Sashe 39
Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mardiya kuwa na zaune gefe guda itama ita daya, ga yarinyarta sai tsala ihun kuka take tana so ta saketa aman ta ki sakin nata
Ta sha wani rantsatsen lesh sai kyalkyali yake yarinyartama ta shiryata cikin wata riga doguwa mai shegen kyau, kyanta zai shaida maka kudinta
Sai ihu take tana kallon Najeeba, dan kaf a cikin yayun nata babu wanda ta shaku da shi irin najeeba dan goyata take ta yi ta mata doki , sannan du idan zata shigo sai ta shigo mata da tsarabar sweet
Wani uban tsaki ta ja ta dangwarar da yarinyar saman cinyarta ta dale keyarta ta ce" zan ci ubanki Nusaiba ki zauna min yau ga jaraba ba inda zaki je
Da sauro Najeeba ya kama bakinsa yana kallon yayansa, a fili ya ce" yaya Mardiya na zagin kanwata bayan ka hanamu zagi walahi
Duban Mardiyar ya yi ya ce" walahi ki bar zagar min kanwa
Mardiya da a cike take irin yanda Abih ya tasota ya tiso keyarta ya kawota a zaunar da su kan laifin da bata san me ta yi ta harareshi ta ce" sai ka hanani zagin nata shege mai katon kai
Da sauri ummulkhair ta dubeta ta ce" aman me yasa kika cika son neman fitina ne ke?
Anmy ta yi mata wani kakausan kallon da ya sakata sada kanta aman kasan zuciyarta a bace yake
Ai kuwa Bilkissu da ba kallon Anmy take ba ta ce" to fa, an tabota
Ranta ya kara baci ta ce" ke bilkisu an taboni ni ga mahaukaciya ko? Yan iska kawai da iyayenku kuke kuma du irin rashin hankalina na fi su domin ni na fi uwar kowa cikinku jimawa da ubanku
Da sauri Anmy ta dago kanta a karo na biyu ta sauke dubanta a kanta
Zahrau ta sada kanta tana jin hawaye na son zubo mata
Ummukulsum ta ce" me yasa idan kin tashi masifarki kike sako iyayenmu? A kan me zaki ringa koya mana muguwar tabi'a ne? Kin dai san uwa ba fin uwa ta yi ba ko? Kuma yai da gobe sai Allah kin san watarana zaki ji kunya? Kar ki manta a damagaram muke idan wannan bai san sirrinki ba wani ya sani balema a tafin hannuna sirrin naki yake
Rufe min baki shashasha, siriin nawa da kika sani meye? A ciki akoy cikin shege ne? Ko akoy yawon ta zubar ne?
Da sauri Dayabu ya dubeta, da yake mahaifiyar Ummukulsum bata zama waje dayan nan ba kennan gori ne ta mata na hakan
NAJEEBA ta kara sada kanta tana jin zuciyarta na yi mata tukuki, sam bata so ta furta ko A a wajen nan domin ba a ko'ina take son raba hali ba
Ummukulsum ta ce" Alhamdulilah, haka ne, na sani na kuma yarda uwata haka take, ke fa ubanki kafin ya zama malami meye bai yi? Ta fada muryarta a dan dage
Fuskarta da Anmy ta tsinke da mari ne ya saka du suka firgice sunna kallonta
Sai a lokacin Anmy ta buda bakinta a hankali ba a tashe ba ta ce" ashe lalacewar tarbiyar naku har ta kai ina zaune a waje kuna tozarta kanku ta hanyar sakarwa harshenku linzami?
Kun san ikon harshe a tare da mutun kuwa? Harshe kan saka bawa ya zama sakarai a cikin al'uma,
Idan baka iya rike harshenka ba zai fada maka maganar da zata saka ka da na sani a cikin duniya baki daya!
Ku shikenan a wajen da ya dace a ji muryarku da wajen da bai dace bama sai ku saki baki ku furta kalma daya?
Ummu a gabana kike rashin kunyar nan? Ummu ni zaki tozartawa iyali? Wuyanki ya yi kwarin da ya isa yankan da zai jazawa mahaifiyarki zagi daga bakin mai nemanki da fitina?
