Sashe 121
Adade Anayi Sai Gaskiya Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yan dubai suka fara dawowa kafin 'yan Saudi, a lokacin har an kammala Gidan Daddy anyi furnishing dinshi da kayan Katakai masu kyau da tsada, wanda a companyn Daddyn aka siyesu, nan suka sauka, dadi kamar ya kashe Daddy da Zaid yace mishi Gidanshi ne, ya rungumeshi yana Godia, Abdulmajeed ma murna ya taya babanshi don be san da shirin nan ba, a ranar Zaid yace "Daddy ina rokon Alfarma ka bamu izini muje maka bikon Mummyn mu, kaga kar a kawo maka Amarya Uwargida bata nan" yace "haka ne, da kai na zanje na maido Maryam dita" duk aka hau shewa, har zuciyan Abdulmajeed da Ziyada sunji dadin yanda Zaid yayi, shiko na ciki na ciki.
A ranar suka dunguma Gidan Aunty Aynarh da Tsaraba Nik'i Nik'i, su Zinatu su ka rungume danginsu, Mairon ce a Parlo, Zaid dai yana daga chan bayabaya ba wanda zai kula yana bayan, nan dai bayan yan surutai, da neman yafiya Mairo zata bisu a yanzu.
Dakin Aunty Aynarh ta isketa din yi mata Godia, duk tana mata wani ladabi da biyayya "Aunty Aynarh, nagode kwarai Allah kadai zai biyaki" Aunty Aynarh tace "na fa sha gaya miki, ba don ke nake abu ba, da don ke ne da baayi ba, kuma wannan nok'e nok'en da kikeyi, na san fa halinki sarai, so kike in saki jiki, in shishige miki ki min wani mugun abu ko? To ba dani ba, ni da kisgiya nesa nesa, bance muyi gaba ba, amma ba ruwana dake ba ruwanki dani, wanda ya biya allonsa ya wanke" Mummy ta murmusa tace "ai Aunty Aynarh, kinsan ni kai tsaye ce, in zan miki wani abu ai ba sai nayi nok'e nok'e ba, na shiryu, nayi nadama, bansan meyasa har yanzu kike min kallon Hajia Mairon Da ba, nidai wallahi ba zan cutar dake ba, ina jiranki nan da kwana 7 a Gidana, kizo mu hada kai, mu samar ma Daddy-- au Abbanmu farinciki da kwanciyar hankali, mu nemi aljannarmu a tafin kafarshi, nidai nagode da taimakon da kika min, da so da kauna da kike nuna ma Yarana, tabbas da ba na sonki, amma yanda naga kinayi da yarana ko ba donAllah kike ba nikam kin gama min komai, akwai wani Girmamawa na musamman da nake ma duk masoyin Yarana, Nagode sai kinzo Kanwata"
Kafin Aunty Aynarh tace wani abu Mummy ta juya ta bar mata dakin.
Aunty Aynarh ta murmusa tace "ban tsaneki ba Hajia Mairo, halinki ne bana so, amma in kin chanza, bamu da matsala" bin bayanta tayi, suka isa parlo, nan a ka k'ara gaisawa, Ziyada ta dauko ma Aunty Aynarh tsarabanta na dubai da Saudia, tayi ta godia, sai wurin 9, suka bar Gidan gabaki daya a ka koma Gidan Daddy, kafin Maama, Najwa, Zaid da Ziyada sai Hajjo suka koma Gidan Paapa .
Mummy ta fara zaban part dinta na dama, na Alhaji Daddy ne a tsakiya, tsarin Gidan ya mata kyau, kunyan Zaid takeji sosai wallahi, tana ganin yanda yake dojewa tun dazun, dama ai batayi tsammanin ya share komai lokaci guda ba amma dai tunda ance komai ya wuce zata zage damtsen wurin ganin ta farantawa kowa rai.
Ta fada toilet tayi wankanta dta shirya zuwa Turaka.
_A gurguje_.
