Sashe 118
Adade Anayi Sai Gaskiya Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haka aka gama cin Abinci, yan matan suka kwashe plates aka kai kitchen, suka wanke, dawo Parlo aka hau fira Iyaye da Yara, maganan Waliman bikin bude Sabon Company din Daddy ake, Daddy yace a bari sai randa aka daura auren Abdulmajeed sai aje chan ayi Walimar" Paapa yace "yauwa hakan ma yayi?" Zaid yace "Yaushe ne?" Paapa yace "sai munje neman auren Aunty Aynarh, randa sukayi fixing date din, rannan zaa daura, sai ayi abun once and for all" Zaid yace "dama Gobe Khaleed zai koma America, akwai Exams din da zai yi a week dinnan, shine yake so a daura musu Aure da Zaineema ya tafi da ita, so by 1am zasu tashi yau" Paapa yace "to sai a daura auren In khalid din ya shirya ko Bayan Laasar ne a masallaci, amma in zaa jira nashi waliyan ne ba matsala, duk yanda yafi mai dai" Khalid ya sadda kai, Abdulmajeed ya zunguro shi yace "kayi magana mana" Khaleed yace "Dama nagaya musu zaa maida auren, sunce tunda ba auren farko bane a daura kawai, kuma goben nake so komawa sabida Exams din" Paapa yace "hakan ma yayi, bayan Laasar sai a maida auren, ke kuma sai ki fara shiri, gobe sai ki bishi ku tafi" raurau Zaineema tayi da ido, bata so tayi missing bikin Yayanta, Maama tace "Yadai Zaineema?" kamar zatayi kuka tace "Banso na barku, yaje dai ya dawo" Maama tace "dont be silly yarinya, ki bi Mijinki, Exams fa kawai zaiyi ku dawo, ki hakuri kinji?" a hankali ta gyada kai.
Bayan Laasar aka daura Auren Khaleed Ishaka Maikudi da Zaineema Abba Abu, bisa sadaki naira 40k wanda Zaid ya bada, Khaleed baki har wuya, a k'afa suka dawo Gida kasancewar masallacin ba nisa. Zaineema ta kulle a dakin Maama kamar auren fari sai kuka take tayi, Ziyada ta shigo tace "ta fito su Daddy na kiranta" kasa tashi tayi, Ziyada tazo ta rungumeta, tana lallashi, "haba sis, meyasa kike kuka? Ya Khalid dinki ne fa, please dont be Sad, ba sabon abu bane, please sis, kuma fa Exams zaiyi ku dawo, please kiyi hak'uri" Zaineema ta gyada kai ta tashi, Ziyada tayi gaba, ta bi bayanta.
Gaban su Daddy ta durkusa ta sadda kanta k'asa. Daddy ya mata nasiha me ratsa zuciya kafin Papa ya dora da cewa "ki tashi yanzu kuje kiyi ma Mahaifiyarki Sallama, yanzu zaku wuce Zaria gun Mahaifan Khaleed, kuyi musu Sallama sannan ku wuce Abuja inda Jirginku zai tashi by 1am" jiki a sanyaye yace da AbdulMajeed "kuje ko?" Abdulmajeed ya mike yace "Zaid, kana ina?" Abdulmajeed ya dinga shiga daki bega Zaid, har kitchen be nan, ba wanda ya ga fitanshi, Papa yace "Oya kuzo ku tafi, ba lokaci" Abdulmajeed yayi gaba, k'annenshi suna binshi a baya" ya waiga yaga Najwa ta choge, be ji dadi ba, ko dai ba su yafe ma Mummynsu bane? Amma ya musu uzuri.
