Sashe 124
Adade Anayi Sai Gaskiya Complete Hausa Novel · about 8 min read
Duk sunci gayu cikin shiga ta Alfarma, Ziyada da k'awayensu na dakin Najwa ana ta kai da kawowa, Najwa tayi kyau harta gaji, Meenerhparrot's glam tayi mata makeup, sanye take cikin wani cream lace, da mayafinta sky blue, sosai tayi kyau, k'amshi baa magana, tun a cikin gidan ake ta selfie, Maama ta shigo dakin cikin shiga ta Alfarma tace "Zaineema, ki hada ku ga motoci chan ku shiga ku nufi Gidanku, mu mun tafi daukan Amarya, ku wuce chan Mummynku na jiranku" Zaineema tace "to Maama yanzu zamu tafi" Maama ta fita suka bar Gidan ita da tawagarta zuwa daukar Amarya Hajia Aynarh.
Zaineema tace "Oya ku tashi muje Gida" Ziyada ta mik'ar da Najwa, Kaveri da sauran cousins din su Najwa kowa ya tashi ya gyara mayafinshi, su ka fita daga dakin, kamar daga sama sukaji Sallamar Ango,ga Ango ga Ango, Najwa na jinshi ta sadda kai k'asa, hannu ya ba Zaineema sukayi musabaha, Ziyada kuwa ta sa ihu "YaMaji ka ganka kuwa, wannan haduwa haka?" be amsata ba ya hau amsa gaisuwan yanmatan Amaryan dake wurin kafin yace "Ina zuwa haka Zuzu?" tace "Gida zamuje" Zaineema ya kalla da ido, tuni ta harbo jirginshi, tace "Kaveri, lets wait for the bride outside, oya ku muje waje, har ke Ziyada" Zaineema ta tasa keyarsu gabaki daya suka fita suka barsu su biyu a Parlorn.
Kallonta yakeyi kamar ya hadiyeta, sosai ta mishi kyau, sonta na fuzgarshi, yana sonta matuka, yana kaunarta yana begenta, a hankali ya karasa gunta cikin nustuwa, "PureHeart" ya kira sunanta cikin wani siga, a hankali ta dago idanuwanta ta watsa mai cikin sanyi tace "Jaaan" a hankali kamar me rada yace "You are Mine (Ke tawa ce)" itama tace "I'm Yours (Ni taka ce)" yace "i wanted to this for long(ina so inyi haka tun da dadewa)" da dan mamaki ta kalloshi tace "Mene?" Hada jikinsu yayi ta hanyar rungumeta dauke da mixed feelings yace "this" bata yi magana ba illa itama ta kai hannunta bayanshi tare da lumshe ido, sun kusa mintuna uku a haka, jefi jefi suna sauke ajiyar zuciya kafin ya sausauta rikon da ya mata, yana kallon idanunta, sauke su tayi kasa, har yanzu jikinsu na daf da juna, har tanajin hucin numfashinshi a goshinta, don Abdulmajeed dogo ne, hannunshi ya sa ya dago ha66arta sama yanda zata fuskanceshi, idanuwanta ta mayar ta rufe, bakinshi ya kai kan nata yayi kissing dinta lightly kafin ya sake rungumeta, cike da sanyin murya tace "Jaaan" shima yace "PureHeart" tace "Mein bohot pyar kharta hoon(ina sonka sosai)" Yau da gobe ya san maanar hakan shima yace "I love you too PureHeart, ina sonki, lets get you home" murmushi tayi ya ja hannunta, suka rufe Gidan, suka fita, da suka isa Haraban Gidan, su Zaineema sun tafi, Motar da ta kawoshi Gidan ya bude mata, ta shiga shima ya shiga baya, yace da Driver "Muje Gidan Daddy" Driver ya ja Motar..
A bayan Motan ya rik'o hannunta ya dinga kissing din hannun wai lallen yayi kyau sosai, ita dai bata ce komai ba, haka har suka isa Gidan Daddy..