Abih da kansa ke sade yana cike da mamakin rayuwa irin yanda yau shine mace, matarsa take budar baki tana zagin y'ayansa a gabansa aman ya kasa furta mata komai
Sunnayen Allah ya ringa kira ido rufe domin baya so rashin kunyar Mardiya ya kaishi wajen da zai kuma aikata kaifin rabuwa da mace, irin yanda ya rabu da matansa ya yiwa kansa alkawarin ita wannan ta birne shi ko ya birneta, sai dai kash ya yo hakan a lokacin da yake aure da matar da bata san darajar kanta ba, ya yi zama da mata kala daban daban, har yar bariki da ustaziya, bai tashi daukan wannan niyar ba sai a kan wace zata tarwatsa masa nutsuwar zuciya
Tun da Anmy ta fara magana sauranma suka kara sada kansu
Ummukulsum kuwa sai ta fashe da kukan nadamar sakin bakinta da ta yi har haka ta faru
Kanta ta dora a gefen kafadar Najeeba tana kukan inda Najeeba ta rintse idannuwanta tana jin kukan yar uwar tata har cikin zuciyarta
Bata taba jin tsanar matar abih irin na yau ba, tabas bata zo wajen nan dan furta kalma daya ba aman ta rantse a yau b sai gobae ba sai ta tardata du gidan ubanda ta shiga ta ci uwarta!
Sanarwar shigowarsa ya saka Anmy sada kanta tana jin kamar ta fashe da kukan itama, kai ina, dole ne ya bara mata yaren nan dan walahi ba zata yarda ya kara tafia da su ba ya kaisu tarbiyarsu na kara shiga hatsari! A haka zaa aurar da mace a kaita gidan miji a kai me? Ta tabata irin yanda ummu ta kasa dane bacin ranta ta nuna shirme ko miji ya fada zata fada ne!
Ya kai minti ashirin kafin yake karasa shigowa cikin shigarsa ta kamala
Da hannayensa ya dakatar da amintacensa kan ya tsaya a kofa domin shara'ar ta cikin gidansu ce
Direct wajen kujerar ya karasa yana tsaye yana bin kowa da kallo
Yarinyar dake sheka kuka kamar zata sike ya bi da kallo, mahaifiyarta da ta riketa gam ya kuma bi da kallo kafin ya maida dubansa inda yarinyar ke nunawa tana son a saketa ta karasa wajen Najeeba aman an hana
Murmushi ya yi a kasan zuciyarsa domin nan take ya gama fahimtar matsalarsu baki daya sai dai kamar yanda ya kasance sai ya saurara to fa zai sauraran ne dole
A hankali murya a tausashe ya ce" *KI SAKE TA TA JE WAJEN YAN UWANTA*
A hankali ya yi maganar, sai dai kasancewarsa mai cike da kwarjini da bulaliyar dukan magana ya sakata tunkudo yarinyar a biye wanda ita a boye ta yi aman du an gani
Yarinyar kuwa da gudu ta karasa jikin Najeeba
Tana zuwa ta ringa dora kanta a jikinta tana rukunkumeta, sai dai Najeebar bata riketa a jikinta ba itama
Zuciyarta na mata tsale, so take ta riketa ta rungumeta aman ba hali a hankali ta saci kallon yayansu wanda komai a kan idannuwan sarki, shima duban nasa ya kai wajen DAYABU sai ya ga idannuwansa a rintse suke, ya gama hawa stage din da ba zai iya furta kalma daya ba tare da ya yi maganin matar nan ba!
Murmushi ya yi ya idasa gani kan matsalar kafin a hankali ya kai zaune
Sai da ya zauna ya gyara zamansa sannan ya yi sakama a hankali
Baki daya suka dago kawunnansu daga sadawar da suka yi,
Dubansa ya kara kaiwa wajen yarinyar dake ta wawuwar Najeeba dan bata yi shirun ba so take ta kulata ta yi mata wasa ta rarasheta aman ta ki yi mata hakan
A tausashe ya ce" Abu hauraira Allah ya yarda da shi yana cewa" ka so masoyinka daidai gwargwado domin zai iya zamowa makiyinka, haka kuma ka ki makiyinka daidai gwargwado domin zai iya zama masoyinka wata rana
Numfasawa ya yi ya shiga binsu da kallo tun daga kan Abih har zuwa mahaifiyarsa
A hankali ya kuma furta" *ME KE DAMUN AHALINA NE? ME KE DAMUN SHUGABAN CIKIN GIDAN BIYU NE?* *YAYA AKA YI YA YARDA KIYAYA TA YI ZAFI HAKA A CIKIN GIDANSA BAYAN YANA DA IKON KATSETA KODA KUWA TA HANYAR KAWAR DA MAI HADASATA NE A WAJE?*🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
23
Baki daya wajen ne ya dauki shiru , kawunnansu du a sade a kasa haka kuma NUSAIBA bata daina kukan da take ba
Sarki ya kuma buda bakinsa ya ce" mazon Allah tsira da amincin Allah su tabata a gareshi yana son yin alfahari da mu a gobe kiyama
Aman ta yaya?
