← Book details Mage Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 24 OF 138

Sashe 24

Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Wata budurwa mai ji da kanta ce ke kallonta tun dazun, ita kanta ta lura da kallon sai ta share dan ba magana ta mata ba gashi kana ganninta zaka gane irin yan matan nan ne masu jiji da kansun nan

Sai da ta gama ta dauki jan baki a cikin kayan mak up din ta shafa kalar lebenta ta juyo

Wauh budurwar ta fada a lokacin da bata shirya ba tana kallon Najeeba
Murmushi ta sakar mata ta mike ta mika mata hannu

Itama hannun ta bata suka gaisa kafin ta dan sakar mata murmushi

Budurwar ta ce" kina da kyau sosai, na yaba

Wani dan murmushin NAJEEBA ta yi mata tana kallon kafarta
Irin sarkar da ta gani da kuma zobe a yatsarta ya shaida mata ko wacece ita
Dan rabata ta yi kusa da kunnenta kasa kasa ta ce" sorry, na haramta bin mata

Budurwar kadai ta ji sai ita da ta fada , tana fada ta shige ciki ta daura alwallah ta gabatar da salar la'asar sannan ta ci gaba da zama da carbinta irin na hannun nan tana dan dannawa a hankali a hankali

Sai da dare ya yi ta dauki kanwarta, ta gama hada kan kudaden da aka samu a ranar ta hada da takardar gidan wuta da ruwa da aka kawo masu ta salami sauran baki daya sannan ta rufe ta yi adu'o'i ta totofa sannan ta tayar da motarta ta nufi gida

A kofar dakin mamanta ta sauketa tana mata byby, yarinyar ta ringa nokewa ba zata je ba dan ba karamin dadi ta ci a wajen Najeebar ba ga wasan da suka yi ta yi na goyo a dakin ga ta bata wayarta ta yi ta dannawa

Daukan yarinyar ta yi ta nufi bamgarensu da ita dan sam ta ki ta shiga wajen mamanta

Sunna shiga ta yi turus sakamakon gannin yayunta du sunna tsaitsaye da alama ita akae jira

Yayanta ne da fada fada ya ce" daga gidan ubanwa kike Najeeba?

Da mamaki take kallonsa ta ce" yaya, daga saloon nake mana ina zan je ni kuwa yau?

Ummulkhair ta ja tsaki ta ce" a saloon din naki ne kuka yi fada yau? Gashi har an kai kararki gidan sarki ga samaci an kawo wai ke kam me ke yawo a cikin kwakwaluwarki na masifa ne? Me ya hada ki fada da matar ambasador?

Gaban goshinta ta dafe a lokacin da Bilkissu ke fadin" aunty, me yasa kika tafi da Nusaiba kin ga mamanta ta yi ta zage zage da fada tana fadin zaki lalata mata yarinya har a gaban abih

NAJEEBA ta ringa gyada kanta a hankali ta ce" inaga sai na sha magannin baki yaya, ka ji fa kowa ni na masa laifi yau harda kai? Yaya to ka san me ta min ne?

Koma me ta maki sai ki duba yannayin da Anmy ke ciki, gashi shara'ar karfe hudu za'ai maku da wahala ace sarki baya nan! So kike a kara zuwa a fada mata cewa gaki cen yauma wata ta kawo kararki? Ke bakya tsoron kur'anin da ake saka maki ya lalata ki ne? Ina dalili wai ke kamar yar agunla?

Bani y'ata! Bani y'ata
Kuma daga yau kar ki kuma daukan min y'ata ja fada maki, haka kawai kin fi karfin uban da ya haife ki ki koyawa y'ata irin fitintinun ki?
Tana fada tana warce Nusaiba dake hannun Najeeba

Najeeba ta sakar mata yar, tana kallonta

Zahrau ta ce" subahannalah, ke kuwa meye hadinki da shiga tsakaninmu da yar uwarmu? Kin taba gannin mun sakota a cikin matsalarmu da ke? Dan Allah ki daina zagar mana yar uwarmu, yau koda Najeeba yanda kike fadi ne ai bai dace ki ringa zaginta haka ba
Kema fa macen kika haifa, kuma kema mace ce, bale kanwata ba yar iska bace walahi, ki fita a harkar shiga tsakaninmu da Nusaiba, Najeeba ba zata taba cutar da Nusaiba ba, na san ko baki daya mun mutu koda dako ne Najeeba zata yi ta rike kanwarta dan Allah ki shafa mana lafia hakannan mana kema?

Sai da ta harareta sama da kasa ta yi daria irin ta wulakancin nan ta ce" wai kililin kasau macijin kumba
Wace ake kawo sadakinta ana fardewa ne zata nemi ta bani shawara? Munanan halayanki sun hana maki samun mijin aure kina wani kumbiya kumbiya ke ga ta kirkinsu ko? To bari ki ji, a tafin hannuna kuke baki dayanku kuma ma rantse maku baku isa ku raba ni da gidan nan ba
Ko a irin yanda na fi sauran iyayenku jimawa da mutumen nan kun san ya mace a so na
Matar ubanku nake dan haka dole a kira ni mama

Ummukulsum ta budi baki zata yi magana da sauri Dayabu ya dubeta duba irin na ido cikin ido

Muryarsa har rawa take ya ce" Mardiya me yasa kike mana haka ne? Yaya kike tunanin cin riba idan har kika shiga tsakaninmu da yar uwarmu? Kin tabata zaki kai girmanta zaki iya tarota zaki iya rayuwa da ita ke daya kin iya mata?

