← Book details Adade Anayi Sai Gaskiya Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 128 OF 128

Sashe 128

Adade Anayi Sai Gaskiya Complete Hausa Novel · about 5 min read

SADAM AUDU MEMORIAL ORPHANAGE HOUSE KADUNA
Walima Uku akeyi a SAMOH, na daya Walimar saukar Kurannin wasu daga cikin yan gidan Marayun SAMOH, na biyu kuma Walimar aurar da Mata 50 da Maza 50 da akayi wanda aka Gina Compound Houses guda 20, wanda Abdulmajeed yayi , inda Maauratan zasu zauna. Na uku kuma Walimar Karamma da Award of excellence da aka ba Gatan Marayu na Biyu wanda Gwamntin k'asa ta bashi.
Taron ya kunshi Manyan mutane daga sassa daban daban, wanda suka zo karamma Gatan Marayu na biyu, Alhaji Zaid farinciki ne lullube a fuskanshi, Mahaifanshi duk sun hallara, yanuwa da abokan Arziki duk sun zo tayashi murna.
Jawabin minti 45 Zaid yayi akan marayu, da wanda ake yaddasu don an samesu ta wata hanya, daga karshe ya rufe taro da ba wa mutane shawara kan Marayu, su tainakesu, su kuma jasu a Jiki don su ma 'Ya'yane..
Kabbara kawai kakeji inda manya da yara ke fadin "ALLAH YA JI K'AN GATAN MARAYU NA FARKO. YA JA KWANAN GATAN MARAYU NA BIYU, YA RAYA GATAN MARAYU NA UKU" haka sukayi ta maimaitawa kamar wak'a. Har taro ya watse kowa na ta sambarka.
***
Washegari Yan Kano suka koma Kano, Abdulmajeed da Iyalanshi suka koma Abuja inda Najwa na aji na k'arshe a matakin jami'a.
Abdulmajeed ya zama wani babba wanda ake damawa dashi a kasa gabaki daya, duk wani kwangila da ya kunshi Ginegine ko wani abu makamancin haka shi keyi, duk shekara sai ya kai Mahaifanshi Hajji don sauke farali, in akace Mahaifa ana nufin dukansu Biyar,
Ko da zaayi taron nan Abdulmajeed ya ba Zaid gudunmuwar miliyan Goma, ba wai don Zaid din baya dashi ba, aa don shima yana kwadayin ladan, sai dai muce Allah ya bada lada Yayan Gatan Marayu.

A kaduna a ka bar Zaid da iyalanshi, sun dawo Nan Main House din Marigayi Alhaji Sadam da ke Mando, Gidan da babanshi ya fara kawoshi kafin yasa suka koma PH, inda zasu dan kwana biyu, saboda ta gama University, , a cewarshi yana son yaronshi ya girma a nan, ya nuna mishi legacy din Marigayi kakanshi.

