Sashe 48
Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kuma kausasa muryarsa yayi ya furta" Ba'a kyauta ba, an tafka abinda Allah ya haramta, sannan an shiga hakin baiwar Allahn da bata ji ba bata gani ba." Shiru ya kuma yi kafin ya dubi wajensu.
Muryarsa ya sanyaya sosai kafin ya furta" UMMUKULSUM, shin zaki iya jurewa, ki jajirce, ki d'auki hak'uri ki yafewa bawan Allahn nan duba da irin abubuwan da suka gabata da shaidar wace abin ya faru a sanadiyarta ? Zaki iya yafe masa har cikin zuciyarki? Ki tuna Allah na yafewa bayinsa masu yafiya ya Ummu."
Kanta dake kife a jikin kafad'ar Najeeba tun daya kama k'afarta yana gunsheken kukan nan ta ji wani irin tausayinsa ya tsirga mata haka kawai sannan wani irin tsigar jikinta ta ringa tashi, bata k'arasa jin tausayinsa ba sai da ta ji kalaman mahaifinsa da kukan mahaifinsa da shi kansa.
Gimbiya ce ta k'ara duk'awa tana kallonta muryarta na rawa ta furta" Ki rufa masa asiri, ki rufawa kanki Ummukulsum, kar ki manta kema mace ce, fitar sirin nan tamkar fitar da sirrinki ne, ki rufe shi dan girman Allah."
Cire dubanta ta yi daga kanta, muryarta na rawa ta furta" Na yafe masa."
Sai kuma ta fashe da kukan da ya saka Najeeba wace jikinta ya d'ume da zafi kanta na sarawa ita ma fashewa da kukan tana k'ara rungumeta, Zahrau kuwa ta zama wata mutun mutumi sai juya kai take baki d'aya ta rasa me take ji.
Hamdallah yayi kafin ya maida dubansa wajen sarki a sanyaye sarki ya ringa sakin ajiyar zuciya, muryarsa a sanyaye ya furta" ina neman alfarma, ina neman alfarmar a bar min ita a nan gidan, ta yi istibra'i a d'aura masu aure, domin na rantse shi zai gyara abinda ya lalata."
Daga Gimbiya har matarsa a tsorace suka kalli sarkin da ya watsar da su yana cike da jin haushinsu, sam tamkar basa wajen tun da ya masu tambaya yayi watsi dasu.
Da baya ta kai zaune tana mai d'ora hannayenta saman kanta a b'oye, kishiyarta kuwa bayan tarin tausayin yarima domin yaron yana da mutunci sosai, sai kuma tarin al'ajabin abinda ke shirin faruwa, auren yarima da matarsa aure aka yi na zobe, yar k'awar gimbiya ta k'ud da k'ud wace ak'idarsu d'aya cewar ba za'a yi masu kishiya bace ya aura, hakan yasa Gimbiyar ke taya ta yak'in maganar kishiya sai gashi a yau abu biyu ya faru da su baki d'aya, wato wanzuwar *KISHIYA* a tsarin da basu ajiyeta ba.
Kansa ya kuma sadawa yarima ya k'ara duk'awa shima yana rok'an hakan.
Ajiyar zuciya ya sauke a sanyaye ya furta" zamu juya gida a jirgin safe in sha Allahu, zan yi kira na sanar da abinda ake ciki."
A haka dole aka tashi, sarki na zaune saida kowa ya tashi sannan ya bi bayan Zahrau dake son shiga d'akin jikinta a mace.
Hannunta ya kamo ya maidota baya
A hankali ya sakata cikin jikinsa ya rungumeta yana buga bayanta kad'an kad'an kafin ya jata suka koma saman kujerar
Sai a lokacin ta samu kuka ya kubce mata cike da tsoro take nuna masa ba zata iya zama ba yan uwanta a wannan gidan da ya gama tsoratata ba.