*Anzo gurin*
A yau Asabar, dubannin Jamaa daga wurare daban daban suka shaida daurin Auren Alhaji Abba Abu, da Amaryarsa Hajia Aynau Mustapha bisa sadaki Naira dubu 40..
Da kuma auren Abdulmajeed Abba Abu da Amaryarsa Najwa Sada Abu, bisa Sadaki Naira dubu 100 lakadan ba ajalan ba sai fatan Allah ya basu zaman lafiya Ameen....
Hello Bibilicious freaking fans, afuwan, nasan wasu sunyi tsammanin ganin karshen ADAY a wannan page din, nima hakan nayi tsammani, i thought zan iya juye komai a cikin page din nan, amma naga hakan ba zai yiwu ba, in nayi hakan zanyi rushing kaina kuma komai in summary zanyi, wanda nasan ba haka zaku so ba. So don kar kuyi ta jira shisa na baku wannan ku fara kafin pagen karshen yazo nan ba da dadewa ba.
So kuban kwana daya zuwa biyu in gama concluding, komai fa plus the everyevery (wink) if you know you know kawai.
#1love
#ADAY
#bibiliciousfreakingfans
#anatare
#nagode.
Biebee Isa.
💭A DADE ANA YI....sai gaskia💭
NA
Wattpad:@biebeeisa
KARSHE
Kafin daurin Auren.
Sai da suka kwana 5 a Yola, sunje nuna Zaid wurin dangi, da kuma sanar dasu Biki saura Sati 2 a wannan lokacin, Zaid be yarda yaje wani Lodge ba, nan gidan Baffansu Maama suke kwana, dakin samari ma, a cewarshi zai san kowa da kowa, zuwa ake ganin dan Yaya Ai da akayi zaton ya mutu, kowa na Alfahari dashi kasancewarshi jininsu, duk inda yaje sai ya raba Alheri, Abokan wasanshi suyi ta mai tsiya be iya fullanci ba. Haka dai sukayi sabo da Gwaggoninshi da Matan kawunnanshi, nan suka dawo Kano.
'Yan Yola sun iso garin Kano, su Baffa Hussaini, da k'annen Maama da Matan Yayunsu mutane sunfi 20, tun biki na sauran Kwana 2, Gidan Paapa cike yake da Mutanen Yola, Amare kuwa Najwa da Ziyada da Yanmata wanda kansu ke daya kuma suna Gidan Baba Abba, kamar yanda Zaid ya ma Kaveri da Mamarta da Vijhay Alkawari cewa lokacin Biki, zai tura musu kudin Jirgi suzo bikin to hakan yayi, already ya tura musu har sun iso Nigeria, Mota ya tura a dauko suwo, murna gun Najwa baa magana.
Matar Baffa Shamsu Karima(Matar k'anin Maama) gwana ce wurin gyaran Jiki, tun da sukazo take mamulan jikin Najwa da gyara, Maama ta shigo lokacin da ake mata gyaran Jiki, Maama tace "Ahh Aunty Karima, ya da son kai?" Aunty Kariman da ta dage tana murzan jikin Najwa da wami kwababben abu ya dago ta kalleta tace "Yaya A'i son kai name?" Maama tace "Ya naga kin kama diyarki kina ta gyara ni kin bar min nawa? Nima fa diyata Amarya ce" Aunty Karima tace "wake nan?" tace "Ziyadatu mana, kin kama Najwa sai gyara kike ni tawa ta zama 'yar kallo" Ziyada ta boye kanta, bata son tayi surukuta da Maama, amma Maama na bata kunya.
Aunty Karima tace "Yo na isa na k'i gyara Matar Gatan Marayu Aunty A'i? Wai da na fara da sabuwar Amarya, itama sai a mata" Maama tayi daria tace "Yauwa yanzu naji batu" sukayi daria gabaki daya, Ziyada ta rufe face dinta da tafin hannunta.