Tun daga farkon Unguwar suke ganin motoci wanda da alama gidan suka zo, Sai da ya fita ya bude mata k'ofa kafin ta fito, Gidan Cike yake, harabar Gidan anyi decorating dinshi, daga chan gefe ga UmmuSudais Catering service, dayan bangaren kuma DJ ne, Mata ne ko ta ina wasu na cikin canopies zaune ana fira, hankalin mutane ya dawo kansu, ga Ango da Amarya, Mummy na jin haka ta fito daga cikin Kawayenta ta karaso gunsu, rungume Najwa tayi ta mata kiss a goshi, kafin ta rungume Majeed, tana jin zata iya chanza komai amma ba zata iya chanza nuna ma Yaranta So a baiyane ba, aa ita haka take, a baiyane take nuna son 'yayanta tace "Kai ka kawo matarka ka koro mun yarana ko?" daria yayi, yace "Oya ga Iyayenka chan kuje gaishesu, da kanta ta hada hanayen su wuri guda ta musu iso wurin kawayenta da ke zaune, wasu ma batayi zaton zasu zo ba sai gasu, bin iyayen yake tayi yana gaishesu, nan Mairo ta ya fito Cameraman ya dauke su hoto, ta shiga tsakiar Abdulmajeed da Najwa ta rungumosu aka daukesu, farincikin ganin danta cikin farinciki ya wanke mata tambarin jin zafin zuwan kishiyarta.
Abdulmajeed yace "Mummy taron Mata ne, nikam barin tafi" Mummy tace "kuma kuna taronku ai nayi mamakin ganinka a nan" yayi daria ya kalli Najwa, sukayi magana ta ido ya juya ya fita.
Mummy ta ja Najwa zuwa inda yanmata suke ta zaunar. Gudar da sukaji ne ya sanar dasu cewa Amarya ta iso, zata rantse sai da gabanta ya fadi, jin hannun Mrs Splendid ya k'ara mata kwarin guiwa tace "kece hajia Mairo, wanda ba kya tsoro ko fargaban komai, durkusa ma wada ba gajiyawa bane, Bariki" Hajia Mairo ta murmusa tace "Iyawa, Nagode Maman Husna" Mairo ta chanza face zuwa na farinciki ta amsa microphone a hannun DJ tace "Oya Oya OYa, a tashi tsaye, ina son kowa ya tashi tsaye , ku tayani maraba da Amaryata,ga Amaryata tazo, Dj samana wakar Lagbaja" nan da nan Dj ya saka kidar Lagbaja, Mairo ta fara takawa, sowa kakeji, kawaayen Mairo yan bariki, suka tayata takawa suka karasa inda su Hajia Aynarh da danginta ke zuwa, Mairo na zuwa ta rungumo Aunty Aynarh, nan aka kaure da rawa Mairo ta kamo hannun Aunty Aynarh tayi suka dunguma zuwa part din Aunty Aynarh, Maama ta sa key ta bude Part din, Aunty Aynarh tayi addua ta shiga da bismillah, MashaAllah nan aka sada Amarya da dakinta, Gidanta yayi kyau matuka, nan yan ganin daki suka dinga shiga dakin one by one.
Aka bar Aunty Aynarh da Aminnanta a daki, sauran kuma suka fito waje, nan aka ci Abinci, mostly Abincin Yarbawa ne, Amala da Ganda, wata Yayar Aunty Aynarh ta ba Dj Disc dinsu na wakokin Yarbawa aka basu fili, Dj ya samusu wakokinsu, nan suka hau juya mazaunai cikin iyawa, nan suka zama abun kallo, kafin Mairo da Kawayenta suma suka shigo fili don baja tasu kolin, daga baya kuma Mairo ta jawo yayanta su Zaineema, Ziyada, Zinatu da Najwa suka shiga Part din Aunty Aynarh suka fito da ita fili suka chashe, Taron Matan yayi sosai, an ci an sha, an gyatse, harda su turmin atamfa da leshi a sourvenirs, nan Yan ZBI ake ta hadama, suna warwaso, Haly Ghana dake rabo tace "ku kwantar da hankalinku, duk zaku samu, akwai da yawa" softie ta kalleta tace "gaskia ba zamuyi inviting dinsu Dinner din anjima ba, dube su da yawa fa su256, ai sai su ba mu kunya" Sholingaye tace "strictly on Invitation ne. Ko sun zo sai dai su tsaya a harabar wurin".
Da Daddare wurin 8 kuma aka dunguma akayi wurin Dinner Party da zaayi a Afficent
Bristol palace inda akayi na su Ziyada, wuri yayi wuri, taro ne har iyaye, bayan kowa ya zauna, Abokan Ango da kawayen Amarya suka shigo ciki, wurin da aka tanada domin su suka nufa suka zauna, nan akayi introducing shigowan Gatan Marayu da Matarsa, da kuma kanwar Ango Zaineea da Mijinta, suma shigowa sukayi a tare, Zaid cikin Rigar Suit Bak'a sai ta ciki fara da bowtie maroon, Ziyada kuma da riga bak'a, da gyalenta black and white.


