← Book details Mage Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 62 OF 138

Sashe 62

Mage Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bata kula irin rikicewarsu ba ta bud'a baya ba gardama ta shiga ta kwontar da kanta jikin kujerar
*da ban je ba, da ban ga wulak'anci ba, da ban ba da hanya ba, da bai rungumi jikina ba, ni Najeeba, ni ba yar iska bace* wannan abubuwan take fad'awa kanta a cikin zuciyarta har suka k'araso fada.

Su sun fita shiga damuwa domin sun san cewa an san basa tare da ita gashi sun d'ora lokaci sosai a kan lokacin dawowarta.

Tun daga yannayin Amintace suka k'ara sarewa har suka gama parking da motar ta bale ta fita ta nufi b'angaren Anmy su kuwa sun kasa fitowa daga cikin motar domin tsaye yake hakimce hannayensa rungume a k'irjinsa da yanayi irin na zaku ci ubankun nan yana jiran su gama k'umbiya k'umbiya su fito su tarkata su yo b'angaren SULTAN.

*Masha Allah*
[2/12, 6:58 PM] Ummu Sadeeq: 🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻

*Na*

*SAJIDA*

💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝

☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_

33

Tana shiga ta tarar da Anmy zaune tana rike da wayarta

DAYABU na tsaye da wayarsa shima yana dokawa haka Abih na zaune aman kansa a kasa

Tana shigowa Anmy ta fara ganninta hakan ya saka ta mike da sauri tana fadin" NAJEEBA, daga ina kike? Waye ya daga wayana yake ce min na shafa maki lafia na bar kiran ki? Ina wayarki take? Me ya same ki?

Dayabu ya juyi da sauri yana kallon yanda ta yi wani irin turus sannan kukan da take ga kuma irin yanda jikinta ke bari gabansa ne ya fadi hakan ya saka da wani irin sauri ya karaso ya kamo hannayenta ya yi ciki da ita

Sai da suka shige daki ya zaunar da ita har jikinsa na rawa ya ce" daga ina kike? Kukan me kike?

Anmy da ta biyo bayansu ji take kafafuwanta sai bati suke kamar zasu rabu da gangar jikinta dan tsoro da fargaba

A kidime ta karasa shigowa tana fadin" wani ya maki wani abu? Wani abu ya same ki?

Fashewa ta yi da kuka tana zumburo bakinta ta ce" Anmy, wayata ce ta bata

Ba anmy ba, shi kansa sai da ya ji ya sauke ajiyar zuciya duda ba wani yarda ya yi da maganarta ba

Abih ne ya shigo ya zauna bakin gadon yana kallonta

A sanyaye ya dubi Anmy ya ce" Bilkissu, mu je

Anmy sai da ta kamo hannun Najeeba ta rike tana kallonta a sanyaye ta ce" wannan shine alfarma ta fari da zan nema a wajenki nurul khalb

Najeeba ta kurawa fuskar Anmy ido aman ta kasa tambayar menene har suka fita

Sunna fita Anmy ta ringa sintiri ta kasa zama, dama sun yanke sai dai Dayabu ya tarbeta da maganar dan shi kawai zai iya fatatakarta kuma ta saurareshi

Cikin daki

Na san karya kike da maganar dan an sace wayarki kike kuka, ki fada min abinda ya saka ki kuka tun raina bai baci ba

DAYABU ya fada yana kuma mai jin tsoron abinda zata ce ya sakata yin kukan

Sai da ta rintse idannuwanta wasu hawayen suka kara zubowa daga gurbin idannuwanta, cike da jin kunyar abinda zata fada ta shiga kwatanta masa abinda ta aikata wanda ta tabata sai ya babala mata mari aman kuma da ta rike ita daya ta yi ta jin haushi gwara ta fada masa ya wanwanka mata mari ko zai huce

Da mamaki yake kallonta kafin ya girgiza kansa a sanyaye ya ce " Najeeba, kin san irin darajar da Allah ya yi maki har kike aikata halaya irin na wasu sakakun mata? Najeeba kin kuwa san irin daukakar da Allah ya maki har zaki je ki zubda kanki haka? Najeeba kin kuwa san irin matsayin da Allah ya maki har zaki yarda wani sakarai ya rungumi jikin ki? Yaya aka yi kika kasance mai saurin sakarwa maza fuska bayan ke din kadara ce da ta fi lu'u lu'u daraja?
Najeeba nan da kwana goma idan Allah ya yarda za'a zafa fatiyar daurin aurenki da mutun mafi daraja da mutunci, mai girman mulkin da Allah ya nada tun a kannanun shekaru, mai zamani mai takawa da Alfarmar Annabi, mai watsa taron yan daba mai rikita taron tsageru, Najeeba zaki kasance daya daga cikin mata masu girman daraja wa'inda idan sun zo ficewa ake sada kai ba'a hada ido da su tsabar yanda Allah ya daukaka su ya darajanta su ya fitar da tarmamuwarsu ko da rana take kyali? Najeeba zaki kasance hakima, gimbiya, wace zata zama daya daga cikin wa'inda ko sarakai na jinjina mata kasancewarta matar daya kwalin kwal din sarkin da ya kafa tarihi, Najeeba yaya zaki yarda ki je wani sakaran da ko baran gidan nan ya fi shi mukami a damagaram ya kai hannunsa jikin ki?
*NAJEEBA, ZAKI KASANCE DAYA DAGA CIKIN MATAN MAI DAMAGARAM NAN DA KWANA GOMA KACAL* kike faman saka mu a uku?