Wayarta tayi k'ara, special ringtone din da tasa domin Zaid ya sa ta gane *Forever* dinta ne, Najwa tace "Didi, ba zaki dauka ba? Ba Bhaiy bane" Ziyada ta dan turo baki tace "wai sai dai in fito mu tafi" Najwa tace "bani wayar in mishi magana" Aunty Karima tace "Yara kenan, kuna wasa da zama, yanzu Mijinki na kiranki kin k'i dauka, in kin k'i amsa kiran Miji to me zai hanashi sauraro ko kula matan banza? Yanda yake da kudi da Kyau kuna tunanin ba a kawo mai hari?" nan da nan jikin Ziyada yayi Sanyi, tace "wallahi wata sa'in muke jama kanmu kishiyoyi, tashi ki bi Mijinki kinji Ziyadatu, gobe da Safe kizo na fara miki gyaran"
Jakkarta ta dauka ta ma Aunty karima da Najwa sai da safe, fita tayi ta lek'a dakin Maama don mata sallama, ji tayi an rik'o hannunta, a dan firgice ta juyo ganin Zaid ne ya sata saukar da ajiyar zuciya, baya so hankalin mutane suyo kansu, ya ja hannunta zuwa dakin Paapa da tun da yan Yola suka zo ya koma Gidan Hajjo da zama, mayar da k'ofa yayi ya rufe ya mata rumfa a inda take kusa da bango da hanayensa yana mata wani irin kallon da ya sa ta janye idanuwanta yace "Babe, don nace tare zamu tafi shiyasa ki k'a ki daukan wayana?"ta dan shagwabe fuska tace "bafa haka bane" yace "I'm just missing you ne, jiya kika biye ma Baby kuka gudu gidan Daddy, na gaya miki ba daya kuke da ita ba, you are married amma ki dina biye mata kuna yawo, ba kwa nan ba kwa chan, tunda bakya so ki bini, muyi bankwana ki tsaya ki cigaba da abunda kike wanda ya fini" ya fada cike da shagwaba tare da juya mata baya.
Da sauri ta rungumeshi tare da kwantar da kanta a kan bayanshi tace "mu tafi Kaji myforever, duk inda zaka tafi ina biye da kai, kaine har abada dina, dama gyaran Jiki Aunty Karima zata min, amma tace gobe da safe zata min nawa, yanzu tana chan tana gyara maka baby" juyo da ita yayi gabanshi yace "Yauwa, inga Gyaran Gashin da akace anje dazun" be jira cewarta ba ya warware mata ribbon din da aka daure mata gashin dashi, gashin ya sauka kan kafadunta, sai salk'i da walk'i yake, da yatsun hannunshi ya dinga sharce mata gashin, Man da ya bi hannunshi ya chusa anashi gashin kai din, ya matso da ita daf dashi har suna jin hucin juna, yace "My Forever!! Ina sonki sosai" lumshe idanunta tayi ta bude so biyu "Nima ina sonka sosai" Mayafin ya daura mata a kai yace "mutafi ko?" gyada mai kai tayi don jikinta ya soma mutuwa.
Jakarta ya karba kafin ya ja hannunta su ka fita daga dakin Paapa suka nufa na Maama don yi mata Sallama.
***
A bayan seat ya tattarota gabaki daya jikinshi yana shak'ar kamshinta, waya yake da Abdulmajeed "Yeah, na dauki matata mun bar gidansu Baby, eh din bazan barta din ba, da mijinta ta dinga kwana wani gida, hahaha Mallam gata dai" sa mata wayan yayi a kunne "Hello YaMaji, ina wuni, eh mun tafi, tana chan Aunty Karima na gyara mata jiki harda lalle zaayi, hahah dagaske YaMaji, Allah shi kaimu sai da safe" Zaid yace "Mallam sai na ganka Gobe" ya datse wayan.