Daga Bisani kuma akayi sanarwar isowan Amarya da angonta, Abdulmajeed cikin shiga ta Alfarma, Navy blue Suit da skyblue shirt, Najwa kuwa Navy blue wedding gown ne me dogon hannu, da mayafi sky blue, sosai sukayi kyau, cikin tafiyan couples suka iso wurin da aka tanada dominsu, bayan sun zazzauna, aka fara gudanar da dinner, Baba Ado shine ya bude taro da Addua, Welcome speech by Gatan Marayu, Kaveri ta bada takaitacen Tarihin Najwa da turancinta na Indiyawa, Aliyu ya bada takaitaccen tarihin Abdulmajeed, aka ci abinci, aka dan taka, Maama dai bata rawa, Hajia Mairo kam ta chashe, Amaray Aunty Aynarh ma ta dan taka, haka aka ci taro taro ya watse lafiya, abun dai sai wanda yaje ya gani.
*A GURGUJE*
WasheGari da Safe gabaki daya Family din aka hadu a Parlorn Daddy, Paapa ya bude taro da addua, Daddy ya fara da musu gajian biki, kafin ya fara da ""Ammm, Tohm Abdulmajeed a yau ka sake zama Miji, Hak'k'i ya rataya a wuyanka, ba zan gaya maka hakkin matarka kanka ba, amma na san zaka kula ka sauke duk wasu hak'k'unan dake rataye a wuyanka, Abdulmajeed na san ka da Hakuri, na sanka da kawaici da kau da kai, nasan ba zaka bani kunya ba, nasan zaka tayani k'arafafa zumuncina da na danuwana, nasan ba zaka bari ta dalilinka zumuncinmu ya ruguje ba, Abdulmajeed ka kula da Najwa, Abdulmajeed ku zauna lafiya, zaman lafiyanku shine namu kana jina?" Ya dago ya kalleshi yace "Eh Daddy, naji, kuma InshaAllah ba zaku sameni da wani abun da ba daidai ba" Daddy ya maida hankalinshi kan Najwa yace "Najwa, a sanin da na miki ke yarinya ce me kirki da son yanuwanta, na fuskanci kina da hakuri Paapanku ya tabbatar min da haka, amma NAJWA ki sani, aure ya sha bamban da abubuwan da kike gani a talabijin, aure ya wuce soyayyar da kike gani na India, Aure dan zo mu zauna, zo mu saba ne, shauki da soyayyar da kuke ma junanku, ba wai ya na nufin ba zaku sabu sabani ba, aa zaku samu sabani, zaku bata ran junanku, amma hakan be nufin ki dauki waya ki kira maamanki ko mumnynku ki gaya musu, ki rike sirrin gidanki, dana Mijinki, in kun samu sabani ku shirya kanku, kiyi hakuri kinji Najwa? Allah ya baku zaman lafiya da zuri'a Dayyiba".
Zaineema tace "Oya ku tashi muje Gida" Ziyada ta mik'ar da Najwa, Kaveri da sauran cousins din su Najwa kowa ya tashi ya gyara mayafinshi, su ka fita daga dakin, kamar daga sama sukaji Sallamar Ango,ga Ango ga Ango, Najwa na jinshi ta sadda kai k'asa, hannu ya ba Zaineema sukayi musabaha, Ziyada kuwa ta sa ihu "YaMaji ka ganka kuwa, wannan haduwa haka?" be amsata ba ya hau amsa gaisuwan yanmatan Amaryan dake wurin kafin yace "Ina zuwa haka Zuzu?" tace "Gida zamuje" Zaineema ya kalla da ido, tuni ta harbo jirginshi, tace "Kaveri, lets wait for the bride outside, oya ku muje waje, har ke Ziyada" Zaineema ta tasa keyarsu gabaki daya suka fita suka barsu su biyu a Parlorn.
