Sashe 101
Adade Anayi Sai Gaskiya Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daga bisani ya rada mata a kunne cewa "I'm hungry" a hankali ta janye jikinta daga nashi ta tafi kitchen, plates da serving spoon ta dauko musu, lekawa tayi daki yana tsaye inda ta barshi "Oya dauko Lunch Bag din" dauka yayi suka fito daga parlorn suka isa dining area, ta zage zip din ta fiddo da warmers din, ta bude coolern farko Peppersoup din jan nama ne, dayan kuma hadadden Couscous ne wanda ya ji kanya lambu da hanta, ki samun Peppersoup din da yawa, sai abincin kadan, a plate daban daban tayi yanda yace ta tura mishi gabanshi, ita kuma ta zuba Couscous din da dan yawa, ta sa naman a ciki, harta zauna tayi saurin tashi don dauko ruwa a fridge, tana budewa taga Fruits da drinks kala kala, bata ganin sanda ake kawo duk wani abun amfaninsu, babban roban ruwa ta dauko da wasu Orange drinks din daga kallo kasan foreign ne, ta kai kan table, lokacin Zaid cin Couscous dinshi yake cikin kwanciyar hankali, itama ta fara cin nata, kura mai ido tayi yanda yake cin abincinshi ya burgeta, tana kallon ya ture ya janyo plate din peppersoup din, har zai fara ci ya fasa tare da k'ura ma plate din ido, kamar naman zai yi magana, ta lura da yanayin chanjin fuskar shi, ta dan taboshi tace "Yadai? Lafia? " Murmushi yayi tare da girgiza kai yace "Duk sanda zanci Peppersoup din jan Nama, na kan tuna Babana, yanason Jan Nama, ya san fa yana da Gout amma be fasa ci ba, Doctor ya kirashi ya hanashi, sai yace ya bari ashe in ya dawo Gida yana sa a masu aiki su dafa mishi, da Dr ya gane be daina cin naman ba, sai ya kirani yace in kula da abincin da yake ci, Baba be ji dadi ba da na sani, ina zuwa duk RedMeat din da ke fridge sai da na sa aka fitar dashi a gidan, sai Kaza saboda ban san Kifi shima ya bar ci, wai kinsan me Mutumin nan keyi?" ya tambayeta yana daria, ta girgiza kai itama tana dariar ba wai don tason dariyar me yakeyi ba, ya cigaba yana cewa "Wai sai mutumin nan ya siyo Naman shi ko ya sa Masu aiki su dafa mai amma kar a gaya min, sai yaje bayan k'ofa ya ci abunshi, kullum fa haka yakeyi, har sai da na kamashi redhanded yana ci a bayan kofa, could you imagine, the Whole Alhaji Sadam Audu Gatan Marayu boye bayan kofa yana cin nama a boye?" daria suke gaba daya, bata taba ganin faraarshi ba kamar yau, yanda yake bata labari yana daria tsakaninshi da Allah ita ba wai labarin ya bata daria sosai bane, amma ganinshi cikin annashuwa yasata biye mai tana daria, tace "to ya akayi ya rabu da cin Nama? " Zaid ya tsagaita darianshi yace "Wa? That stubborn Old Man, ai ba zai bari ba, sai da ya kasance indai ya sa a dafa mai sai dai ni na kwace na ci, kullum haka muke, a dafa mai in cinye sai in sa mishi Kaza, wai sai yace be son Kaza, ji yake kamar Dusa, ke har ranar da zai mutu sai da yaci Parpesun kan rago".
Ziyada tace "Allah Sarki, Allah ya gafarta mai ya sa ya huta" Murmushi Zaid yayi ya cigaba da cin Naman, "Matarshi fa? I mean Mamanka" jimm yayi tare da tsagaita taunar naman da yakeyi kafin daga bisani yace "ban taba ganin Matarshi ba" Ziyada da mamaki tace "Bangane ba" a takaice yace "Matanshi ba donAllah suke son shi ba, yana da wani laluri da Mace ba zata iya zama dashi ba, su kance baya iya haihuwa, to duk wanda kika ga ta aureshi, to ba dan Allah bane sai dai don dukiyarshi da abun da ya tara, to tunda muka hadu be sake wani auren ba" kai ta jinjina bakinta na nauyi zatayi magana yayi saurin katseta don ya san me take son cewa, a takaice yace "i'm only his adopted Son, the son he never had, the son he always wished for(Ni Yaron da ya rika ne, nine yaron da be taba samu ba, Nine yaron da ya dade yana son samu) ".. Ya danyi jim kafin yace "My Parents are Dead". Allah sarki, sosai ta tausaya mishi, akwai tambayoyin da take so ta mishi, amma zata share, tace "Ubangiji Allah ya gafarta musu duka, ya sa sun huta, ya sa Aljanna ce makomarsu" ya ansa da Amin, ta chigaba da cewa "akwai hikima babba a taimakon maraya, balle shi wannan Marayu sama da dubu ya inganta rayuwarsu, ya dauke su kamar nashi, ai tashi tayi kyau InshaAllah,sai dai mu roki Allah ya inganta k'abarinshi" Sosai aji dadi da adduointa, yace "Ameen, i'm sure da ya ganki da ya soki, sabida yana son duk wani abun da nake So" blushing ta fara yi a hankali tace "Kana sona?" bata san yaji ba yace "Fiye da tunaninki" kallonta ya cigaba dayi kasa kasa, da sauri ta maida kanta kan plate tana cin Abinci, har suka gama ya tashi ya koma daki ita kuma tayi clearing gun da suka ci Abinci ta danyi kallo a ZeeWorld har wurin to 11 kafin ta kashe ta koma Daki don bacci.