Tun daga wannan kalmar kunnayenta suka dode ta daina fahimtar abinda yake fada har sai da ya dasa aya ya ga ta kurawa bakinsa ido kamar wace ta suma a zaune

Hannunsa ya kai wajen kuncinta dan gannin yana furya sunnanta a sanyaye ta kasa amsa shi ya shiga dan taping a hankali ta ce" Najeeba kina ji na kuwa?

Sai a lokacin ta yi wani firgigita ta farka daga summan zaunen da ta yi kafin ta kurawa fuskarsa ido a karo na biyu

Wani irin hantsilowa ta yi daga saman bed din ta fadi kasa har tana take doguwar rigar dake jikinta ta kuma dagowa

Hannayenta duka biyu ta dora saman kanta kafin ta takarkare ta kwala wani firgitacen ihun da ya saka Dayabu saurin kai hannayensa wajen kunnensa ya dode lokaci daya kuma yana nufarta dan rufe bakinta daga wannan ihu da ta saka daya kwal ta ja shi da wani irin jan da ake yi kamar wace ke kiran sallah...

Happy juma'at jama'atul musulmi😲🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻
*MAGE*
_(Mai kwanciyar d'aukar rai)_
🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻🧕🏻

*Na*

*SAJIDA*

💫✨ *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*🌟
_(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_🤝

☆ *[ T.M.N.A]* ☆ 📖🖊️

https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/

_Bismillahir rahamanir rahim_

34

Hannayensa dode da kunnayensa ya diro ya karasa inda take ihun nan
Yana zuwa ya saki kunnensa ya damke bakinta da hannunsa sannan ya saka dayan hannun nasa ya riketa da kyau

Sikewa ta yi, lokaci daya numfashinta ya dauke ta tafi luuu a jikinsa

Ido ya zaro cike da tsoro da mamakin suma ta yi?
Lalle ya dauki abin da wasa ashe har ya kai cen?

Jikinsa na bari ya samu ya kaita saman gadon ya shinfideta sannan ya mike ya karasa wajen kofar dakin

A hankali ya bude hakan ya saka Anmy saurin juyowa a lokacin da Abih ya rike hannayenta yana lalabata cewar kar ta shiga ta bari har su fito

Ummu da Ummulkhair dake tsaye jikin kofar ne suka kutsa kawunansu cikin dakin hakan ya saka ya basu damar shiga sannan ya maida kofar da sauri ya datse dan ya ga Anmy ta zaburo ta nufo wajen

Dakatawa ta yi kusa da kofar hankalinta tashe ta kalli Abih, a sanyaye ta ce" me ya sa ya hana min shiga? Baka jin shirun ya yi yawa ko wani abu ne ya sameta?

Abih ya kara kamo hannunta suka koma falo suka zauna, a sanyaye ya ce" mu yi jira, idan yana irin wannan hali da kannensa nakan basu dama, idan na saki mace na dauko wata haka muke shiga da su du su rikice, shi ke rufe kofa daga shi sai su, ban san ta yanda yake lalaba su ba, in sha Allahu zai lalabata (Ya Allah, du wani yaya da ya dauki girma ya kasancewa kannensa tamkar bango, wajen da suke kai kukansu ya share masu, wajen da sun san uba ne a gare su, Allah ka dafa masa, ka masa albarka, ka kare shi, Yayana JAMILU Allah ya kara daukaka baban yaya👏👏👏)

........................................

Cike da tashin hankali Ummulkhair ta yi kanta, ita kuwa Ummukulsum ta yi bayi da gudu dan dibo ruwa

A rikice Ummulkhair ta ce" yaya, summa fa ta yi? Innalilahi wa'ina ilaihi raj'une daga fada mata ta summa yaya zamu yi da ita ta nutsu?

DAYABU ya sauke ajiyar zuciya ya ce" Ummulkhair, kar ki yi kuka, kar mu saki ta ga rauni a tatare da mu idan ba haka ba na rantse zata botsare mana ne ya kasance mu dake son tirsasata ta amince da maganar nan mu zamu dawo mu goya mata bayan bata so,abinda bana fata sam, kun dai san wacece Najeeba, tana da karfi a cikin zukatanmu, rigimarta ta fi ta NUSAIBA girma dan haka na roke ku kar na ga wace ta wani zubar da hawaye

UMMUKULSUM ta share hawayenta ta shiga tofa adu'a a cikin ruwan sannan ta mika masa ta jingina da jikin gadon a sanyaye ta ce" eyah, Najeeba ta cika daukan abu da zafi, in ba wannan ba na zata zata kama ihun murna ne, meye a cikin auren Mai Damagaram? Ka ga kamar kaza yanzu ta zama daga abu ya dan daga mata hankali sai kawai ta summe

Zuwa ya yi kusa da fuskarta a hankali yana shafa mata ruwan nan

Kamar second goma yana dan shafa mata ruwan ta ja wata irin doguwar numfashi ta sauke kafin ta buda idannuwanta a tsorace

Ido hudu suka yi da yayanta, sai yayunta da du suka matso sosai kusa da ita

Da sauro ta janye hannunta daga na yayanta ta kai saman hannun Ummulkhair da take yiwa fushi aman tashin hankalin nan ya saka ta manta da wani fushi, hannunta ta damko tana kallonta ta ce" Ummu, mafarki na yi ko? Ki yiwa Allah ki samo wani faskare ko ki dauko wani birgi ki kima min na farka dan mafarkin nan sam bashi da dadi kar na mace a cikinsa

Ummulkhair ta sada idannuwanta tana jin kamar ta mayar da hannun agogo baya ta ce ita zata aure shi da wannan tashin hankalin da kanwar tasu ta shiga, shin tsoronsa ne take har yaka ko menene? Dama rashin kunyar tata a boye ne take yi ko meye?
Chapter 62 · 0% Book details