← Book details Adade Anayi Sai Gaskiya Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 127 OF 128

Sashe 127

Adade Anayi Sai Gaskiya Complete Hausa Novel · about 7 min read

Suprise suka mata,  sai dai ganinsu tayi sunyi diran Mikiya,  Ihu ta sa ta hau rungumesu,  Najwa tace Didi ashe kema kinyi nauyi" hararrasu tayi tace "kema cikin gareki" tace "wallahi banda komai" tace "ahap mu dai zuwa" sukayi daria,  nan Abdulmajeed da Zaid suka shigo Khalid na musu Jagora,  Zaineema ina zata sakasu don jin dadi,  yanuwanta sun kawo mata ziyara,  dadi kamar ya shideta.
Abdulmajeed yace "Khalid,  are you busy?" Khalid yace "Haba Aa why? " Zaid yace "Aron Lokacinku zaku bamu kai da matarka" Khalid yayi zaton wani abu ya faru ya tattaro hankalinshi yace "ina fatan lafia" Zaineema taji gabanta ya fadi,  Abdulmajeed yace "Relax kuzo muje" ya mik'e ya tashi,  duk suma suka m'ike,  suka fita, suka shiga Mota,  Driver yaja, mota uku sukayi,  Zaineema    sai dai ta kalli Khalid shima ya kalleta suna son k'arin bayani.

Wurin wani K'atoton Mall suka yi Parking me dauke da *ZEEMA SUPERMARKET AND BEAUTY SPA SALON* suka firfito,  suna tunanin me suke a wurin,  wannan k'aton ginin, su kan wuce wurin ita da Khalid tunda hanyansu ne,  kuma ta na ganin wurin da ba a dade da fara gina shi ba,  tace "Dee,  dube ginin nan,  wai har an gama kamar an ma fara aiki a ciki" Khalid yace "Ahap,  ai na ce miki daga gani wani Maikudin ke gina wurin" ya kalli su Zaid yace "wurin fa ko two weeks baayi ba muka ga an fara ginashi, wai har an gama" Zaid ya kalli Abdul suka ma juna murmushi, ko Najwa sai dai ta kalli Ziyada duk basu san meye ba,  Zaid ya kama hannun Ziyada da tayi nauyi sosai haihuwa yau ko gobe,  ya kalle su yace "to mu shiga ko?" Zaineema tacw "Allah Sarki,  shopping ku ka kawoni, aikam wallahi Dee yau zanyi ma babyna siyayya" Abdulmajeed yace "Its Yours" ta dan kkalleshi bata gane me yake nufi ba tace "What?" Zaid yace "Naki ne Sister" ta kalli Abdulmajeed ta kalli Zaid tace "Wai mene?" Abdulmajeed ya nuna duka ginin yace "All of it Sis,  its yours,  kece mamallakiyan Zeema Supermarket,  allofi it" Waiyo Allah dadi yasa Zaineema hawaye,  ta kalli Mijinta shima farincikin yake tayata,  me zatayi?  Bata sani ba,  dadi ji take kamar ta fara nakuda yanzu,  ta kalli Zaid tace "Me zan ce muku?" Zaid ya nuna Abdulmajeed yace "It was all him, Filinshi ne,  shi ya zana, ya sa a ka gina" Abdulmajeed  yace "Kayan cikin kuma Zaid ya sa akayi ordering dinshi daga Dubai,  da kayan cikin da Maaikatan cikin duk Zaid ne" Hawaye take na farinciki, su Ziyada suka rungumeta suna tayata murna,  Khalid ya musu godia Zaid yace "Haba Maikudi,  don munyi ma kanwarmu kyauta sai kace zaka gode mana" Khalid yace "dole kam, farincikin Zaineenah,  nawa ne,  mungode Allah ya kara  girma" suka amsa da Ameen,  Zaineema kasa daurewa tayi saida ta rungume Abdulmajeed.
Nan suka shiga ciki aka nuna musu ko ina da ko ina,  kuma akayi  introducing maaikata wurin Mai wurin wato Zaineema Abba Abu..

A ranar suka koma Abuja,  kamar jira ake,  da daddare Ziyada tafara Nak'uda,  Zaid ya kira Abdulmajeed a waya,  don shi ya tsorata sosai,  Najwa ya tada da ta fara bacci, a rude suka fito suka nufa Gidan Zaid,  sun iskeshi yana waya da Maama inda tace su kaita asibiti,  zata turo musu adduar nakuda a karanta a bata cikin ruwa tasha,  tsam Zaid ya dauke Ziyada ya fita da ita,  Abdulmajeed ya dauko ruwa a cup ya tofa adduar da mama ta mai texting, daidai bakin ziyada ya kafa kofin,  ta sha dukda tana cikin wahala,  wani Private Hospital a ka kai Ziyada,  cikim ikon Allah ta suntulo yaronta Namiji.

Bayan an kimtsata aka maidata daki, Zaid suka shiga, hannu na rawa ya karba babyn, dagowa yayi ya kallo Abdulmajeed suka sakar ma Juna murmushi Abdulmajeed yace "Ka kira mishi Adhan(Kiran Sallah) ka mishi huduba" wani farinciki Zaid keji da ya rungume danshi a k'irjinshi, yana sonshi da duk wata numfashin da yake, ya dago dan wurin fuskarshi ya mai kiran Sallah, ya mai huduba, ya dago Abdulmajeed yace "let us guess, ka maida sunan Gatan Marayu ko?" Zaid ya Jinjina kai yace *"SADAM ZAID SADAM"* suka hada baki wurin cewa Allah ya rayashi, nan suka karbeshi, Ziyada kuwa ta samu bacci.
A cikin daren labarin Haihuwan Ziyada ya zagaya Yanuwa da Dangi.
WasheGari kam suka fara ganin yan Barka, Zaineema ta ruga Yan Kano suka isowa.
A ko wani Headline na News da Internet sanarwan samun k'aruwan Gatan Marayu ne....