Shirun dai ne ya kara tabata a wajen hakan ya saka ya dago yar yatsarsa ya yi nuni da Zahrau a tausashen dai ya furta" Bismillah
Zahrau ta kara sada kanta a hankali ta ce" Allah ya kara girma, ya umarcemu da mu hayayafa dan gobe ya yi alfahari da mu
Kansa ya gyada a hankali kasa kasa ya furta" barakalahu fihk,
Kansa tsaye ya nuna Najeeba dake dan janye Nusaiba daga jikinta ya furta" meye ilar gaba a musulunci?
Dungurar da Anmy ta yi mata ya sakata dagowa domin ta so ta yi kamar bata gane da it ake ba , sai dai ba hali domin a irin yanda Anmy kanta ta nutsu a gabansa abin sai wanda ya gani,
A sanyaye ta furta" *Allah yana yiwa mutane afuwa, aman banda masu gaba da junna*
Dubansa ya maida wajen DAYABU da kansa ke kasa shima kafin ya ce" shin me ya dace shugaba ya koyar tsakanin hakuri da rashinsa?
Yaya DAYABU ya dago yana dubansa kafin ya furta" Hakuri, Hakuri shine ya dace da kowani bawa, mai hakuri zai ci riba
Sarki ya gyada kansa ya furta" Mai hakuri zai kai ga ci
Dubansa ya maida kan iyayensa daga Abih har Anmy
A sanyaye ya furta" shugaba, ya dace ya kasance mai matsanancin hakuri, ya ringa shanye abinda da yawa ba zasu iya shanyewa ba
Shugaba koda na wasan yara ne, ya dace ya zama mai yanke hukunci cikin aminci, da kawar da kai
Dubansa ya maida wajen Mardiya, sunna hada ido ta yi gagawar sada kanta, a hankali ya furta" ka karfafa zumunci, ka yada zumunci, kar ka zamo wanda zai yi silar yanke zumunci
Shiru ya kuma yi kafin ya furta" mai magana bismillah
Ta sha wani rantsatsen lesh sai kyalkyali yake yarinyartama ta shiryata cikin wata riga doguwa mai shegen kyau, kyanta zai shaida maka kudinta
Sai ihu take tana kallon Najeeba, dan kaf a cikin yayun nata babu wanda ta shaku da shi irin najeeba dan goyata take ta yi ta mata doki , sannan du idan zata shigo sai ta shigo mata da tsarabar sweet
Wani uban tsaki ta ja ta dangwarar da yarinyar saman cinyarta ta dale keyarta ta ce" zan ci ubanki Nusaiba ki zauna min yau ga jaraba ba inda zaki je
Da sauro Najeeba ya kama bakinsa yana kallon yayansa, a fili ya ce" yaya Mardiya na zagin kanwata bayan ka hanamu zagi walahi
Duban Mardiyar ya yi ya ce" walahi ki bar zagar min kanwa
Mardiya da a cike take irin yanda Abih ya tasota ya tiso keyarta ya kawota a zaunar da su kan laifin da bata san me ta yi ta harareshi ta ce" sai ka hanani zagin nata shege mai katon kai
Da sauri ummulkhair ta dubeta ta ce" aman me yasa kika cika son neman fitina ne ke?
Anmy ta yi mata wani kakausan kallon da ya sakata sada kanta aman kasan zuciyarta a bace yake
Ai kuwa Bilkissu da ba kallon Anmy take ba ta ce" to fa, an tabota
Ranta ya kara baci ta ce" ke bilkisu an taboni ni ga mahaukaciya ko? Yan iska kawai da iyayenku kuke kuma du irin rashin hankalina na fi su domin ni na fi uwar kowa cikinku jimawa da ubanku
Da sauri Anmy ta dago kanta a karo na biyu ta sauke dubanta a kanta
Zahrau ta sada kanta tana jin hawaye na son zubo mata
Ummukulsum ta ce" me yasa idan kin tashi masifarki kike sako iyayenmu? A kan me zaki ringa koya mana muguwar tabi'a ne? Kin dai san uwa ba fin uwa ta yi ba ko? Kuma yai da gobe sai Allah kin san watarana zaki ji kunya? Kar ki manta a damagaram muke idan wannan bai san sirrinki ba wani ya sani balema a tafin hannuna sirrin naki yake
Rufe min baki shashasha, siriin nawa da kika sani meye? A ciki akoy cikin shege ne? Ko akoy yawon ta zubar ne?