***
Maama da Najwa na shiga dakinta suka ga Zaid la6e bayan k'ofa, Maama ta kalli Najwa, Najwa ta kalleta kafin suka tuntsire da daria a tare, Zaid ya fito daga bayan kofan yana cewa "sun tafi?" Maama tace "hmm, yaro nasan baka son ganin Mairo shiyasa kazo nan ka boye" yasan gaskia ta fada, amma sai ya fara inina yace "aa, Maa, gani nayi ya kamata a barta da 'yayanta, be kamata naje na musu zaune ba, nasan akwai maganganun da ke tsakani uwa da yayanta da zasuyi" tabe baki tayi tace "na jika, amma dole ka cire duk wani abu game da ita, Diyarta kake aure, she wont have you disrespect her Mom" cike da shagwaba yace "Maaa" tace "Yaro ban tashi tare da kai ba, amma ni na haifeka, and nasan deeply inside you kana jin haushin Mairo, don ka samu Yafiyan kowa hakan ba zai sa ka yafe maa farat daya ba, ko tun da chan na san ka da dan banzan rik'on tsiya, balle abunda ka kitsa ma ranka tun kana yaro, da wuya ya fita lokaci guda, so kawai ina ce maka ka bi a hankali" Tabbas abunda ta fada haka yake, ba karya ciki, amma shima har ga Allah yana jin haushin Mairo, duk da yafe mata, amma zuciya bata da k'ashi, baya tunanin zai manta abunda ta mishi da iyayenshi, ba zai taba mantawa, amma for her kids, zai k'okari ya danne asalin abunda yakeji game da ita, har sanda Allah zai sa ya manta komai.
Baki ya turo ya rik'o hannun Najwa tare da fita daga dakin yana cewa"Zokiji Baby" Maama ta san gudun maganar yake shiyasa bata tanka su ba ta dauko wayarta don kiran su Baffa.
"Baby, ki gaya min duk abunda kike so, zan miki kinji, ki tuna waye Yayanki" Murmushi tayi tace "Bhaiyy, ina so ayi min Wedding Partyna a India, kasan all my friends are there, kuma banyi proper farewell dasu, so ina so inje India" yace "Ehen, ina jinki, daya kenan" tace "uhm sai kuma ina son yin Hajj, ban tabayi ba, ban taba zuwa Makka ba, ina so, and then shikenan" yace "are you sure?" tace "Noo Bhaiy, akwai abubuwa da yawa a kaina, amma duk sun shige min, but da na tuna, zan gaya ma kaji??" bude hannuwanshi yayi ta fada a rungumesu yace mata "yana sonta sosai" itama ta bashi tabbacin tana son Yayanta.
Tunda ya zauna yake waya, Umurni kawai yake ba dawa, yana gaya musu yanda yake so a mishi abu da kuma lokacin da yake so a mishi abu. Maama ta shigo dakin Najwa, ta gansu zaune, itama hawa Gadon da suke tayi, lokacin ya gama waya, yace "Maama Gidan Baba Abba na sa aka rushe, akwai wani Gida a gefen gidan, na siya nace shima a rushe a mishi Katon Gida me Part 2, tunda Aure zai sake, kowa da Part dinshi i think hakan zaifi" Maama tace "yauwa hakan yayi, Yaya Yagode" ya cigaba da cewa "and ku kuma--" Maama ta katse shi tace "Ahh, kar ma ka fara tunanin cewa zamu bar gidan nan, don wannan Gida da zufan Babanka ya siyeshi, shi ya bada tsari aka gina mishi shi, ina da tabbacin don danshi shine Gatan Marayu na biyu ba zai bar Gidan nan zuwa ko wani Gida da zaka bashi ba, so kawai ka bar mu a nan, Ina laifin Gida 3bedrooms? Daga ni sai Babanku?" Najwa ta turo baki tace "nifa" Maama tace "kin manta Aure zakiyi? " "kuma dai don zanyi aure, sai ace banda daki a Gidanmu?" Maama ta jawota jikinta tace "Dakinki na nan, ba inda zaije, duk sanda kikazo, you can sleep in your room, amma this house is more than enough for us, Zaid ba sai ka chanza mana Gida ba".