Bayan wasu Watanni.
Zaineema ta haifi Yanbiyu, Hassanar taci sunan Uwar Khalid wato Aisha duk da ita Zaineeman nacewa ita Maamanta tama takwara asalin sunanta kenan, Hussainar kuma taci sunan Mummy wato Maryam saidai muce Allah ya sa kar tayi halin Grandmoza.

Ba da jimawa Aunty Aynarh ta haifi diyarta Mace, inda taci sunan Hajjo wato Hajara, Randa Aunty Aynarh ta haihu, kuka take wiwi don bata taba haihuwa ba, ko don bata taba kwantar da hankalinta tayi zaman aure ba? Aa rabo ajali, Allah yayi a Gidan Alhaji Abba zata haihu.
**
Shekara Kwana
Sadam na da Shekara 1 da rabi Allah ya Azzurta Najwa da samun diya Mace, ranar suna yarinya taci sunan Maamansu wato Aishatu Yesmin.

Bayan wasu Watannin da basu kai Shekara ba.
Hutu suka samu Abdulmajeed da Zaid suka yanke hukuncin zuwa Paris yawon bude ido da Iyalansu.
Ayshatu Yesmin ta fara rarrafe, Sadam kuwa ya zama bigboy, yana magana ya na da farin jini, yaron kowa yaganshi sai ya dauka, a wurin da sukaje shakatawa wuri kamar Park, Sadam ya faki ido ya k'ara gabanshi, wata Mata ta daukeshi tace "Hello Boy, whats your name?" yace "Sadam Zaid Sadam" matar ta zaro ido tace "Wheres your Daddy?" da yake beyi nisa dasu ba, da hannu ya nuna mata inda Su Daddynshi ke zaune, da sauri ta karasa gunsu Sadam na dauke a hannunta, sallama ta musu, Zaid ya mik'e yace "Na'ilah" ta murmusa tace "Ina wuninku" Najwa ta ganeta, Abdulmajeed ya amsa gaisuwan, ta kalli Ziyada tace "baku ganeni ba ko?" Abdulmajeed yace "kanwar Nura Kurma" sukayi daria, tace "Well, ashe zaku ganeni" karban Ayshatu Yesmin tayi daga hannun Ziyada tace "Wow, Allah ya sa Alheri" Zaid dauke da expression na tausayi, yasan Naeela na sonshi, ya san har yanzu tana sonshi yace"Naeela, how have you been?" ta dan murmusa tace "Good, i can see you are good also" ya gyada mata kai yace "Are you?" tace "Married? No banyi aure ba, amma zanyi dana koma Nigeria next month" Zaid ya saukar da ajiyam zuciya da yaji zatayi aure yace" Allah ya sa Alheri, kar ki manta ki gayyaceni in lokaci yayi tace "InshaAllah" ta kalli Ziyada tace "Your son is very brave, tell him about his Aunt Na'ilah in ya girma" murmushi Ziyada ta mata tace "InshaAllah" Sallama ta musu ta juya ta tafi.

Zaid duk yayi wani iri, be son Naeela, be taba sonta ba, amma yaji tausayinta, ya san ta so shi, jikinshi yayi sanyi ya kalli Najwa da ke zaune, yace "Baby je kamo Sadam kafin ya kara gaba" ta tashi ta chapkoshi, Ziyada ta lura da Zaid, ko kadan bata so taga ya shiga damu tayi tunanin sashi daria Mikewa tayi ta isa inda yake zaune, ta dagoshi, tace "kaga dai my Forever ka bar cema Matar YaMaji Baby, tun ina kauda kai, ina kawaici, kai baka gani ko? Har yanzu baka fasa ce mata Baby ba ko?" murmushi ya sakar mata yace"Ita fa yar baby ce in ba kya so sai a ce mata yarinya, ke kuma kece Babe, the one and only one Babe, My Forever, My Pure Heart" Abdulmajeed ya tashi da sauri hannunshi rike da Ayshatu Yesmin yace "No, No, ka kira matarka da ko wane suna banda PureHeart, i'm the originator of that name, nikuma kadai ke da lasisin amfani da sunan" Zaid ya dago kai yace "ko dadi ma, MyForever, an bar cema wata Baby, yarinya zaa dina ce mata, you are my one and only one Babe, and i love you".

Najwa tace "Meri Jaan, sharesu, their jealous of us, Tumase pyar kharta hoon" Zaid yace "oho dai bamu san me kikace ba, Abdulmajeed yace "wanda ta fada dominshi ya sani, au tumase bahoot pyar kharta hoon PureHeart"..

Armstrong da ke tsaye yana kallonsu yace "Group Picture?" Zaid yace "Oh Yes Arm" ya karbe Ayshatu Yesmin daga hannun Abdulmajeed yace "Zo nan Mamana"Abdulmajeed ya dauki Sadam, tare da rungumo Najwa ta gefe, itama Ziyada ta rankwafo wurin Zaid, Arm ya dinga daukansu Hotuna.

Bayan Shekara Uku
Chapter 127 · 0% Book details