Har ta hau Gado taji shigowarshi, juyawa tayi da sauri kasancewar duhu ne ta kashe Wuta bata ganshi ba, da fitilar wayara ta haka shi, tsaye ta ganshi cikin fararen shorts da top karama, ta dan muskuta tace "Bakayi bacci ba" cikin mintunan da sukayi kama da har abada yace "Erhm Eh banyi ba" ya karaso kan Gadon ya zauna, ta tashi zaune duk da cikin duhu ne amma tana hangenshi, tace "Lafiya? Kaje daki zan kwanta" da sauri yace mata "ina jin tsoro ne" ido a ware tace "Wani irin tsoro kuma?" yace "ba zan iya kwana ni kadai ba, ina tsoron dodo ne ko me ake cewa?" Ziyada ta fahimci ya ma raina mata wayau, ta juya mai baya tayi kwanciyarta tare da jan bargo.
Sosai ya hau kan Gadon, Gabanta ya hau dukkan ukuuku, a bayanta ya kwanta tare da juyo da ita tana fuskantarshi, a kunnenta ya mata rada "Ni Mijinki ne, be kamata ki juya min baya ba kinji?" a hankali ta gyada kai alamun taji, kare matseta yayi yana binta da wasu kauna a jiki, ganin yanda yake matsowa jikinta ne ya sa ta daburcewa jiki na rawa tace "Zanje Makaranta" Murmushi yayi don ya san ta tsorata dashi ne yace "Yanzu zaki makaranta?" da sauri ta gyada kai tace "Gobe" a takaice yace "na cireki" za tayi magana yace "Makarantarki zaki Koma, baze ko? Chan zaki cigaba da karatunki bata iya amsa shi ba, ta mayar da idanunta ta rufe.
A nutse yake nuna mata yanda yake jinta a zuciyarshi, cikin kwanciyar hankali yake nuna mata yanda soyayyarta tai mishi illa batare dayai amfani da kalamai ba. Cikin kwanciyar hankali yake hade zuciyoyinsu da ruhinsu waje daya cikin salon da bazai mantu a wajen su ba har abada.
***
*Bayan Wasu yan Kwanakin da ba su kai Sati ba*
Soyayya, Aminci da Shakuwa ta darsu a cikin zuciyoyin masoyan nan biyu, burin daya ya kyautata ma daya, a zaman da sukayi da juna sun fahimci halaiyar junansu, sun sake da junansu, sabida Kwanciyar hankali Zaid ya kashe wayoyinsa don samun hutu, shi fita kasashe bude ido be dameshi ba, niyyarshi ya dauketa su tafi chan Porthacourt su danyi hutu ba tare da hayaniya ba, a yanzu ne Zaid yasan cewa ya dade yana cikin bakin duhu, a yanzu ya san cewa akwai wani abu So, a yanzu ya san cewa mutum na zama da tsana da bakinciki a ranshi in yaso, in ko ya so cirewa zai cire ya musanya da So, Allah ne shaidarshi yana son Ziyada, yana son kyautata mata kamar yanda take kyuatata mishi, shiyasa jiya da daddare da ta zo mai da bukatar suje Gidansu be ce komai ba, amma duk da baya so, ba zai hana ba, dole ya hakura suje Gidan, wurin breakfast ya gaya mata ta shirya anjima su tafi, dadi ya kamata, ta tashi ta rungimeshi tana mai godia breakfast din da basu gama ba kenan.