Sosai yayi anfani da hikima ya ringa rarashinta har ta dawo nutsuwarta ta ringa sauke ajiyar zuciya da kansa ya mata alk'awarin zai nemi alfarmar malan ya bashi y'aya biyu k'annenta su tare da ita su tayata zama kafin a kawo mata Ummu.
Da wannan ya samu ta kwontar da hankalinta kafin ya rakata har d'akin suka ci gaba da gabatar da sallah baki d'ayansu suna godewa Allah da irin wannan ranar.
....................................
Zabura ya yi tsaye sai kuma ya yanke jiki ya fad'i zaune saman kafet d'in hannayensa aje saman kansa muryarsa na rawa ya furta" innalilahi wa'inna ilaihi raj.une, hasbunnalahu wani'imal wakim
aya ta tabbata a kaina ni MUTALAB gashi, abinda na aikata ya kamo ni da wuri haka a kan yarinyata."
Sai ya fashe da kuka yana kallon yanda D'AYABU ya tsurawa sarki ido kamar wanda ya suma a zaune.
Da sauri Anmy dake kukan itama ta kaleshi a firgice jin zai tona asirin da suke lullub'ewa kansu da k'afarsu, zai tonawa kansa asiri a cikin irin rud'anin nan da suke ciki zai k'ara masu wani.
Duban da Ummu ke masa ne ya saka shi k'ara sada kansa yana hawaye
Ummulkhair ta kalli Najeeba wace ita ma ita take kallo kafin Najeeba ta bud'a bakinta a hankalì tana kallon Ummulkhair tana dan yatsine fuskarta tace" eyah, eyah, yau kin yarda da ayar tambayar da na d'ora a kan maganar da Abih kan fad'a wani sa'in?"
Maida dubanta tayi wajen Abih a sanyaye ta furta" *ABIH, WACE AYA CE TA TABBATA A KANKA?*
komawa sarki yayi ya jinginar da bayansa jikin kujera yana lumshe idannuwansa, ta faru kuma ta k'are, rikicin cikin gidansu zai k'ara kunnuwa a yanzu, ya tabbata wani tashin hankalin ne zai k'ara kunno kansa hakan ya saka ya idasa had'e fuskarsa da dukan wani abu wai shi annuri ya lumshe idanuwansa a lokacin da Anmy a firgice ta kallesu tace "...
Happy juma'at🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
27
A firgice, a rikice, a tsawace Anmy ta ce" yaya muna cikin wannan tashin hankalin zaki yi mana wata tambaya kina mai kokarin tirke mun tamkar kece uwarmu mu kuwa y'ayanki?
Baki daya yan matan sai abin ya basu mamaki, yannayin Anmy din ya saka jikinsu ya yi sanyi harma du suka zuba mata ido da wani irin duba na mamaki
Anmy ta kawar da kanta tana jan hancinta tana kara rintse idannuwanta da sukai mata luhu luhu ranta hade ta ce" ku tashi ku je dakin ku
Jiki sanyaye du suka mimike, Najeeba ta kara waigowa ta kalli mahaifinta ta ga kansa a kasa sannan hannayensa sai rawa suke, ta kai dubanta wajen yayansu ta ga shima kan nasa a sade shi kuwa kuka ne yake a hankali ta saci kallon mai martaba ta ga ya yi wata kwonciya a jikin kujerar ya daga kansa sama idannuwansa lumshe rawanin dake kansa ya kara fadi sakamakon yannayin kwonciyar nasa, shigar alkyaba ne a jikinsa mai ruwan duhu wace ke da igiya wajen wuyanta, fari kal din hannunsa daya ne a waje yana rike da sandar girmansa dake ajiye a kusa da kafarsa, sai dayan dake dafe da gefen zuciyarsa
Da sauri ta cire dubanta a kansa ta juya da wani irin sauri ta bi bayan yan uwanta
Sunna shiga da sauri Ummulkhair ta zube a kasa tana mai dora hannunta saman kanta tana dubansu a rikice ta ce" shin kun fahimci abinda na fahimta? Kun gane cewar akoy wani gagarumin sirin dake damun mahaifinmu wanda da alama mahaifinmu ya shafa wanda nake kyautata zaton idan har ya fito fili mun kade?