Zaid duk yaji ba dadi, to me zai ma Mahaifanshi? Me zai musu suyi alfahari dashi? Ina amfanin Arzikinshi in Mahaifanshi basuci moriyar shi ba?" kamar ta san tunanin da yakeyi tace "Zaid, babban abun Alfaharinmu shine abunda ka zama yau, muna Alfahari da kai, tunda kowa ya sanka da taimaka ma marayu da gajiyayyu, Zaid kowa ya sanka ta fanni taimako, mun san abubuwan dakayi achieving, i think its more than enough, we are proud of you, we are proud of what you became, kawai dai Allah ya kara maka tsawancin rai ka cigaba da baza legacy din Marigayi Babanka Gatan Marayu na farko, Allah ya kara maka budi da Arziki na Alheri, Allah ya ja kwana, i'm proud of you" fadawa yayi jikin Maamanshi tako rungumeshi, hannu ya bude ma Najwa ta shigo cikin hug dinsu, Ina Sonku 'Ya'Yana Abun Alfaharina, kune Duniyata, ina Sonku fiye da rayuwa da kanta" Paapa ya shigo Dakin, yace "Ohhh, group hug ake shine aka wareni" hawa yayi kan Gadon ya rungumosu gabaki daya yace "Allah ya muku Albarka, ya Albarkaci Rayuwarku" suka amsa da Ameen, Paapa yace "wai su mutanen chan na waje ba sa zuwa hutu ne? Suna waje suna jiranka?" Zaid ya danyi tsaki yace "Wallahi Baba haka suke, ko ina naje suna waje suna jirana, wai kareni suke, yanzu in suka tafi suka barni Faisal naji korensu zaiyi ya kawo wasu, abun haushi yake ban, ko ina mutum zaije fa Convoy" Dariya sukayi gabaki Daya.
Nan suka zauna suna fira gwanin ban shaawa, Zaid na fada musu Plans dinshi suna mai contributing suna bashi shawara, Daddy kadai a parlo yana gyangyadi.
****
Muhsin da Zinatu suka shiga Gidan Aunty Aynarh da gudu, ita kadai ke parlorn sukayi saurin hawa kanta suna mata "Oyoyo" "Iyye, my babies, nayi missing dinku" ta hau daga su one by one, daidai da shigowar AbdulMajeed, Zaineema da Ziyada, "Ashe ku duka kuke tafe" suka amsa da fara'arsu, kafin suka hada baki wurin cewa "Aunty ina wuni?" ta amsa su da fara'arta, ita dai har ranta tana son 'Ya'yan nan, son da take ma Mahaifinsu ne ya shafesu, suka gaisa cike da mutunta juna, AbdulMajeed yace "Aunty, dama Zaineema muka kawo ta muku Sallama, Mijinta ya dawo, jirginsu zai tashi 1am zuwa America, amma Exams kawai zaiyi ya dawo". Tunda ya fara magana Aunty Aynarh ke zabga Murmushi tace "kai madallah MashaAllah, Allah ya sanya Alheri" nan tai ta addua suna amsawa. Mikewa tayi ta shiga ciki don kiran musu Mairo, "Hajia Mairo, ga Yarana sunzo" tsaf ta gane ko su wa take nufi da Yaranta, Hajia Aynarh yar bariki ce, so take ta dinga k'ular da ita ta hanyan kiran 'yayanta, yaranta, inshaAllah ta daina nuna mata haushi ko wani abu takan hakan, don ta hakan take so ta dinga k'ular da ita, indai bariki ne to itama ai ta iya, murmushi ta mata, tace "sunzo gaida uwasu ko? Barinje in gaida yaran Aunty Aynarh" ba ta jira cewar Aynarh ba ta fita daga dakin, ita ko Mamaki ya sa ta bita da budadden baki.
Bayan Laasar aka daura Auren Khaleed Ishaka Maikudi da Zaineema Abba Abu, bisa sadaki naira 40k wanda Zaid ya bada, Khaleed baki har wuya, a k'afa suka dawo Gida kasancewar masallacin ba nisa. Zaineema ta kulle a dakin Maama kamar auren fari sai kuka take tayi, Ziyada ta shigo tace "ta fito su Daddy na kiranta" kasa tashi tayi, Ziyada tazo ta rungumeta, tana lallashi, "haba sis, meyasa kike kuka? Ya Khalid dinki ne fa, please dont be Sad, ba sabon abu bane, please sis, kuma fa Exams zaiyi ku dawo, please kiyi hak'uri" Zaineema ta gyada kai ta tashi, Ziyada tayi gaba, ta bi bayanta.