**
Aunty Aynarh ta shigo Gidan da Sallama, duk yaran su ka tashi suka rungumeta, fara'a take tayi, ta zube kasa ta gaida Hajjo, Daddy baki har wuya yaga Masoyiya, a mutunce aka gaisa, Mummy sai famar wurga mata harara take ko a jikinta, ta kalle su tace "Allah ya sa ba ku daura abincin Rana ba, na riga na mana Lunch" Zaineema ta murmusa tace "ba mu daura ba ko" tace "yauwa perfect" Key ta mik'a ma Abdulmajeed tace "Ka dauko Kayan Booth" Abdulmajeed ya karba ya kalli Najwa yace "muje ki tayani dauko kaya" tashi tayi ta bi bayanshi suka bar Parlorn, Mummy ta kalli Daddy tace "bari in daura mana Abinci kafin yara su fara jin yunwa" Daddy yace "Maryam bakiji Hajia Aynarh tace ta yo abinci damu ba?" Galala ta kalleshi, kwana biyun nan tsinkata yakeyi gaban jamaa, kar ya mata haka yanzu ta wayance tace"wai sai a kara ko?" Daddy yace "Aa, am sure Abincin da yawa, ki bari da daddare ayi, yanzu dai muci wannan" zama tayi tana wurgar Hajia Aynarh da harara, ita ko hararar mugunta take mata.
"PureHeart, i cant wait naga su Maama don nace su bani ke na aura" Murmushi tayi tace "suna nan tafe cikin kwanaki" yace "Allah ne shaidana, ina sonki dominsa" Murmushi tayi tace "main tumase karta hoon" idonshi ya juya sama cikin salon banji me kikace ba, tayi daria tayi gaba, ya bi bayanta yace "Nidai a bar min magana da Indiyanci" dariya tayi tace "Aunty Aynarh na jira" ya bude Booth ya fiddo kayan ciki duka har su carpet, plates da cups, sai Flask kusan kala uku, suka dau iyakan iyawansu suka kai ciki, suka dawo suka dauka sauran.
Ziyada tace "Allah Sarki, Allah ya gafarta mai ya sa ya huta" Murmushi Zaid yayi ya cigaba da cin Naman, "Matarshi fa? I mean Mamanka" jimm yayi tare da tsagaita taunar naman da yakeyi kafin daga bisani yace "ban taba ganin Matarshi ba" Ziyada da mamaki tace "Bangane ba" a takaice yace "Matanshi ba donAllah suke son shi ba, yana da wani laluri da Mace ba zata iya zama dashi ba, su kance baya iya haihuwa, to duk wanda kika ga ta aureshi, to ba dan Allah bane sai dai don dukiyarshi da abun da ya tara, to tunda muka hadu be sake wani auren ba" kai ta jinjina bakinta na nauyi zatayi magana yayi saurin katseta don ya san me take son cewa, a takaice yace "i'm only his adopted Son, the son he never had, the son he always wished for(Ni Yaron da ya rika ne, nine yaron da be taba samu ba, Nine yaron da ya dade yana son samu) ".. Ya danyi jim kafin yace "My Parents are Dead". Allah sarki, sosai ta tausaya mishi, akwai tambayoyin da take so ta mishi, amma zata share, tace "Ubangiji Allah ya gafarta musu duka, ya sa sun huta, ya sa Aljanna ce makomarsu" ya ansa da Amin, ta chigaba da cewa "akwai hikima babba a taimakon maraya, balle shi wannan Marayu sama da dubu ya inganta rayuwarsu, ya dauke su kamar nashi, ai tashi tayi kyau InshaAllah,sai dai mu roki Allah ya inganta k'abarinshi" Sosai aji dadi da adduointa, yace "Ameen, i'm sure da ya ganki da ya soki, sabida yana son duk wani abun da nake So" blushing ta fara yi a hankali tace "Kana sona?" bata san yaji ba yace "Fiye da tunaninki" kallonta ya cigaba dayi kasa kasa, da sauri ta maida kanta kan plate tana cin Abinci, har suka gama ya tashi ya koma daki ita kuma tayi clearing gun da suka ci Abinci ta danyi kallo a ZeeWorld har wurin to 11 kafin ta kashe ta koma Daki don bacci.
Har ta hau Gado taji shigowarshi, juyawa tayi da sauri kasancewar duhu ne ta kashe Wuta bata ganshi ba, da fitilar wayara ta haka shi, tsaye ta ganshi cikin fararen shorts da top karama, ta dan muskuta tace "Bakayi bacci ba" cikin mintunan da sukayi kama da har abada yace "Erhm Eh banyi ba" ya karaso kan Gadon ya zauna, ta tashi zaune duk da cikin duhu ne amma tana hangenshi, tace "Lafiya? Kaje daki zan kwanta" da sauri yace mata "ina jin tsoro ne" ido a ware tace "Wani irin tsoro kuma?" yace "ba zan iya kwana ni kadai ba, ina tsoron dodo ne ko me ake cewa?" Ziyada ta fahimci ya ma raina mata wayau, ta juya mai baya tayi kwanciyarta tare da jan bargo.