Najeeba ta jefar da iPhone dinta saman kujerar dake ajiye ta cire alkyabar jikinta ta jefar ta zauna a kusa da Ummukulsum ta shiga cakuda gashin kanta
Dagowa ta yi da wani irin yannayi ta ce" aya ta kasance a kansa da wuri? Bai fadi haka ba sai da ya ji cewar wannan tsautsayi ya afku da Ummu? Me ke faruwa da mahaifinmu? Wace aya ce wannan ta kasance a kan ubanmu?
Ummukulsum dake share hawaye itama ta budi bakinta a hankali ta ce" sai jake jin tsoron abinda zuciyata ke fada min, sai nake jin tsoron abinda nake tunani
Ummulkhair ta ce" me kike tunani ummu?
Ummu itama ta dora hannunta a kanta ta ce" sai zuciyata ke ce min bayan mahaifiyata mai amsar kudin zina ce mahaifinama ya taba fadawa wata
Da sauri Najeeba ta matso kusanta tana daga hannunta da ihu ihu ta ce" ke ke, yi min shiru, walahi zan tsinka maki mari idan kika fadi cewar Abih ya taba yiwa wata fyade
Ummulkhair ta shiga yarfe hannayenta tana fashewa da kuka ta ce" Najeeba ai ba haka ta fada ba, abinda kike tunani ne kika fada kuma nima abinda nake tunanin kennan innalilahi wa'ina ilaihi raj'une me ke faruwa da mu?
Itama Najeebar baki daya kafafuwanta ne suka gaza daukanta
Tana kokarin zubewa kasa Dayabu ya shigo
Da wani irin sauri ya karaso ya tareta a jikinsa suka kai kasan tare
Da rarafe sauran suka karasa wajensa suka rungume shi sunna kuka baki dayansu
Innalilahi wa'ina ilaihi raj'une, yake maimaitawa hankalinsa a tashe ya shiga fadin" tabas kadara, mumunar kadara ta faru da kanwata, sai nake jin ba wanda ya kaini jin ciwo duda irin yanda aka fada min lamarin cewar ba da son ransa ba, duda na san Allah ya kadarto hakan, sannan har an yanke hukunci zai zama mijinki aman zuciyata ta kasa daina hawaye
Tsoro nake ji , walahi tsoro nake ji
Idan ita ummu ta faru da ita a wajen mutunci wajen da aka isa a tankwasa karfe komai taurinsa ku fa?
Shin wace irin kadara ce ta afkawa mahaifinmu ya aikata mana haka?
Da sauri Najeeba ta dago kanta tana kallonsa
DAYABU da hankalinsa ke tashe ya shiga fadin" ba zan iya kuma zuba maku ido kuna yawo haka ba, du ku fitar da mazan aure a cikin manemanku a yi maku aure ku tare a gidajenku hakan zai saka mani nutsuwa a cikin zuciyata, walahi idan ayar nan ta kuma kasancewa a kan wani a cikinku bana tunanin zan iya yafewa Abih!
Lebunanta ke hadewa da junna sai jimkesu take tana kara budewa
A rikice ta ce" me me ya yi ne wai? Me ya yi?
DAYABI ya sasauta masu rikon jin du sun dago shi suke kallo
Kansa ya sada ya kasa magana hakan ya saka Ummukulsum dora hannunta a kai ta shiga zunduma ihu tana son mikewa ta yi burgima ko zata ji sanyi, cikin muryarta take fadin" shikenan uwa karuwa uba karuwi ko dai ni shegiya ce ban sani ba?
NAJEEBAma dake kuka tana kallonsa ta ce" yaya waye shege a cikinmu?