Da sauri Dayabu ya dubeta, da yake mahaifiyar Ummukulsum bata zama waje dayan nan ba kennan gori ne ta mata na hakan
NAJEEBA ta kara sada kanta tana jin zuciyarta na yi mata tukuki, sam bata so ta furta ko A a wajen nan domin ba a ko'ina take son raba hali ba
Ummukulsum ta ce" Alhamdulilah, haka ne, na sani na kuma yarda uwata haka take, ke fa ubanki kafin ya zama malami meye bai yi? Ta fada muryarta a dan dage
Fuskarta da Anmy ta tsinke da mari ne ya saka du suka firgice sunna kallonta
Sai a lokacin Anmy ta buda bakinta a hankali ba a tashe ba ta ce" ashe lalacewar tarbiyar naku har ta kai ina zaune a waje kuna tozarta kanku ta hanyar sakarwa harshenku linzami?
Kun san ikon harshe a tare da mutun kuwa? Harshe kan saka bawa ya zama sakarai a cikin al'uma,
Idan baka iya rike harshenka ba zai fada maka maganar da zata saka ka da na sani a cikin duniya baki daya!
Ku shikenan a wajen da ya dace a ji muryarku da wajen da bai dace bama sai ku saki baki ku furta kalma daya?
Ummu a gabana kike rashin kunyar nan? Ummu ni zaki tozartawa iyali? Wuyanki ya yi kwarin da ya isa yankan da zai jazawa mahaifiyarki zagi daga bakin mai nemanki da fitina?
Abih da kansa ke sade yana cike da mamakin rayuwa irin yanda yau shine mace, matarsa take budar baki tana zagin y'ayansa a gabansa aman ya kasa furta mata komai
Sunnayen Allah ya ringa kira ido rufe domin baya so rashin kunyar Mardiya ya kaishi wajen da zai kuma aikata kaifin rabuwa da mace, irin yanda ya rabu da matansa ya yiwa kansa alkawarin ita wannan ta birne shi ko ya birneta, sai dai kash ya yo hakan a lokacin da yake aure da matar da bata san darajar kanta ba, ya yi zama da mata kala daban daban, har yar bariki da ustaziya, bai tashi daukan wannan niyar ba sai a kan wace zata tarwatsa masa nutsuwar zuciya
Tun da Anmy ta fara magana sauranma suka kara sada kansu
Ummukulsum kuwa sai ta fashe da kukan nadamar sakin bakinta da ta yi har haka ta faru
Kanta ta dora a gefen kafadar Najeeba tana kukan inda Najeeba ta rintse idannuwanta tana jin kukan yar uwar tata har cikin zuciyarta
Bata taba jin tsanar matar abih irin na yau ba, tabas bata zo wajen nan dan furta kalma daya ba aman ta rantse a yau b sai gobae ba sai ta tardata du gidan ubanda ta shiga ta ci uwarta!
Sanarwar shigowarsa ya saka Anmy sada kanta tana jin kamar ta fashe da kukan itama, kai ina, dole ne ya bara mata yaren nan dan walahi ba zata yarda ya kara tafia da su ba ya kaisu tarbiyarsu na kara shiga hatsari! A haka zaa aurar da mace a kaita gidan miji a kai me? Ta tabata irin yanda ummu ta kasa dane bacin ranta ta nuna shirme ko miji ya fada zata fada ne!
Ya kai minti ashirin kafin yake karasa shigowa cikin shigarsa ta kamala
Da hannayensa ya dakatar da amintacensa kan ya tsaya a kofa domin shara'ar ta cikin gidansu ce
Direct wajen kujerar ya karasa yana tsaye yana bin kowa da kallo
Yarinyar dake sheka kuka kamar zata sike ya bi da kallo, mahaifiyarta da ta riketa gam ya kuma bi da kallo kafin ya maida dubansa inda yarinyar ke nunawa tana son a saketa ta karasa wajen Najeeba aman an hana
Murmushi ya yi a kasan zuciyarsa domin nan take ya gama fahimtar matsalarsu baki daya sai dai kamar yanda ya kasance sai ya saurara to fa zai sauraran ne dole
A hankali murya a tausashe ya ce" *KI SAKE TA TA JE WAJEN YAN UWANTA*
A hankali ya yi maganar, sai dai kasancewarsa mai cike da kwarjini da bulaliyar dukan magana ya sakata tunkudo yarinyar a biye wanda ita a boye ta yi aman du an gani
Yarinyar kuwa da gudu ta karasa jikin Najeeba
Tana zuwa ta ringa dora kanta a jikinta tana rukunkumeta, sai dai Najeebar bata riketa a jikinta ba itama
Zuciyarta na mata tsale, so take ta riketa ta rungumeta aman ba hali a hankali ta saci kallon yayansu wanda komai a kan idannuwan sarki, shima duban nasa ya kai wajen DAYABU sai ya ga idannuwansa a rintse suke, ya gama hawa stage din da ba zai iya furta kalma daya ba tare da ya yi maganin matar nan ba!