"Babe, wai gyaran jikin na meye? Naga jikinku ba wani abun gyara, gashi ne kuma kunje saloon, to meye zaa gyara" gyara kwanciyarta tayi a jikinshi, tace "ka tambayeni gobe in Aunty Karima ta gama gyaran, zaka ga Changes" yace "i cant wait" ya rungumeta a jikinshi har suka iso Guest house dinshi.
A wannan daren suka jiyar da juna kauna, sunyi missing juna kwarai dagaske, su ka kwanta manne da juna.
Washegari bayan sunyi breakfast, suka shirin zuwa Gidan Maama lokacin ana gobe daurin Aure.
A ranar suka dunguma Gidan Aunty Aynarh da Tsaraba Nik'i Nik'i, su Zinatu su ka rungume danginsu, Mairon ce a Parlo, Zaid dai yana daga chan bayabaya ba wanda zai kula yana bayan, nan dai bayan yan surutai, da neman yafiya Mairo zata bisu a yanzu.
Dakin Aunty Aynarh ta isketa din yi mata Godia, duk tana mata wani ladabi da biyayya "Aunty Aynarh, nagode kwarai Allah kadai zai biyaki" Aunty Aynarh tace "na fa sha gaya miki, ba don ke nake abu ba, da don ke ne da baayi ba, kuma wannan nok'e nok'en da kikeyi, na san fa halinki sarai, so kike in saki jiki, in shishige miki ki min wani mugun abu ko? To ba dani ba, ni da kisgiya nesa nesa, bance muyi gaba ba, amma ba ruwana dake ba ruwanki dani, wanda ya biya allonsa ya wanke" Mummy ta murmusa tace "ai Aunty Aynarh, kinsan ni kai tsaye ce, in zan miki wani abu ai ba sai nayi nok'e nok'e ba, na shiryu, nayi nadama, bansan meyasa har yanzu kike min kallon Hajia Mairon Da ba, nidai wallahi ba zan cutar dake ba, ina jiranki nan da kwana 7 a Gidana, kizo mu hada kai, mu samar ma Daddy-- au Abbanmu farinciki da kwanciyar hankali, mu nemi aljannarmu a tafin kafarshi, nidai nagode da taimakon da kika min, da so da kauna da kike nuna ma Yarana, tabbas da ba na sonki, amma yanda naga kinayi da yarana ko ba donAllah kike ba nikam kin gama min komai, akwai wani Girmamawa na musamman da nake ma duk masoyin Yarana, Nagode sai kinzo Kanwata"
Kafin Aunty Aynarh tace wani abu Mummy ta juya ta bar mata dakin.
Aunty Aynarh ta murmusa tace "ban tsaneki ba Hajia Mairo, halinki ne bana so, amma in kin chanza, bamu da matsala" bin bayanta tayi, suka isa parlo, nan a ka k'ara gaisawa, Ziyada ta dauko ma Aunty Aynarh tsarabanta na dubai da Saudia, tayi ta godia, sai wurin 9, suka bar Gidan gabaki daya a ka koma Gidan Daddy, kafin Maama, Najwa, Zaid da Ziyada sai Hajjo suka koma Gidan Paapa .
Mummy ta fara zaban part dinta na dama, na Alhaji Daddy ne a tsakiya, tsarin Gidan ya mata kyau, kunyan Zaid takeji sosai wallahi, tana ganin yanda yake dojewa tun dazun, dama ai batayi tsammanin ya share komai lokaci guda ba amma dai tunda ance komai ya wuce zata zage damtsen wurin ganin ta farantawa kowa rai.
Ta fada toilet tayi wankanta dta shirya zuwa Turaka.
_A gurguje_.
*Anzo gurin*
A yau Asabar, dubannin Jamaa daga wurare daban daban suka shaida daurin Auren Alhaji Abba Abu, da Amaryarsa Hajia Aynau Mustapha bisa sadaki Naira dubu 40..
Da kuma auren Abdulmajeed Abba Abu da Amaryarsa Najwa Sada Abu, bisa Sadaki Naira dubu 100 lakadan ba ajalan ba sai fatan Allah ya basu zaman lafiya Ameen....
