ta samu lafia*."
Dan saurarawa ya yo kafin ya dago dubansa ya cire daga kanta ya d'ora kan Nadia , wanda hakan ya fadar mata da gaba domin tuni launin idannuwansa sun canza kala
Ya furta" *Zaku iya tafia*."
Yana kai Aya ita ta fara mikewa, a hankali kasa kasa ya kuma dora idannuwansa a kan bayanta,
Da sauri ya rintse lokaci daya kansa ya sara masa
*WHY? WHY? ZALAMARKI TA HANA MAKI HAKURIN LOKACIN DA ZAKI MORI HAKAN YA ZO GAREKI?*
Ya tsinci zuciyarsa na tambayarsa
Bai iya cire dubansa ba sai da ya ga ta amshi Alkyabar nan kafin ya cire kansa ya mika hannunsa ya rike na Nadia
Gabanta ne ya fadi, yau take kare kwana a bangarensa, aman ji take dama ya sawake mata kwanan yau
Ta kasa sabawa, kwata kwata ta kasa sabawa
Bata yi rayuwar biye biyen maza ba, tabas sun kasance masu saka kannanun kaya aman sam rayuwar bin maza ba nasu bane
Ita, bata fiya kallon BP ba, sannan ba mai karance karance bace
Kwarai lamarin nan ke bata wahala, har yau kuwa tun kallo daya da ta masa ta kasa kuma masa wani irin kallon na tsanaki
Idan ya yi tsaye a gabanta nan da nan take rikicewa, tsoronsa take ita kam kwarai da gaske
Bayan komawarsu wani zaman hiran suka bude kafin ta amsa kiran Anmy ta sakata bacin wuri wand ata yi hakan ne dan gobe itace da daukan girki
Idannuwansa ya buda daga lumshewar da yake ya kurawa waje daya ido
Haka ta fada? Ya tambayi kansa, maganarsa da sarkin Agadez ce ta fado masa a rai inda yake fadin" da kyar in zan iya baci, ban taba sannin darajar mace mai fatar Zahrau ba sai da na hadu da zahrau, lalle zan ringa begenta na lokutan da ta dauka
Sultan, ka riki matarka, ina mai tabatar maka zaka yi bayani
Saurin korar zancen ya yi yana tunanin meye kuma na tuna zancen?
Wayar ya duba ya ga ba'a kashe ba, wato dai a kunne Anmy take kan karyar y'arta?
Murmushi ya yi a sanyaye ya furta" Allah ya huci zuciyar Anmy
Anmy ta girgiza kanta kawai tana kashe wayar ta dubi Ummu dake sauraron du abinda ya faru ta shiga yi mata bayani
To a wannan darema ya rabu da Nadia, ya rabu da n'imarta, sun raya daren duda ita din damuwarta daya ce daga ta ga alamu sai ta kama hawaye da magiya
......................................
A haka suka ringa raya darensu tare,
A daren da ya kama na biyar a garesu ya yi kokarin kunna fitila dan kallon Nadia a fili
Idannuwansa ya mayar ya lumshe da sauri sai kawai kamaninta suka fito a fatar idannuwan nasa
Tun daga kanta har kafafuwanta ne suka saka shi saurin buda idannuwan nasa daga lumshe yana kallon waje guda
A hankali ya mike tsaye ya nufi bayi cikin zuciyarsa yana dauke da adu'ar kore shetan
Baki dayama sai ya dauro alwallah ya fito daga bayin ya nufi darduma
Ya raya daren ne a nafila kafin ya nem8 wajen hutawa ya kwonta
Washe gari, ahine ranar da zasu kuma haduwa a bangarensa baki daya
Ranar ya kasamce kwana shida da farin kwanan daya a bangarensa kwana akwai kuma da daurin aurensu
Tun karfe bakwai ta shige daki da niyar kimtsawa ta cewa iyayenta tana zuwa wa'inda suka shiga hada hadar fitar da suturar da zata saka dan wannan rana.............
A ci weekend lafia🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
42
Ba wata kwaliya ta yi ba, ko daya bata sakawa fuskarta wani lamari na kwaliya ba sai gashin idon da ta zauna ta dora shi das a idanuwanta kafin ta idasa gyara fuskarta ta hanyar gyara sajen gefe da gefen fuskar nata ta hade gashinta waje daya ta d'aure.