Kallonta yakeyi kamar ya hadiyeta, sosai ta mishi kyau, sonta na fuzgarshi, yana sonta matuka, yana kaunarta yana begenta, a hankali ya karasa gunta cikin nustuwa, "PureHeart" ya kira sunanta cikin wani siga, a hankali ta dago idanuwanta ta watsa mai cikin sanyi tace "Jaaan" a hankali kamar me rada yace "You are Mine (Ke tawa ce)" itama tace "I'm Yours (Ni taka ce)" yace "i wanted to this for long(ina so inyi haka tun da dadewa)" da dan mamaki ta kalloshi tace "Mene?" Hada jikinsu yayi ta hanyar rungumeta dauke da mixed feelings yace "this" bata yi magana ba illa itama ta kai hannunta bayanshi tare da lumshe ido, sun kusa mintuna uku a haka, jefi jefi suna sauke ajiyar zuciya kafin ya sausauta rikon da ya mata, yana kallon idanunta, sauke su tayi kasa, har yanzu jikinsu na daf da juna, har tanajin hucin numfashinshi a goshinta, don Abdulmajeed dogo ne, hannunshi ya sa ya dago ha66arta sama yanda zata fuskanceshi, idanuwanta ta mayar ta rufe, bakinshi ya kai kan nata yayi kissing dinta lightly kafin ya sake rungumeta, cike da sanyin murya tace "Jaaan" shima yace "PureHeart" tace "Mein bohot pyar kharta hoon(ina sonka sosai)" Yau da gobe ya san maanar hakan shima yace "I love you too PureHeart, ina sonki, lets get you home" murmushi tayi ya ja hannunta, suka rufe Gidan, suka fita, da suka isa Haraban Gidan, su Zaineema sun tafi, Motar da ta kawoshi Gidan ya bude mata, ta shiga shima ya shiga baya, yace da Driver "Muje Gidan Daddy" Driver ya ja Motar..
A bayan Motan ya rik'o hannunta ya dinga kissing din hannun wai lallen yayi kyau sosai, ita dai bata ce komai ba, haka har suka isa Gidan Daddy..
Tun daga farkon Unguwar suke ganin motoci wanda da alama gidan suka zo, Sai da ya fita ya bude mata k'ofa kafin ta fito, Gidan Cike yake, harabar Gidan anyi decorating dinshi, daga chan gefe ga UmmuSudais Catering service, dayan bangaren kuma DJ ne, Mata ne ko ta ina wasu na cikin canopies zaune ana fira, hankalin mutane ya dawo kansu, ga Ango da Amarya, Mummy na jin haka ta fito daga cikin Kawayenta ta karaso gunsu, rungume Najwa tayi ta mata kiss a goshi, kafin ta rungume Majeed, tana jin zata iya chanza komai amma ba zata iya chanza nuna ma Yaranta So a baiyane ba, aa ita haka take, a baiyane take nuna son 'yayanta tace "Kai ka kawo matarka ka koro mun yarana ko?" daria yayi, yace "Oya ga Iyayenka chan kuje gaishesu, da kanta ta hada hanayen su wuri guda ta musu iso wurin kawayenta da ke zaune, wasu ma batayi zaton zasu zo ba sai gasu, bin iyayen yake tayi yana gaishesu, nan Mairo ta ya fito Cameraman ya dauke su hoto, ta shiga tsakiar Abdulmajeed da Najwa ta rungumosu aka daukesu, farincikin ganin danta cikin farinciki ya wanke mata tambarin jin zafin zuwan kishiyarta.
Abdulmajeed yace "Mummy taron Mata ne, nikam barin tafi" Mummy tace "kuma kuna taronku ai nayi mamakin ganinka a nan" yayi daria ya kalli Najwa, sukayi magana ta ido ya juya ya fita.
Mummy ta ja Najwa zuwa inda yanmata suke ta zaunar. Gudar da sukaji ne ya sanar dasu cewa Amarya ta iso, zata rantse sai da gabanta ya fadi, jin hannun Mrs Splendid ya k'ara mata kwarin guiwa tace "kece hajia Mairo, wanda ba kya tsoro ko fargaban komai, durkusa ma wada ba gajiyawa bane, Bariki" Hajia Mairo ta murmusa tace "Iyawa, Nagode Maman Husna" Mairo ta chanza face zuwa na farinciki ta amsa microphone a hannun DJ tace "Oya Oya OYa, a tashi tsaye, ina son kowa ya tashi tsaye , ku tayani maraba da Amaryata,ga Amaryata tazo, Dj samana wakar Lagbaja" nan da nan Dj ya saka kidar Lagbaja, Mairo ta fara takawa, sowa kakeji, kawaayen Mairo yan bariki, suka tayata takawa suka karasa inda su Hajia Aynarh da danginta ke zuwa, Mairo na zuwa ta rungumo Aunty Aynarh, nan aka kaure da rawa Mairo ta kamo hannun Aunty Aynarh tayi suka dunguma zuwa part din Aunty Aynarh, Maama ta sa key ta bude Part din, Aunty Aynarh tayi addua ta shiga da bismillah, MashaAllah nan aka sada Amarya da dakinta, Gidanta yayi kyau matuka, nan yan ganin daki suka dinga shiga dakin one by one.
