Sashe 102
Adade Anayi Sai Gaskiya Complete Hausa Novel · about 7 min read
Carpet din suka shimfida a tsakar Gidan, suka jera komai a kai, sai da sukayi Sallahr Azahar suka fito waje kan Carpet din, daidai nan Ziyada ta shigo Gidan da Sallama, duk sukayi kanta suka yayyabeta suna murnan ganinta, Oyoyo Oyoyo, daga baya Zaid ya shigo, baki Mairo ta washe, shi kuwa kamar an aiko mai da Sakon mutuwa, faraar fusakrshi ya dauke dif, Abdulmajeed a karaso gunshi ya mika mai hannu don suyi musabaha, ba yabo ba fallasa ya karba, tare da dan durkusawa ya gaida da Daddy da Hajjo da Aunty Aynarh da ke zaune kan Carpet, duk ya bi yaran gidan da kallo inda suke gaisheshi, tausayinsu ya kamashi, Zaineema yarinyar da yaso kamar me, be manta kaunar da ke tsakaninsu ba, yarinyan da Mairo ke rankwashinshi in ya dauketa, rashin imaninshi ya sa ya rabata da Mijinta, ya zaiyi ya gyara mistake dinnan? Idonshi ya kaiga Najwa wanda take wurga mishi wani mugun kallon "na san ko waye kai" da sauri ya dauke kai yana me jin tsoronta, kar fa ta ganeshi, kar ta tona mai asiri Ziyada a rabu dashi, Allah sa bata ganeshi ba, ji muryar Mairo yayi tana cewa "Ku shigo Parlo sannunku da zuwa" Ziyada tace "Aa Mummy, bari mu zauna a nan so kike ayi picnic din banda mu?" Mairo ta tabe baki tace "ba wani picnic, dangin yarbawa ce tayi son iyawanta wai ta dafo mana Abinci, kamar munce ba mu da abinci". Ziyada tace "Yayy, dama nayi missing Abincin Aunty Aynarh" Mairo takaici kamar ya shideta, tace "Alhaji Zaid kai ka shigo Parlo ka zauna" banza yayi da ita, ba wanda ya lura da ko gaishe da Mairo beyi ba, ya samu wuri kusa da AbdulMajeed ya zauna, wanda Hajjo ke gefenshi Najwa na nata gefen, Mairo tace "Lah, Alhaji, zaman kasa be kamace ka na, please ka shigo ciki" ko kallo bata isheshi ba, Daddy yace "Maryam ki barshi ya zauna cikin Yanuwanshi mana"
"'Yanuwanshi" kalmar da Zaid ya fada kenan, ya kalli gefen shi ya ga su Hajjo da Muhsin da Zaineema zaune, dayan gefen Daddy da AbdulMajeed da Zinatu da Ziyada a zaune, sai ya ji shi kamar daya daga cikinsu, ba abunda ya kai bond din Yanuwan jini karfi, ba abunda ya kai feeling din dadi, tabbas yaji wannan connection din, ya ji shi among them, ko yaki ko ya so "they are his Family" yayi Alkawarin gyara laifinshi, "I will fix this , i will fix everything " ya fada a ranshi..
Daddy yace "Oya a bamu mu ci" Hajia Aynarh tace "ai ga yara na nan, su zuba mana" Mairo kamar ta mutu ganin yanda Hajia Aynarh ke fi'ili gaban Daddy.
Zaineema ta bude kulolin, Faten Wake da Amala, duk wanda kake so sai a sa maka, Miyar Amalan yaji Ganda da Stock fish, Alallen kuwa ya hadu da kwai da kifin Sardine, Faten waken ma yaji dryfish da Ganda.
Tace "Daddy me zaa sa maka? Hajjo me zaki ci?" tace "a zubo min Faten Wake, mun dade bamu hadu ba" akayi daria, Daddy yace "a zuba min Amala" Mummy fa baki ta yatsina tace "Moimoi".
Ziyada tace "YaMaji me zakici?" ya tashi daga durkuson da yayi yace "Zuzu serve your Husband, ni da kaina zan zuba abinci na" Hajia Aynarh tace "banda abunki Ziyada ana ta Miji wake ta wani YaMaji".