Wurin karfe 5, Sadam na bacci a dakinshi, Zaid ya shigo cikin shiga irin ta leburori masu aikin gidan zuwa dakin Ziyada kamar mara gaskia, zatayi magana ya sa mata hannu a baki alamun tayi shiru, a hankali yake magana "kin taba hawa Kekenapep?" ta gyada kai alamun eh, yace "kina so ki kara hawa?" ta daga kai sama, yace "badda kama zanyi, sabida yau nayi mafarkin na hau keke napep, and ina so mafarkina ya zama gaskia, for once in my life, ina so in fita ba tare da an bini ba" itama a hankali tace "ta ya zaka fita, kasan Faisal ya sa tight security" tsaki yayi yace "zo muje" faken idanuwa sukayi suka bi dakin masu aiki dake baya, Hijab din H-Jidda ta gani a saman igiya, ta daura da zanin jgonees itama ta bada kama, sukayi kama da masu aiki, yayi gaba tana binshi a baya, kansu a k'asa don kar a ganesu, har ta gaban Faisal suka wuce yana waya, har sun kusa gate hankalin Faisal ya isa kan wani me tafiyan Oganshi, ya dan latse wayar ya fara dan binsu a baya yace "kai, waye nan ku tsaya, kai ke ku tsaya" Zaid na jin haka ya kamo hannun Ziyada ya jata da gudu, Faisal na ganin haka ya zaro ido yace "Oga ne, kar ku barshi a fita close the Gates" Zaid na gudu hannunshi rike da na ziyada yace "in baka bude min ba ka bar aiki a gidan nan" Maigadi na jin haka ya wangale Gate, Zaid da Ziyada suka fita suna Daria da gudu, Faisal na binsu a baya don kar ya rasu wasu securities kuma suka bi bayansu a Mota.
Gudu suke sosai, Ziyada ta gaji ta fara haki ta ci burki tace "wallahi na gaji, sai kace barayi" a haka Faisal suka tarar dasu yace "Haba Oga, ina zaka haka? Look at how you are dressed" Zaid yayi tsaki, ya kawar da kai gefe, Ziyada tace "Keke Napep wai yake son hawa" Faisal yace "shine ka bamu wahala?" ya karasa bakin Titi ya tsaida Keke Napep, yace "Oya ku shiga" Zaid da Ziyada suka shiga, Faisal yace da Me Napep "Mu zagaya Kaduna" Me Napep ya ja Napep dinshi, Faisal suka bi bayansu a Mota.
Ziyada ta lek'a tace "Suna binmu" Zaid yayi daria yace "duk kece kikaja aka kama mu, da ni kadai ne da basu kamani ba" Ziyada tace "Hello Mr, kaima fa ka gaji, ji nayi kana nishi samasama kamar zaka shide, saboda kar a kamani nayi sneaking da Gatan Marayu shiyasa na tsaya" rungumota yayi yace "Wa ya isa ya kamaki? Kin uwar marayu" Mai Napep ya kallesu ta mirror a baiyane yace "Allahu Akbar, yau gani ga Gatan Marayu, Kakata ta yanke saa" Zaid da Ziyada suka sa Daria.

*ALHAMDULILAH TAMMAT BI HAMDULLAH*

Alhamdulilah Alhamdulilah Alhamdulilah
Allah kuskuren da nayi a cikin wannan rubutun nawa Allah ka yafe min, na tuba, Allah ka sa ayi amfani da abubuwan dake daidai a labarin nan, wanda nayi kure Allah ka bamu ikon wasti dashi.

*DonAllah Don Girmansa Kar ayi min Document din wannan labari, hakkina ne, duk wanda yayi ana iya mana hukunci dashi ranar gobe k'iyama, donAllah a kiyayye*

*Kamar sunan Novel din nan A DADE ANA YI, AN KO DADE ANA YI, AMMA KUN HAKURI, HAR DAI HUTU AKA JE AMMA KUNA TARE DANI, RASHIN UPDATE DA WURI, YI MIN UZURIN DA KUKE YI, ba abunda zance muku illah Nagode Nagode*

*ZAUREN BIEBEE ISA, KU SANI I LOVE EACH AND EVERY SINGLE ONE OF YOU WITH EVERY FIBRE OF MY BEING, BIEBEE BA KOWA BACE IN BA KU* *A BIG SHOUTOUT TO ZBI ADMINS#1love*

*Lubna Sufyan, Aynarh Dimples, My Muskeeteers, kunsan sai hali yazo daya ake abota ai? Yeah right we are of the same feathers and we flock together, these two are my people, like you dont know me if you dont know they are my ROD, ILYSVM.*

*WATTPADIANS, MY DIEHARDFREAKINGFANS EVER SINCE DAY ONE, THANKYOU FOR TAKING YOUR TIME TO VOTE AND COMMENT ON EVERY SINGLE LINE, I APPRECIATE EACH AND EVERY SINGLE ONE OF YOU, AND ILOVE Y'LLS*

*Bibiliciousfreakingfans a duk inda kuke Wallahi banda abunda zance muku illa na rok'i Allah Allah ya hada mu a gidan Aljanna Firdausi Ameen*.

ALLAH YA HADAMU DA DUKKAN ALHERINSA (Amin )

#1love
#ADAY
#Bibiliciousfreakingfans
#anatare
#bissalam
#nagode

Biebee Isa.
Chapter 128 · 0% Book details