Murmushi ya yi ya idasa gani kan matsalar kafin a hankali ya kai zaune
Sai da ya zauna ya gyara zamansa sannan ya yi sakama a hankali
Baki daya suka dago kawunnansu daga sadawar da suka yi,
Dubansa ya kara kaiwa wajen yarinyar dake ta wawuwar Najeeba dan bata yi shirun ba so take ta kulata ta yi mata wasa ta rarasheta aman ta ki yi mata hakan
A tausashe ya ce" Abu hauraira Allah ya yarda da shi yana cewa" ka so masoyinka daidai gwargwado domin zai iya zamowa makiyinka, haka kuma ka ki makiyinka daidai gwargwado domin zai iya zama masoyinka wata rana
Numfasawa ya yi ya shiga binsu da kallo tun daga kan Abih har zuwa mahaifiyarsa
A hankali ya kuma furta" *ME KE DAMUN AHALINA NE? ME KE DAMUN SHUGABAN CIKIN GIDAN BIYU NE?* *YAYA AKA YI YA YARDA KIYAYA TA YI ZAFI HAKA A CIKIN GIDANSA BAYAN YANA DA IKON KATSETA KODA KUWA TA HANYAR KAWAR DA MAI HADASATA NE A WAJE?*🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*Na*
*SAJIDA*
💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝
☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️
https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/
_Bismillahir rahamanir rahim_
23
Baki daya wajen ne ya dauki shiru , kawunnansu du a sade a kasa haka kuma NUSAIBA bata daina kukan da take ba
Sarki ya kuma buda bakinsa ya ce" mazon Allah tsira da amincin Allah su tabata a gareshi yana son yin alfahari da mu a gobe kiyama
Aman ta yaya?
Shirun dai ne ya kara tabata a wajen hakan ya saka ya dago yar yatsarsa ya yi nuni da Zahrau a tausashen dai ya furta" Bismillah
Zahrau ta kara sada kanta a hankali ta ce" Allah ya kara girma, ya umarcemu da mu hayayafa dan gobe ya yi alfahari da mu
Kansa ya gyada a hankali kasa kasa ya furta" barakalahu fihk,
Kansa tsaye ya nuna Najeeba dake dan janye Nusaiba daga jikinta ya furta" meye ilar gaba a musulunci?
Dungurar da Anmy ta yi mata ya sakata dagowa domin ta so ta yi kamar bata gane da it ake ba , sai dai ba hali domin a irin yanda Anmy kanta ta nutsu a gabansa abin sai wanda ya gani,
A sanyaye ta furta" *Allah yana yiwa mutane afuwa, aman banda masu gaba da junna*
Dubansa ya maida wajen DAYABU da kansa ke kasa shima kafin ya ce" shin me ya dace shugaba ya koyar tsakanin hakuri da rashinsa?
Yaya DAYABU ya dago yana dubansa kafin ya furta" Hakuri, Hakuri shine ya dace da kowani bawa, mai hakuri zai ci riba
Sarki ya gyada kansa ya furta" Mai hakuri zai kai ga ci
Dubansa ya maida kan iyayensa daga Abih har Anmy
A sanyaye ya furta" shugaba, ya dace ya kasance mai matsanancin hakuri, ya ringa shanye abinda da yawa ba zasu iya shanyewa ba
Shugaba koda na wasan yara ne, ya dace ya zama mai yanke hukunci cikin aminci, da kawar da kai
Dubansa ya maida wajen Mardiya, sunna hada ido ta yi gagawar sada kanta, a hankali ya furta" ka karfafa zumunci, ka yada zumunci, kar ka zamo wanda zai yi silar yanke zumunci
Shiru ya kuma yi kafin ya furta" mai magana bismillah