Sket da riga na shada color blue mai duhu ne suka ciro mata
Ta zo saka sket din ya shige aman zif d'in da k'yar ya janyu har Anmy na fadin ko a cenza wasu ne?
Rigar ta saka mai dogon hannu budade sosai an yiwa rigar gidan mama dan ko bra bata saka ba kafin ta d'auki dan kwali ta sasauta gashinta kasa sosai ta d'ora masa daurin Zarah buhari das das a saman kanta.
Wata yar siririyar sarka da dan kunne siraru ne aka bata ta saka kafin ta amshi alkyabar da aka miko mata ruwan pink domin zubin jikin shadarma ruwan pink din ne.
Takalma masu tsini sosai ta saka a kafarta kafin a wanketa da turare mai k'amshin gaske.
Murmushi ta yiwa Su UMMU dake biye da ita sunna hira kasa kasa , ba komai suke son sanni ba sai wai yaya kamaninsa suke?
A daidai kofar shiga ta juyo tana kallonsu ta ce" dan Allah ku tsayani mana? Kun ji An ce k'arfe takwas ake zaman , na tabata ba za'a jima ba ni na tsani ina bin hanyar nan ana wani gaisheni uwa wata shugabar kasa.
Ummulkhair ta ce" aa, ke kuwa wani irin jira tsakani da Allah? Ki rufa mana asiri kar a je a ganmu tsaye a kofar nan a zata wani abin ne."
Murmushi ta yi ta dan tura kofar mai dauke da maduban da ba"a hango na ciki aman tun tsayuwarsu su suna ganinsu daga ciki.
Sai da ta dan shige kadan kafin ta saka hannunta ta cire alkyabar nan ta jefowa Ummukulsum da ta fi kusa da ita tana daria ta juya kasa kasa ta ce" sai ku tafin ai na gani."
D'ago idanuwanta da take suka sauka a saman fuskokinsu.
Sai da gabanta ya kwonci kwonci ya fadi kafin da sauri NADIA ta sada kanta tana jin gabanta na dukan sitin sitin.
A hankali ta yi kasa kasa da dubanta kafin ta cije ta kuma dago idannuwanta tar ta sauke a cikin nasa
A hankali ta ringa takowa, kafarta sanye da takalminta bata cire , sannan idannuwanta a cikin nasa
Murmushi ne yake kokarin subuce masa sannan tar yana mai kallon idannuwan nata yana son ganin iya gudun ruwanta.
Ji take kamar za'a dauketa a nanata da kasa , ji take ta fara jin wata irin juwa mai karfin gaske sanadiyar kallon junnan da suke
Ji take idannuwansa na zama kamar wani mashi sunna son sukar nata
A hankali ta ji kwalah na taruwa a cikin idannuwan nata
A hankali ta lumshe su domin ta yarda , idannuwansa sunna dauke da wani sirri na daban sai dai gagar jikinta ba zata tsaya daga kusantarsa ba
Sai da ta kusa gareshi kafin ta cire dubanta daga wajensa ta maida wajen Nadia
Murmushi ta kakaro a hankali ta furta" *Asalamu alaikum*
Da sauri Nadia ta dago dan duban fuskarta, kuma sada kanta ta yi kasa sosai dan jin tsoronta take har ranta
Muryarta na rawa ta furta" Amen wa alaiki salam
Dubansa ya cire daga kan NAJEEBAR ya kai wajen Nadia , kwarai ya yi mamakin yanda a bayane take barin jikin tsoron kalonta, kuma kallon NAJEEBA ya zo yo a tunaninsa stil tana tsaye somin kamshin turarenta na nan, sai dai ya ga ta je wajen zama ta zauna, kafafuwanta ya bi da kallo, takalman dake jikinsu ya bi da kallo
Neman izinin shigowar da ake ne ya saka shi lumshe idannuwansa ya maida dubansa bakin hanyar
Sai da aka dauki minutes kamar biyu kafin ya yi gyaran murya.