Ta k'asa ta kalli Zaid din da yayi mugun dauke kai, yana iya cin Abincin Musamman da yaji cewa ba Mairo tayi shi ba, Hajia Aynarh tayi, kuma yana iya cin Amala, don yana son abincin, ita kuma bata yi zaton zaici ba shisa bata tambayeshi ba, a hankali suka hada ido yace mata "Amala" Ziyada ta murmusa, Najwa tace ita kuma a bata irin na Hajjo ba wai don ta san meye ba, amma don yayi kama da wani soup din India, kowa ya fadi abunda zaici akayi serving kowa..
Addua Daddy ya umurta ayi, a tare kowa yayi suka fara cin Abinci, kasancewar duk Abinci da busasshen kifi da kuma gasasshen kifi akayi, in ba ci kayi ba ba zaka gane kifi bane, yafi kama da Nama.
Ko Cokali biyu ba suyi ba numfashin Zaid da Najwa ya fara daukewa, sama sama Numfashin ya fara, AbdulMajeed da ya kafa Najwa da ido ya lura da abunda takeyi yayi saurin ajiye spoon yace "PureHeart are You OK?" Zaineema ta kalli Najwa tayi saurin mikewa tsaye Hajia Aynarh ma haka, Najwa me ya faru? Abu takeyi kamar mai neman shidewa, Ziyada ta dan waiga ta kalli Zaid, gabanta ya fadi, irin abun Najwa yakeyi, numfashin shi samasama, fuskarshi yayi ja, da sauri ta karasa gunta "My Forever, lafiya" Hankalin Mairo ya tashi ta mike ta ci kwalar Aunty Aynarh "Munafuka Algunguma, me kika sa ma Abinci? Me kika sa ma sirikina? So kike ya mutu" Aunty Aynarh ta tsure sosai tana girgiza kai tace "Wallahi bansa komai ba, Wallahi ba abunda na sa, mukai su Asibiti" Najwa ta riko hannun Hajjo tana bankarewa kamar zata mutu, Zaid ma hannu ya sa ya rike wuyanshi yana jan numfashin dake fita da kyar, fuskar nan tayi Ja, Daddy yayi saurin fita don taro A daidajta sahu a kaisu Asibiti, yana fita ya ci karo da Convoy din Zaid, Ziyada Hawaye kawai takeyi hankalinta tashe, Abdulmajeed hankali a tashe ya kalli Aunty Aynarh yace "Aunty kinsa Kifi a abincin nan?" da sauri ta gyada kai tace "duka abincin da Kifi nayi shi" Abdulmajeed ya ruga kitchen a guje, Ya shiga bincikar Kayan Miya da ya siyo dazun Tomatoes ya dauko, ko wankewa beyi ba ya fito ya mika ma Ziyada 1 yace ki bashi, lokacin sun fara fita daga hayaccinsu, fasawa yayi da bakinshi ya juye ma Najwa ruwan tumatirin a baki, haka Ziyada ta ma Zaid, a hankali a hankali numfashin su ya fara dawowa daidai, daidai nan Idi da wasu Yaran Zaid suka shigo sukayi kan Zaid wai zasu kaishi Asibiti, daga musu hannu yayi yace "i'm fine" Ziyada tace "me ya faru da kai?" Zaid yace "ina tsammanin Abincin nan akwai Fish, and i'm allergic to Fish" daidai lokacin da Najwa ta ke ce ma Hajia Aynarh "Dama bansan da kifi a cikin Abincin ba, shine naci?" Hajia Aynarh tace "I'm So Sorry, wallahi bansan ba kwa son Kifi ba, Abincin ba wanda ban sa Kifi ciki ba, kuyi hakuri donAllah" Najwa tace "Laah Aunty ba wani abu, ni in na samu irin attack dinnan da na sha tomato zanji normal, ai farkon zuwana Nigeria na taba samun attack din" Abdulmajeed yace "shiyasa na tuna Tomato ne first Aid treatment din" Zaid ya kira Idi ya zo kusa dashi, ya rada mai abu a kunne, da sauri ya fita, Aunty Aynarh duk tayi wani iri, gani take laifinta ne, Zaid ya kalle su Daddy da sukayi cirko cirko suna kallonsu yace "Baba Abba ku zauna ku cigaba da cin Abincinku, Ni kifin ne bana so, yanzu zaa kawo min wani Miyan sai in ci" Daddy ya sage yana kallon Zaid, wani abu ke bin zuciyanshi, dunia Zaidun Sada kadai ke ce mishi "Baba Abba" jiki a sake ya zauna, yace da Muhsin su cigaba daci, Daddy ya kallesu yace "sai kuka tuna min da k'anina Marigayi, kunsan shi ko kanshi Kifi ya ji sai ya fara sheshek'a?" Hajjo ta chabe tace "haka ne, ko abinci nayi da Man kifi in ya fara Amai kamar zai zazzago kayan cikinsa" Zaid ya runtse idonsa yana tausar zuciyarsa. Abincinsu su ka cigaba daci banda su 3, Zaid da Najwa da Mummy, su kadai ne basu cin Abincin, gaban Mairo ke dukan uku uku, ta kalli Najwa a kalli Zaid, tunanin da bata son yi ta fara yi, Sada be cin Kifi, Zaid din Sada be cin Kifi, Wannan dan Sada ne. Da sauri ta girgiza kanta ta tashi kamar mahaukaciya ta shige daki, daidai nan Idi yayi Sallama da Cooler a hanayensa, Gaban Oganshi ya Dire, Ziyada ta bude Miyan Kubewa danya ne da yaji Jan Nama, ta bude wani Amalan ta sa mai da miyan Kubewar, ta kalli Najwa tace "in sa miki ko? " kai Najwa ta daga, Ziyada ta zuba mata suka cigaba da ci, Hajia Aynarh ta saukar da Ajiyar zucia ganin basuyi zargin ko tayi poisoning dinsu bane.
I N D I A
Duk wasu Process na tafia sun gama, Jirginsu zai tashi Gobe zuwa Dubai, washegari su tafi Nigeria inda zasu isa Lagos daga nan suyi Kano, Paapa da Maama sunyi Resigning a wuraren Aikinsu, an basu kudin Sallama me tsoka, harta Motocinsu da Gidan da suke zaune sun saida, Paapa ya samu wani Agent dan Kano suna communicating, nan ya tura mishi kudi ya siya mishi dankareren Gida a Tarauni, don shi baya tunanin zai koma Gidanshi na da, yafi karfin ya tada Yayanshi a gidan da yake, ya bar mai Gidan nan har abada, Maama ta dinga shiga Gidajen Neighbors dinsu tana musu sallama, Vijhay Bhaiya yayi kuka sosai, Maama tace "InshaAllah zasu zo wani lokacin" bayan sun mishi Alheri me yawa, ko da ta shiga Gidansu Kaveri nan suka bata lokaci da Maman kaveri suna jimamin rabuwansu, Kaveri kuwa bata fito ba tana daki tana cizgar Kuka.
N I G E R I A.
"'Yanuwanshi" kalmar da Zaid ya fada kenan, ya kalli gefen shi ya ga su Hajjo da Muhsin da Zaineema zaune, dayan gefen Daddy da AbdulMajeed da Zinatu da Ziyada a zaune, sai ya ji shi kamar daya daga cikinsu, ba abunda ya kai bond din Yanuwan jini karfi, ba abunda ya kai feeling din dadi, tabbas yaji wannan connection din, ya ji shi among them, ko yaki ko ya so "they are his Family" yayi Alkawarin gyara laifinshi, "I will fix this , i will fix everything " ya fada a ranshi..
Daddy yace "Oya a bamu mu ci" Hajia Aynarh tace "ai ga yara na nan, su zuba mana" Mairo kamar ta mutu ganin yanda Hajia Aynarh ke fi'ili gaban Daddy.
Zaineema ta bude kulolin, Faten Wake da Amala, duk wanda kake so sai a sa maka, Miyar Amalan yaji Ganda da Stock fish, Alallen kuwa ya hadu da kwai da kifin Sardine, Faten waken ma yaji dryfish da Ganda.
Tace "Daddy me zaa sa maka? Hajjo me zaki ci?" tace "a zubo min Faten Wake, mun dade bamu hadu ba" akayi daria, Daddy yace "a zuba min Amala" Mummy fa baki ta yatsina tace "Moimoi".