Aka bar Aunty Aynarh da Aminnanta a daki, sauran kuma suka fito waje, nan aka ci Abinci, mostly Abincin Yarbawa ne, Amala da Ganda, wata Yayar Aunty Aynarh ta ba Dj Disc dinsu na wakokin Yarbawa aka basu fili, Dj ya samusu wakokinsu, nan suka hau juya mazaunai cikin iyawa, nan suka zama abun kallo, kafin Mairo da Kawayenta suma suka shigo fili don baja tasu kolin, daga baya kuma Mairo ta jawo yayanta su Zaineema, Ziyada, Zinatu da Najwa suka shiga Part din Aunty Aynarh suka fito da ita fili suka chashe, Taron Matan yayi sosai, an ci an sha, an gyatse, harda su turmin atamfa da leshi a sourvenirs, nan Yan ZBI ake ta hadama, suna warwaso, Haly Ghana dake rabo tace "ku kwantar da hankalinku, duk zaku samu, akwai da yawa" softie ta kalleta tace "gaskia ba zamuyi inviting dinsu Dinner din anjima ba, dube su da yawa fa su256, ai sai su ba mu kunya" Sholingaye tace "strictly on Invitation ne. Ko sun zo sai dai su tsaya a harabar wurin".
Da Daddare wurin 8 kuma aka dunguma akayi wurin Dinner Party da zaayi a Afficent
Bristol palace inda akayi na su Ziyada, wuri yayi wuri, taro ne har iyaye, bayan kowa ya zauna, Abokan Ango da kawayen Amarya suka shigo ciki, wurin da aka tanada domin su suka nufa suka zauna, nan akayi introducing shigowan Gatan Marayu da Matarsa, da kuma kanwar Ango Zaineea da Mijinta, suma shigowa sukayi a tare, Zaid cikin Rigar Suit Bak'a sai ta ciki fara da bowtie maroon, Ziyada kuma da riga bak'a, da gyalenta black and white.


Daga Bisani kuma akayi sanarwar isowan Amarya da angonta, Abdulmajeed cikin shiga ta Alfarma, Navy blue Suit da skyblue shirt, Najwa kuwa Navy blue wedding gown ne me dogon hannu, da mayafi sky blue, sosai sukayi kyau, cikin tafiyan couples suka iso wurin da aka tanada dominsu, bayan sun zazzauna, aka fara gudanar da dinner, Baba Ado shine ya bude taro da Addua, Welcome speech by Gatan Marayu, Kaveri ta bada takaitacen Tarihin Najwa da turancinta na Indiyawa, Aliyu ya bada takaitaccen tarihin Abdulmajeed, aka ci abinci, aka dan taka, Maama dai bata rawa, Hajia Mairo kam ta chashe, Amaray Aunty Aynarh ma ta dan taka, haka aka ci taro taro ya watse lafiya, abun dai sai wanda yaje ya gani.
*A GURGUJE*
WasheGari da Safe gabaki daya Family din aka hadu a Parlorn Daddy, Paapa ya bude taro da addua, Daddy ya fara da musu gajian biki, kafin ya fara da ""Ammm, Tohm Abdulmajeed a yau ka sake zama Miji, Hak'k'i ya rataya a wuyanka, ba zan gaya maka hakkin matarka kanka ba, amma na san zaka kula ka sauke duk wasu hak'k'unan dake rataye a wuyanka, Abdulmajeed na san ka da Hakuri, na sanka da kawaici da kau da kai, nasan ba zaka bani kunya ba, nasan zaka tayani k'arafafa zumuncina da na danuwana, nasan ba zaka bari ta dalilinka zumuncinmu ya ruguje ba, Abdulmajeed ka kula da Najwa, Abdulmajeed ku zauna lafiya, zaman lafiyanku shine namu kana jina?" Ya dago ya kalleshi yace "Eh Daddy, naji, kuma InshaAllah ba zaku sameni da wani abun da ba daidai ba" Daddy ya maida hankalinshi kan Najwa yace "Najwa, a sanin da na miki ke yarinya ce me kirki da son yanuwanta, na fuskanci kina da hakuri Paapanku ya tabbatar min da haka, amma NAJWA ki sani, aure ya sha bamban da abubuwan da kike gani a talabijin, aure ya wuce soyayyar da kike gani na India, Aure dan zo mu zauna, zo mu saba ne, shauki da soyayyar da kuke ma junanku, ba wai ya na nufin ba zaku sabu sabani ba, aa zaku samu sabani, zaku bata ran junanku, amma hakan be nufin ki dauki waya ki kira maamanki ko mumnynku ki gaya musu, ki rike sirrin gidanki, dana Mijinki, in kun samu sabani ku shirya kanku, kiyi hakuri kinji Najwa? Allah ya baku zaman lafiya da zuri'a Dayyiba".