Tana zaro idannuwanta irin masifa na cinta ta ce" eh, ba abinda ya shafeku da y'ata ba domin baki dayanku kun kasance jinnin masifa karku koyawa y'ata

Daria ya yi yana girgiza kai ya ce" haka ne, aman masifar inaga itama jinnin nata ne idan kika yi la'akari da ubanmu ne daya baki daya
MARDIYA, ba dai NUSAIBA ba? Nusaiba dai ce ko? Ki rubuta ki ajiye daga yau daga kaina har zuwa wannan yar karamar dake kusana
Yana nuna yar kanwarsu wace bata fi shekara shida ba
Ya daki kirjinsa ya ce" Ni DAYABU MUTALAB idan har na isa da kannena daga bakin zahra har zuwa ummi na kankare mana wannan yarinyar daga cikinmu, yarki ko? Ki rubuta ki ajiye bamu isa mu tatse jinninta daga jikinmu ba aman mun isa mu kankareta daga cikinmu! Ko a titi, ko a cikin gida ba mu ba ita!

Gaba daya yaren mutuwar tsaye suka yi sunna kallon irin yanda ran yayansu ya gama baci,
Yana gama fada ya juya ya yi ciki ransa a matukar bace ya je ya gyara shinfidar kananu du ya kora su daki

Manyan kansu silalewa kowace ta yi, zuciyarta da mugun rauni, me ya sa ta yi wannan aika aikar ne? Me ya sa sai da ta kai mutun mai hakuri da kare yan uwansa bango har ya aiwata haka yau? Ya fi su saukin hali da kawar da kai ko dan ya kasance mamiji? Aman a yau ta kaishi bango har haka ta faru

Sun yi baci hankalinsu ba a kwonce ba
Da sasafe ta rigayi kowa barin gidan ta zarce saloon

Yau da kanta ta ringa yin aikace aikacen ta jirga zaman kujerun ta kakabe atach din dake tare ta wanwanke abubuwan wanke kafa ne, ta goge du wajen da ya yi dati

Sai da ta yi aiki jina sannan ta zauna tana maida numfashi

Da wuri wuri aka ringa cika wajen
Nan ta shiga aikinta tana yi tana duba time

Ba abinda ta ci sai da karfe uku ta yi ta bara masu ta shiga ciki

Wanka ta yi mai tsari ta gyara jikinta tsaf ta fito sanye da wata abaya mai ruwan ja mai duhu da bakin hannu
Dan kwalin abayar ta rataya a wuyanta ta fita ta shiga motarta

Bata zame ko'ina ba sai fada
Tana tsayawa ta saka gilas dinta fari dan siriri ta fito a motar

Cirko cirko ta gansu su biyar a tsaye

Ido ta zaro ta karasa wajensu a hankali ta ce" me ya kawo ku nan ku kuwa?

Yaya DAYABU ya harareta ya ce" baki da kowa ne da zamu barki ki zo ke daya?

Fuskarta ta sanyaya ta ce" eyah, na ga du na bata maku rai ne

Zahrau ta kamo hannunta ta ce" mu je lokaci ya yi Najeeba, komai bata mana da zaki yi ba zamu barki ke daya gaban mutane dubu ba

Wani sanyi da kaunarsu ce ta ji a ranta, nan suka rankaya da su ummu suka shiga bayan sun cicire takalmansu

Tun da suka zauna yake yi mata mayatacen kallo

Matarsa ta shiga bayanin a yi mata tsakani da mijinta ba ita ba shi

Da sauri ya ce" aa, Allah ya taimaki waziri ni kam ba da yawuna ba, yarinyar nan ni na je na ce ina son ta, idanma laifin ne ni na yi mata dan haka bana cikin maganar a rabani da ita dan aurenta nake son yi!

Gaba daya wajen ya yi tsit, sai Najeeba da ta kara sada kanta dan kunyar da take ji na irin kallonta du da ake

Daga inda yake tsaye ta wajen tagar dakinsa yake hango komai
Irin yanda ya fahimta yauma itace aka kawo kara

Juyawa ya yi ya karasa wajen wayarsa karama ya danna kira, idan yana son jin abinda ake fada yake hakan sai a ajiye yana jin komai

Zama ya yi ya yi zamansa na sarki ya bude litafi a hannunsa na hadisi yana dubawa still yana sauraron abinda ake fada

Kansa kawai yake girgizawa a lokacin da ya ji ambasador na neman yin sakiyar da ba ruwa ta hanyar sakin matarsa har yana daga muryarsa cewa idan har ta yarda aka sakawa Najeeba wannan layar to ta tabata a bakin aurenta

Karshe dai sai itane ta dawo bayar da hakuri cewa a bari kar a saka
Abinda ya fi bashi takaici da haushi shine yarinyar ko A bata furta ba mutanen wajen ne ke ta hayaniyarsu tun dazu, ita ga isashiya

Karshe dai kashewa ya yi a lokacin da ya ji shara'ar ta koma neman sasanci tsakanin matar ambasador da kuma Najeeba, inda aka shiga sasanta su da gindaya masu sharudan kar wace ta kuma tarban wata da neman fada, shi kuwa aka yi masa kwakwaran kashedin ya zama namiji ya tsawatarwa iyalinsa sannan idan auren Najeeba zai yi ya maida hankali ya aureta ba ya ringa neman fitina da girmansa ba

Sai kusan magariba aka sake su

Ranta kwata kwata a bace yake a yau din nan dan haka ta zarce wajen da ake siyar da shawarma

Siya ta yi isashiya sannan ta karasa wajen hutun da takan je lokuta da dama
Chapter 24 · 0% Book details