Hello Bibilicious freaking fans, afuwan, nasan wasu sunyi tsammanin ganin karshen ADAY a wannan page din, nima hakan nayi tsammani, i thought zan iya juye komai a cikin page din nan, amma naga hakan ba zai yiwu ba, in nayi hakan zanyi rushing kaina kuma komai in summary zanyi, wanda nasan ba haka zaku so ba. So don kar kuyi ta jira shisa na baku wannan ku fara kafin pagen karshen yazo nan ba da dadewa ba.
So kuban kwana daya zuwa biyu in gama concluding, komai fa plus the everyevery (wink) if you know you know kawai.
#1love
#ADAY
#bibiliciousfreakingfans
#anatare
#nagode.
Biebee Isa.
💭A DADE ANA YI....sai gaskia💭
NA
Wattpad:@biebeeisa
KARSHE
Kafin daurin Auren.
Sai da suka kwana 5 a Yola, sunje nuna Zaid wurin dangi, da kuma sanar dasu Biki saura Sati 2 a wannan lokacin, Zaid be yarda yaje wani Lodge ba, nan gidan Baffansu Maama suke kwana, dakin samari ma, a cewarshi zai san kowa da kowa, zuwa ake ganin dan Yaya Ai da akayi zaton ya mutu, kowa na Alfahari dashi kasancewarshi jininsu, duk inda yaje sai ya raba Alheri, Abokan wasanshi suyi ta mai tsiya be iya fullanci ba. Haka dai sukayi sabo da Gwaggoninshi da Matan kawunnanshi, nan suka dawo Kano.
'Yan Yola sun iso garin Kano, su Baffa Hussaini, da k'annen Maama da Matan Yayunsu mutane sunfi 20, tun biki na sauran Kwana 2, Gidan Paapa cike yake da Mutanen Yola, Amare kuwa Najwa da Ziyada da Yanmata wanda kansu ke daya kuma suna Gidan Baba Abba, kamar yanda Zaid ya ma Kaveri da Mamarta da Vijhay Alkawari cewa lokacin Biki, zai tura musu kudin Jirgi suzo bikin to hakan yayi, already ya tura musu har sun iso Nigeria, Mota ya tura a dauko suwo, murna gun Najwa baa magana.
Matar Baffa Shamsu Karima(Matar k'anin Maama) gwana ce wurin gyaran Jiki, tun da sukazo take mamulan jikin Najwa da gyara, Maama ta shigo lokacin da ake mata gyaran Jiki, Maama tace "Ahh Aunty Karima, ya da son kai?" Aunty Kariman da ta dage tana murzan jikin Najwa da wami kwababben abu ya dago ta kalleta tace "Yaya A'i son kai name?" Maama tace "Ya naga kin kama diyarki kina ta gyara ni kin bar min nawa? Nima fa diyata Amarya ce" Aunty Karima tace "wake nan?" tace "Ziyadatu mana, kin kama Najwa sai gyara kike ni tawa ta zama 'yar kallo" Ziyada ta boye kanta, bata son tayi surukuta da Maama, amma Maama na bata kunya.
Aunty Karima tace "Yo na isa na k'i gyara Matar Gatan Marayu Aunty A'i? Wai da na fara da sabuwar Amarya, itama sai a mata" Maama tayi daria tace "Yauwa yanzu naji batu" sukayi daria gabaki daya, Ziyada ta rufe face dinta da tafin hannunta.