Ummulkhair kam sai ta kame, gaba daya ta kasa kuma motsa hannayenta tambayar da yan uwanta ke yi take jiran amsarta
Muryarsa ya sanyaya sosai kafin ya furta" UMMUKULSUM, shin zaki iya jurewa, ki jajirce, ki d'auki hak'uri ki yafewa bawan Allahn nan duba da irin abubuwan da suka gabata da shaidar wace abin ya faru a sanadiyarta ? Zaki iya yafe masa har cikin zuciyarki? Ki tuna Allah na yafewa bayinsa masu yafiya ya Ummu."
Kanta dake kife a jikin kafad'ar Najeeba tun daya kama k'afarta yana gunsheken kukan nan ta ji wani irin tausayinsa ya tsirga mata haka kawai sannan wani irin tsigar jikinta ta ringa tashi, bata k'arasa jin tausayinsa ba sai da ta ji kalaman mahaifinsa da kukan mahaifinsa da shi kansa.
Gimbiya ce ta k'ara duk'awa tana kallonta muryarta na rawa ta furta" Ki rufa masa asiri, ki rufawa kanki Ummukulsum, kar ki manta kema mace ce, fitar sirin nan tamkar fitar da sirrinki ne, ki rufe shi dan girman Allah."
Cire dubanta ta yi daga kanta, muryarta na rawa ta furta" Na yafe masa."
Sai kuma ta fashe da kukan da ya saka Najeeba wace jikinta ya d'ume da zafi kanta na sarawa ita ma fashewa da kukan tana k'ara rungumeta, Zahrau kuwa ta zama wata mutun mutumi sai juya kai take baki d'aya ta rasa me take ji.
Hamdallah yayi kafin ya maida dubansa wajen sarki a sanyaye sarki ya ringa sakin ajiyar zuciya, muryarsa a sanyaye ya furta" ina neman alfarma, ina neman alfarmar a bar min ita a nan gidan, ta yi istibra'i a d'aura masu aure, domin na rantse shi zai gyara abinda ya lalata."
Daga Gimbiya har matarsa a tsorace suka kalli sarkin da ya watsar da su yana cike da jin haushinsu, sam tamkar basa wajen tun da ya masu tambaya yayi watsi dasu.
Da baya ta kai zaune tana mai d'ora hannayenta saman kanta a b'oye, kishiyarta kuwa bayan tarin tausayin yarima domin yaron yana da mutunci sosai, sai kuma tarin al'ajabin abinda ke shirin faruwa, auren yarima da matarsa aure aka yi na zobe, yar k'awar gimbiya ta k'ud da k'ud wace ak'idarsu d'aya cewar ba za'a yi masu kishiya bace ya aura, hakan yasa Gimbiyar ke taya ta yak'in maganar kishiya sai gashi a yau abu biyu ya faru da su baki d'aya, wato wanzuwar *KISHIYA* a tsarin da basu ajiyeta ba.
Kansa ya kuma sadawa yarima ya k'ara duk'awa shima yana rok'an hakan.
Ajiyar zuciya ya sauke a sanyaye ya furta" zamu juya gida a jirgin safe in sha Allahu, zan yi kira na sanar da abinda ake ciki."
A haka dole aka tashi, sarki na zaune saida kowa ya tashi sannan ya bi bayan Zahrau dake son shiga d'akin jikinta a mace.
Hannunta ya kamo ya maidota baya
A hankali ya sakata cikin jikinsa ya rungumeta yana buga bayanta kad'an kad'an kafin ya jata suka koma saman kujerar
Sai a lokacin ta samu kuka ya kubce mata cike da tsoro take nuna masa ba zata iya zama ba yan uwanta a wannan gidan da ya gama tsoratata ba.
Sosai yayi anfani da hikima ya ringa rarashinta har ta dawo nutsuwarta ta ringa sauke ajiyar zuciya da kansa ya mata alk'awarin zai nemi alfarmar malan ya bashi y'aya biyu k'annenta su tare da ita su tayata zama kafin a kawo mata Ummu.