Gaban su Daddy ta durkusa ta sadda kanta k'asa. Daddy ya mata nasiha me ratsa zuciya kafin Papa ya dora da cewa "ki tashi yanzu kuje kiyi ma Mahaifiyarki Sallama, yanzu zaku wuce Zaria gun Mahaifan Khaleed, kuyi musu Sallama sannan ku wuce Abuja inda Jirginku zai tashi by 1am" jiki a sanyaye yace da AbdulMajeed "kuje ko?" Abdulmajeed ya mike yace "Zaid, kana ina?" Abdulmajeed ya dinga shiga daki bega Zaid, har kitchen be nan, ba wanda ya ga fitanshi, Papa yace "Oya kuzo ku tafi, ba lokaci" Abdulmajeed yayi gaba, k'annenshi suna binshi a baya" ya waiga yaga Najwa ta choge, be ji dadi ba, ko dai ba su yafe ma Mummynsu bane? Amma ya musu uzuri.
***
Maama da Najwa na shiga dakinta suka ga Zaid la6e bayan k'ofa, Maama ta kalli Najwa, Najwa ta kalleta kafin suka tuntsire da daria a tare, Zaid ya fito daga bayan kofan yana cewa "sun tafi?" Maama tace "hmm, yaro nasan baka son ganin Mairo shiyasa kazo nan ka boye" yasan gaskia ta fada, amma sai ya fara inina yace "aa, Maa, gani nayi ya kamata a barta da 'yayanta, be kamata naje na musu zaune ba, nasan akwai maganganun da ke tsakani uwa da yayanta da zasuyi" tabe baki tayi tace "na jika, amma dole ka cire duk wani abu game da ita, Diyarta kake aure, she wont have you disrespect her Mom" cike da shagwaba yace "Maaa" tace "Yaro ban tashi tare da kai ba, amma ni na haifeka, and nasan deeply inside you kana jin haushin Mairo, don ka samu Yafiyan kowa hakan ba zai sa ka yafe maa farat daya ba, ko tun da chan na san ka da dan banzan rik'on tsiya, balle abunda ka kitsa ma ranka tun kana yaro, da wuya ya fita lokaci guda, so kawai ina ce maka ka bi a hankali" Tabbas abunda ta fada haka yake, ba karya ciki, amma shima har ga Allah yana jin haushin Mairo, duk da yafe mata, amma zuciya bata da k'ashi, baya tunanin zai manta abunda ta mishi da iyayenshi, ba zai taba mantawa, amma for her kids, zai k'okari ya danne asalin abunda yakeji game da ita, har sanda Allah zai sa ya manta komai.
Baki ya turo ya rik'o hannun Najwa tare da fita daga dakin yana cewa"Zokiji Baby" Maama ta san gudun maganar yake shiyasa bata tanka su ba ta dauko wayarta don kiran su Baffa.
"Baby, ki gaya min duk abunda kike so, zan miki kinji, ki tuna waye Yayanki" Murmushi tayi tace "Bhaiyy, ina so ayi min Wedding Partyna a India, kasan all my friends are there, kuma banyi proper farewell dasu, so ina so inje India" yace "Ehen, ina jinki, daya kenan" tace "uhm sai kuma ina son yin Hajj, ban tabayi ba, ban taba zuwa Makka ba, ina so, and then shikenan" yace "are you sure?" tace "Noo Bhaiy, akwai abubuwa da yawa a kaina, amma duk sun shige min, but da na tuna, zan gaya ma kaji??" bude hannuwanshi yayi ta fada a rungumesu yace mata "yana sonta sosai" itama ta bashi tabbacin tana son Yayanta.
Tunda ya zauna yake waya, Umurni kawai yake ba dawa, yana gaya musu yanda yake so a mishi abu da kuma lokacin da yake so a mishi abu. Maama ta shigo dakin Najwa, ta gansu zaune, itama hawa Gadon da suke tayi, lokacin ya gama waya, yace "Maama Gidan Baba Abba na sa aka rushe, akwai wani Gida a gefen gidan, na siya nace shima a rushe a mishi Katon Gida me Part 2, tunda Aure zai sake, kowa da Part dinshi i think hakan zaifi" Maama tace "yauwa hakan yayi, Yaya Yagode" ya cigaba da cewa "and ku kuma--" Maama ta katse shi tace "Ahh, kar ma ka fara tunanin cewa zamu bar gidan nan, don wannan Gida da zufan Babanka ya siyeshi, shi ya bada tsari aka gina mishi shi, ina da tabbacin don danshi shine Gatan Marayu na biyu ba zai bar Gidan nan zuwa ko wani Gida da zaka bashi ba, so kawai ka bar mu a nan, Ina laifin Gida 3bedrooms? Daga ni sai Babanku?" Najwa ta turo baki tace "nifa" Maama tace "kin manta Aure zakiyi? " "kuma dai don zanyi aure, sai ace banda daki a Gidanmu?" Maama ta jawota jikinta tace "Dakinki na nan, ba inda zaije, duk sanda kikazo, you can sleep in your room, amma this house is more than enough for us, Zaid ba sai ka chanza mana Gida ba".