Jakadiya ce ta bayanna a duke sosai ta furta" ALLAH ya taimake ka, ZINARIA na kwonce zazabi ke damunta, shine GIMBIYA ta umarceni na isar da sakon gaisuwa sannan na shaida cewar ba zata samu halartar taron yau ba, tana neman alfarmar a matsa shi zuwa gaba
Kansa ya maida ya jinginar jikin kujerar da yake zaune,
Idannuwansa ya lumshe a kasan zuciyarsa yana furta" Ba zata kwontar da hankalinta ba?, me ya sa ta cika daukan lamarin duniya da zafi? Shi bai ga abin tada hankali dan an maka kishiya ba, kishiyoyinma yara kanana zata wani fitini kanta, zuwansa biyu da kansa har bangarenta, sai tarota yan uwanta suke ta saka sun tare bayan du da mazajensu aman sun kasa tafia domin nunawa take kamar zata mutu,
Idannuwansa ya bude da yan yatsunsa ya salameta hakan ya sa ta yi ta godiya kafin ta tafi.
Sai da ta zauna ta ji wata irin kunya ta lulube zuciyarta hakan ya sa ta kama lebenta na kasa ta lumshe idannuwanta tana dan tsotsa
Jin shirun ya yi yawa ya saka Nadia dago dubanta
A kan Najeeba ta fara dorawa
Lale ita tana dauke da farar fata, Najeeba kuwa bakar fata aman bata taba gannin kalar fatar dake birgeta irin ta Najeeba ba, yanzun sai take gannin Fatar tata ta kara wani fasowa
Inama ace zata saurareta? Inama ace zata iya samun kwarin gwuiwar tunkararta?
A hankali ta kai dubanta wajen Sultan,
Ita kam rayuwar sarauta ta fara bata wahala ba magana, shiru d'in nan na menene? Tana kai dubanta ta ga idannuwansa kamar a lumshe suke aman kasa kasa a kan Najeeba suke, wannan kallon, wannan kallon shine kallon da Najeeba ke yawan fadi cewar yana tsareta da kallon tsana ko wani kallo ne daban? Ita sai take fasara kallon nan a matsayin irin kallon da yake mata idan yana cikin hali na zai je gareta
Kanta ta k'ara sadawa ganin daga yanda yake, idanuwan nasa a kan Najeebar ya budi bakinsa a hankali ya furta" *Zaman yau ba zai yiwu ba, sai dai zuwa lokacin da Zinaria ta samu lafia*."
Dan saurarawa ya yo kafin ya dago dubansa ya cire daga kanta ya d'ora kan Nadia , wanda hakan ya fadar mata da gaba domin tuni launin idannuwansa sun canza kala
Ya furta" *Zaku iya tafia*."
Yana kai Aya ita ta fara mikewa, a hankali kasa kasa ya kuma dora idannuwansa a kan bayanta,
Da sauri ya rintse lokaci daya kansa ya sara masa
*WHY? WHY? ZALAMARKI TA HANA MAKI HAKURIN LOKACIN DA ZAKI MORI HAKAN YA ZO GAREKI?*
Ya tsinci zuciyarsa na tambayarsa
Bai iya cire dubansa ba sai da ya ga ta amshi Alkyabar nan kafin ya cire kansa ya mika hannunsa ya rike na Nadia
Gabanta ne ya fadi, yau take kare kwana a bangarensa, aman ji take dama ya sawake mata kwanan yau
Ta kasa sabawa, kwata kwata ta kasa sabawa
Bata yi rayuwar biye biyen maza ba, tabas sun kasance masu saka kannanun kaya aman sam rayuwar bin maza ba nasu bane
Ita, bata fiya kallon BP ba, sannan ba mai karance karance bace
Kwarai lamarin nan ke bata wahala, har yau kuwa tun kallo daya da ta masa ta kasa kuma masa wani irin kallon na tsanaki
Idan ya yi tsaye a gabanta nan da nan take rikicewa, tsoronsa take ita kam kwarai da gaske
Bayan komawarsu wani zaman hiran suka bude kafin ta amsa kiran Anmy ta sakata bacin wuri wand ata yi hakan ne dan gobe itace da daukan girki