Da wannan ya samu ta kwontar da hankalinta kafin ya rakata har d'akin suka ci gaba da gabatar da sallah baki d'ayansu suna godewa Allah da irin wannan ranar.
....................................
Zabura ya yi tsaye sai kuma ya yanke jiki ya fad'i zaune saman kafet d'in hannayensa aje saman kansa muryarsa na rawa ya furta" innalilahi wa'inna ilaihi raj.une, hasbunnalahu wani'imal wakim
aya ta tabbata a kaina ni MUTALAB gashi, abinda na aikata ya kamo ni da wuri haka a kan yarinyata."
Sai ya fashe da kuka yana kallon yanda D'AYABU ya tsurawa sarki ido kamar wanda ya suma a zaune.
Da sauri Anmy dake kukan itama ta kaleshi a firgice jin zai tona asirin da suke lullub'ewa kansu da k'afarsu, zai tonawa kansa asiri a cikin irin rud'anin nan da suke ciki zai k'ara masu wani.
Duban da Ummu ke masa ne ya saka shi k'ara sada kansa yana hawaye
Ummulkhair ta kalli Najeeba wace ita ma ita take kallo kafin Najeeba ta bud'a bakinta a hankalì tana kallon Ummulkhair tana dan yatsine fuskarta tace" eyah, eyah, yau kin yarda da ayar tambayar da na d'ora a kan maganar da Abih kan fad'a wani sa'in?"
Maida dubanta tayi wajen Abih a sanyaye ta furta" *ABIH, WACE AYA CE TA TABBATA A KANKA?*
komawa sarki yayi ya jinginar da bayansa jikin kujera yana lumshe idannuwansa, ta faru kuma ta k'are, rikicin cikin gidansu zai k'ara kunnuwa a yanzu, ya tabbata wani tashin hankalin ne zai k'ara kunno kansa hakan ya saka ya idasa had'e fuskarsa da dukan wani abu wai shi annuri ya lumshe idanuwansa a lokacin da Anmy a firgice ta kallesu tace "...
Happy juma'at🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
27
A firgice, a rikice, a tsawace Anmy ta ce" yaya muna cikin wannan tashin hankalin zaki yi mana wata tambaya kina mai kokarin tirke mun tamkar kece uwarmu mu kuwa y'ayanki?
Baki daya yan matan sai abin ya basu mamaki, yannayin Anmy din ya saka jikinsu ya yi sanyi harma du suka zuba mata ido da wani irin duba na mamaki
Anmy ta kawar da kanta tana jan hancinta tana kara rintse idannuwanta da sukai mata luhu luhu ranta hade ta ce" ku tashi ku je dakin ku
Jiki sanyaye du suka mimike, Najeeba ta kara waigowa ta kalli mahaifinta ta ga kansa a kasa sannan hannayensa sai rawa suke, ta kai dubanta wajen yayansu ta ga shima kan nasa a sade shi kuwa kuka ne yake a hankali ta saci kallon mai martaba ta ga ya yi wata kwonciya a jikin kujerar ya daga kansa sama idannuwansa lumshe rawanin dake kansa ya kara fadi sakamakon yannayin kwonciyar nasa, shigar alkyaba ne a jikinsa mai ruwan duhu wace ke da igiya wajen wuyanta, fari kal din hannunsa daya ne a waje yana rike da sandar girmansa dake ajiye a kusa da kafarsa, sai dayan dake dafe da gefen zuciyarsa
Da sauri ta cire dubanta a kansa ta juya da wani irin sauri ta bi bayan yan uwanta
Sunna shiga da sauri Ummulkhair ta zube a kasa tana mai dora hannunta saman kanta tana dubansu a rikice ta ce" shin kun fahimci abinda na fahimta? Kun gane cewar akoy wani gagarumin sirin dake damun mahaifinmu wanda da alama mahaifinmu ya shafa wanda nake kyautata zaton idan har ya fito fili mun kade?