Zaid duk yaji ba dadi, to me zai ma Mahaifanshi? Me zai musu suyi alfahari dashi? Ina amfanin Arzikinshi in Mahaifanshi basuci moriyar shi ba?" kamar ta san tunanin da yakeyi tace "Zaid, babban abun Alfaharinmu shine abunda ka zama yau, muna Alfahari da kai, tunda kowa ya sanka da taimaka ma marayu da gajiyayyu, Zaid kowa ya sanka ta fanni taimako, mun san abubuwan dakayi achieving, i think its more than enough, we are proud of you, we are proud of what you became, kawai dai Allah ya kara maka tsawancin rai ka cigaba da baza legacy din Marigayi Babanka Gatan Marayu na farko, Allah ya kara maka budi da Arziki na Alheri, Allah ya ja kwana, i'm proud of you" fadawa yayi jikin Maamanshi tako rungumeshi, hannu ya bude ma Najwa ta shigo cikin hug dinsu, Ina Sonku 'Ya'Yana Abun Alfaharina, kune Duniyata, ina Sonku fiye da rayuwa da kanta" Paapa ya shigo Dakin, yace "Ohhh, group hug ake shine aka wareni" hawa yayi kan Gadon ya rungumosu gabaki daya yace "Allah ya muku Albarka, ya Albarkaci Rayuwarku" suka amsa da Ameen, Paapa yace "wai su mutanen chan na waje ba sa zuwa hutu ne? Suna waje suna jiranka?" Zaid ya danyi tsaki yace "Wallahi Baba haka suke, ko ina naje suna waje suna jirana, wai kareni suke, yanzu in suka tafi suka barni Faisal naji korensu zaiyi ya kawo wasu, abun haushi yake ban, ko ina mutum zaije fa Convoy" Dariya sukayi gabaki Daya.
Nan suka zauna suna fira gwanin ban shaawa, Zaid na fada musu Plans dinshi suna mai contributing suna bashi shawara, Daddy kadai a parlo yana gyangyadi.
****
Muhsin da Zinatu suka shiga Gidan Aunty Aynarh da gudu, ita kadai ke parlorn sukayi saurin hawa kanta suna mata "Oyoyo" "Iyye, my babies, nayi missing dinku" ta hau daga su one by one, daidai da shigowar AbdulMajeed, Zaineema da Ziyada, "Ashe ku duka kuke tafe" suka amsa da fara'arsu, kafin suka hada baki wurin cewa "Aunty ina wuni?" ta amsa su da fara'arta, ita dai har ranta tana son 'Ya'yan nan, son da take ma Mahaifinsu ne ya shafesu, suka gaisa cike da mutunta juna, AbdulMajeed yace "Aunty, dama Zaineema muka kawo ta muku Sallama, Mijinta ya dawo, jirginsu zai tashi 1am zuwa America, amma Exams kawai zaiyi ya dawo". Tunda ya fara magana Aunty Aynarh ke zabga Murmushi tace "kai madallah MashaAllah, Allah ya sanya Alheri" nan tai ta addua suna amsawa. Mikewa tayi ta shiga ciki don kiran musu Mairo, "Hajia Mairo, ga Yarana sunzo" tsaf ta gane ko su wa take nufi da Yaranta, Hajia Aynarh yar bariki ce, so take ta dinga k'ular da ita ta hanyan kiran 'yayanta, yaranta, inshaAllah ta daina nuna mata haushi ko wani abu takan hakan, don ta hakan take so ta dinga k'ular da ita, indai bariki ne to itama ai ta iya, murmushi ta mata, tace "sunzo gaida uwasu ko? Barinje in gaida yaran Aunty Aynarh" ba ta jira cewar Aynarh ba ta fita daga dakin, ita ko Mamaki ya sa ta bita da budadden baki.