Sosai ya hau kan Gadon, Gabanta ya hau dukkan ukuuku, a bayanta ya kwanta tare da juyo da ita tana fuskantarshi, a kunnenta ya mata rada "Ni Mijinki ne, be kamata ki juya min baya ba kinji?" a hankali ta gyada kai alamun taji, kare matseta yayi yana binta da wasu kauna a jiki, ganin yanda yake matsowa jikinta ne ya sa ta daburcewa jiki na rawa tace "Zanje Makaranta" Murmushi yayi don ya san ta tsorata dashi ne yace "Yanzu zaki makaranta?" da sauri ta gyada kai tace "Gobe" a takaice yace "na cireki" za tayi magana yace "Makarantarki zaki Koma, baze ko? Chan zaki cigaba da karatunki bata iya amsa shi ba, ta mayar da idanunta ta rufe.
A nutse yake nuna mata yanda yake jinta a zuciyarshi, cikin kwanciyar hankali yake nuna mata yanda soyayyarta tai mishi illa batare dayai amfani da kalamai ba. Cikin kwanciyar hankali yake hade zuciyoyinsu da ruhinsu waje daya cikin salon da bazai mantu a wajen su ba har abada.
***
*Bayan Wasu yan Kwanakin da ba su kai Sati ba*
Soyayya, Aminci da Shakuwa ta darsu a cikin zuciyoyin masoyan nan biyu, burin daya ya kyautata ma daya, a zaman da sukayi da juna sun fahimci halaiyar junansu, sun sake da junansu, sabida Kwanciyar hankali Zaid ya kashe wayoyinsa don samun hutu, shi fita kasashe bude ido be dameshi ba, niyyarshi ya dauketa su tafi chan Porthacourt su danyi hutu ba tare da hayaniya ba, a yanzu ne Zaid yasan cewa ya dade yana cikin bakin duhu, a yanzu ya san cewa akwai wani abu So, a yanzu ya san cewa mutum na zama da tsana da bakinciki a ranshi in yaso, in ko ya so cirewa zai cire ya musanya da So, Allah ne shaidarshi yana son Ziyada, yana son kyautata mata kamar yanda take kyuatata mishi, shiyasa jiya da daddare da ta zo mai da bukatar suje Gidansu be ce komai ba, amma duk da baya so, ba zai hana ba, dole ya hakura suje Gidan, wurin breakfast ya gaya mata ta shirya anjima su tafi, dadi ya kamata, ta tashi ta rungimeshi tana mai godia breakfast din da basu gama ba kenan.
**
Aunty Aynarh ta shigo Gidan da Sallama, duk yaran su ka tashi suka rungumeta, fara'a take tayi, ta zube kasa ta gaida Hajjo, Daddy baki har wuya yaga Masoyiya, a mutunce aka gaisa, Mummy sai famar wurga mata harara take ko a jikinta, ta kalle su tace "Allah ya sa ba ku daura abincin Rana ba, na riga na mana Lunch" Zaineema ta murmusa tace "ba mu daura ba ko" tace "yauwa perfect" Key ta mik'a ma Abdulmajeed tace "Ka dauko Kayan Booth" Abdulmajeed ya karba ya kalli Najwa yace "muje ki tayani dauko kaya" tashi tayi ta bi bayanshi suka bar Parlorn, Mummy ta kalli Daddy tace "bari in daura mana Abinci kafin yara su fara jin yunwa" Daddy yace "Maryam bakiji Hajia Aynarh tace ta yo abinci damu ba?" Galala ta kalleshi, kwana biyun nan tsinkata yakeyi gaban jamaa, kar ya mata haka yanzu ta wayance tace"wai sai a kara ko?" Daddy yace "Aa, am sure Abincin da yawa, ki bari da daddare ayi, yanzu dai muci wannan" zama tayi tana wurgar Hajia Aynarh da harara, ita ko hararar mugunta take mata.
"PureHeart, i cant wait naga su Maama don nace su bani ke na aura" Murmushi tayi tace "suna nan tafe cikin kwanaki" yace "Allah ne shaidana, ina sonki dominsa" Murmushi tayi tace "main tumase karta hoon" idonshi ya juya sama cikin salon banji me kikace ba, tayi daria tayi gaba, ya bi bayanta yace "Nidai a bar min magana da Indiyanci" dariya tayi tace "Aunty Aynarh na jira" ya bude Booth ya fiddo kayan ciki duka har su carpet, plates da cups, sai Flask kusan kala uku, suka dau iyakan iyawansu suka kai ciki, suka dawo suka dauka sauran.