Najeeba ta jefar da iPhone dinta saman kujerar dake ajiye ta cire alkyabar jikinta ta jefar ta zauna a kusa da Ummukulsum ta shiga cakuda gashin kanta
Dagowa ta yi da wani irin yannayi ta ce" aya ta kasance a kansa da wuri? Bai fadi haka ba sai da ya ji cewar wannan tsautsayi ya afku da Ummu? Me ke faruwa da mahaifinmu? Wace aya ce wannan ta kasance a kan ubanmu?
Ummukulsum dake share hawaye itama ta budi bakinta a hankali ta ce" sai jake jin tsoron abinda zuciyata ke fada min, sai nake jin tsoron abinda nake tunani
Ummulkhair ta ce" me kike tunani ummu?
Ummu itama ta dora hannunta a kanta ta ce" sai zuciyata ke ce min bayan mahaifiyata mai amsar kudin zina ce mahaifinama ya taba fadawa wata
Da sauri Najeeba ta matso kusanta tana daga hannunta da ihu ihu ta ce" ke ke, yi min shiru, walahi zan tsinka maki mari idan kika fadi cewar Abih ya taba yiwa wata fyade
Ummulkhair ta shiga yarfe hannayenta tana fashewa da kuka ta ce" Najeeba ai ba haka ta fada ba, abinda kike tunani ne kika fada kuma nima abinda nake tunanin kennan innalilahi wa'ina ilaihi raj'une me ke faruwa da mu?
Itama Najeebar baki daya kafafuwanta ne suka gaza daukanta
Tana kokarin zubewa kasa Dayabu ya shigo
Da wani irin sauri ya karaso ya tareta a jikinsa suka kai kasan tare
Da rarafe sauran suka karasa wajensa suka rungume shi sunna kuka baki dayansu
Innalilahi wa'ina ilaihi raj'une, yake maimaitawa hankalinsa a tashe ya shiga fadin" tabas kadara, mumunar kadara ta faru da kanwata, sai nake jin ba wanda ya kaini jin ciwo duda irin yanda aka fada min lamarin cewar ba da son ransa ba, duda na san Allah ya kadarto hakan, sannan har an yanke hukunci zai zama mijinki aman zuciyata ta kasa daina hawaye
Tsoro nake ji , walahi tsoro nake ji
Idan ita ummu ta faru da ita a wajen mutunci wajen da aka isa a tankwasa karfe komai taurinsa ku fa?
Shin wace irin kadara ce ta afkawa mahaifinmu ya aikata mana haka?
Da sauri Najeeba ta dago kanta tana kallonsa
DAYABU da hankalinsa ke tashe ya shiga fadin" ba zan iya kuma zuba maku ido kuna yawo haka ba, du ku fitar da mazan aure a cikin manemanku a yi maku aure ku tare a gidajenku hakan zai saka mani nutsuwa a cikin zuciyata, walahi idan ayar nan ta kuma kasancewa a kan wani a cikinku bana tunanin zan iya yafewa Abih!
Lebunanta ke hadewa da junna sai jimkesu take tana kara budewa
A rikice ta ce" me me ya yi ne wai? Me ya yi?
DAYABI ya sasauta masu rikon jin du sun dago shi suke kallo
Kansa ya sada ya kasa magana hakan ya saka Ummukulsum dora hannunta a kai ta shiga zunduma ihu tana son mikewa ta yi burgima ko zata ji sanyi, cikin muryarta take fadin" shikenan uwa karuwa uba karuwi ko dai ni shegiya ce ban sani ba?
NAJEEBAma dake kuka tana kallonsa ta ce" yaya waye shege a cikinmu?
Ummulkhair kam sai ta kame, gaba daya ta kasa kuma motsa hannayenta tambayar da yan uwanta ke yi take jiran amsarta