Wayarta tayi k'ara, special ringtone din da tasa domin Zaid ya sa ta gane *Forever* dinta ne, Najwa tace "Didi, ba zaki dauka ba? Ba Bhaiy bane" Ziyada ta dan turo baki tace "wai sai dai in fito mu tafi" Najwa tace "bani wayar in mishi magana" Aunty Karima tace "Yara kenan, kuna wasa da zama, yanzu Mijinki na kiranki kin k'i dauka, in kin k'i amsa kiran Miji to me zai hanashi sauraro ko kula matan banza? Yanda yake da kudi da Kyau kuna tunanin ba a kawo mai hari?" nan da nan jikin Ziyada yayi Sanyi, tace "wallahi wata sa'in muke jama kanmu kishiyoyi, tashi ki bi Mijinki kinji Ziyadatu, gobe da Safe kizo na fara miki gyaran"
Jakkarta ta dauka ta ma Aunty karima da Najwa sai da safe, fita tayi ta lek'a dakin Maama don mata sallama, ji tayi an rik'o hannunta, a dan firgice ta juyo ganin Zaid ne ya sata saukar da ajiyar zuciya, baya so hankalin mutane suyo kansu, ya ja hannunta zuwa dakin Paapa da tun da yan Yola suka zo ya koma Gidan Hajjo da zama, mayar da k'ofa yayi ya rufe ya mata rumfa a inda take kusa da bango da hanayensa yana mata wani irin kallon da ya sa ta janye idanuwanta yace "Babe, don nace tare zamu tafi shiyasa ki k'a ki daukan wayana?"ta dan shagwabe fuska tace "bafa haka bane" yace "I'm just missing you ne, jiya kika biye ma Baby kuka gudu gidan Daddy, na gaya miki ba daya kuke da ita ba, you are married amma ki dina biye mata kuna yawo, ba kwa nan ba kwa chan, tunda bakya so ki bini, muyi bankwana ki tsaya ki cigaba da abunda kike wanda ya fini" ya fada cike da shagwaba tare da juya mata baya.
Da sauri ta rungumeshi tare da kwantar da kanta a kan bayanshi tace "mu tafi Kaji myforever, duk inda zaka tafi ina biye da kai, kaine har abada dina, dama gyaran Jiki Aunty Karima zata min, amma tace gobe da safe zata min nawa, yanzu tana chan tana gyara maka baby" juyo da ita yayi gabanshi yace "Yauwa, inga Gyaran Gashin da akace anje dazun" be jira cewarta ba ya warware mata ribbon din da aka daure mata gashin dashi, gashin ya sauka kan kafadunta, sai salk'i da walk'i yake, da yatsun hannunshi ya dinga sharce mata gashin, Man da ya bi hannunshi ya chusa anashi gashin kai din, ya matso da ita daf dashi har suna jin hucin juna, yace "My Forever!! Ina sonki sosai" lumshe idanunta tayi ta bude so biyu "Nima ina sonka sosai" Mayafin ya daura mata a kai yace "mutafi ko?" gyada mai kai tayi don jikinta ya soma mutuwa.
Jakarta ya karba kafin ya ja hannunta su ka fita daga dakin Paapa suka nufa na Maama don yi mata Sallama.
***
A bayan seat ya tattarota gabaki daya jikinshi yana shak'ar kamshinta, waya yake da Abdulmajeed "Yeah, na dauki matata mun bar gidansu Baby, eh din bazan barta din ba, da mijinta ta dinga kwana wani gida, hahaha Mallam gata dai" sa mata wayan yayi a kunne "Hello YaMaji, ina wuni, eh mun tafi, tana chan Aunty Karima na gyara mata jiki harda lalle zaayi, hahah dagaske YaMaji, Allah shi kaimu sai da safe" Zaid yace "Mallam sai na ganka Gobe" ya datse wayan.
"Babe, wai gyaran jikin na meye? Naga jikinku ba wani abun gyara, gashi ne kuma kunje saloon, to meye zaa gyara" gyara kwanciyarta tayi a jikinshi, tace "ka tambayeni gobe in Aunty Karima ta gama gyaran, zaka ga Changes" yace "i cant wait" ya rungumeta a jikinshi har suka iso Guest house dinshi.
A wannan daren suka jiyar da juna kauna, sunyi missing juna kwarai dagaske, su ka kwanta manne da juna.
Washegari bayan sunyi breakfast, suka shirin zuwa Gidan Maama lokacin ana gobe daurin Aure.