Ziyada tace "YaMaji me zakici?" ya tashi daga durkuson da yayi yace "Zuzu serve your Husband, ni da kaina zan zuba abinci na" Hajia Aynarh tace "banda abunki Ziyada ana ta Miji wake ta wani YaMaji".
Ta k'asa ta kalli Zaid din da yayi mugun dauke kai, yana iya cin Abincin Musamman da yaji cewa ba Mairo tayi shi ba, Hajia Aynarh tayi, kuma yana iya cin Amala, don yana son abincin, ita kuma bata yi zaton zaici ba shisa bata tambayeshi ba, a hankali suka hada ido yace mata "Amala" Ziyada ta murmusa, Najwa tace ita kuma a bata irin na Hajjo ba wai don ta san meye ba, amma don yayi kama da wani soup din India, kowa ya fadi abunda zaici akayi serving kowa..
Addua Daddy ya umurta ayi, a tare kowa yayi suka fara cin Abinci, kasancewar duk Abinci da busasshen kifi da kuma gasasshen kifi akayi, in ba ci kayi ba ba zaka gane kifi bane, yafi kama da Nama.
Ko Cokali biyu ba suyi ba numfashin Zaid da Najwa ya fara daukewa, sama sama Numfashin ya fara, AbdulMajeed da ya kafa Najwa da ido ya lura da abunda takeyi yayi saurin ajiye spoon yace "PureHeart are You OK?" Zaineema ta kalli Najwa tayi saurin mikewa tsaye Hajia Aynarh ma haka, Najwa me ya faru? Abu takeyi kamar mai neman shidewa, Ziyada ta dan waiga ta kalli Zaid, gabanta ya fadi, irin abun Najwa yakeyi, numfashin shi samasama, fuskarshi yayi ja, da sauri ta karasa gunta "My Forever, lafiya" Hankalin Mairo ya tashi ta mike ta ci kwalar Aunty Aynarh "Munafuka Algunguma, me kika sa ma Abinci? Me kika sa ma sirikina? So kike ya mutu" Aunty Aynarh ta tsure sosai tana girgiza kai tace "Wallahi bansa komai ba, Wallahi ba abunda na sa, mukai su Asibiti" Najwa ta riko hannun Hajjo tana bankarewa kamar zata mutu, Zaid ma hannu ya sa ya rike wuyanshi yana jan numfashin dake fita da kyar, fuskar nan tayi Ja, Daddy yayi saurin fita don taro A daidajta sahu a kaisu Asibiti, yana fita ya ci karo da Convoy din Zaid, Ziyada Hawaye kawai takeyi hankalinta tashe, Abdulmajeed hankali a tashe ya kalli Aunty Aynarh yace "Aunty kinsa Kifi a abincin nan?" da sauri ta gyada kai tace "duka abincin da Kifi nayi shi" Abdulmajeed ya ruga kitchen a guje, Ya shiga bincikar Kayan Miya da ya siyo dazun Tomatoes ya dauko, ko wankewa beyi ba ya fito ya mika ma Ziyada 1 yace ki bashi, lokacin sun fara fita daga hayaccinsu, fasawa yayi da bakinshi ya juye ma Najwa ruwan tumatirin a baki, haka Ziyada ta ma Zaid, a hankali a hankali numfashin su ya fara dawowa daidai, daidai nan Idi da wasu Yaran Zaid suka shigo sukayi kan Zaid wai zasu kaishi Asibiti, daga musu hannu yayi yace "i'm fine" Ziyada tace "me ya faru da kai?" Zaid yace "ina tsammanin Abincin nan akwai Fish, and i'm allergic to Fish" daidai lokacin da Najwa ta ke ce ma Hajia Aynarh "Dama bansan da kifi a cikin Abincin ba, shine naci?" Hajia Aynarh tace "I'm So Sorry, wallahi bansan ba kwa son Kifi ba, Abincin ba wanda ban sa Kifi ciki ba, kuyi hakuri donAllah" Najwa tace "Laah Aunty ba wani abu, ni in na samu irin attack dinnan da na sha tomato zanji normal, ai farkon zuwana Nigeria na taba samun attack din" Abdulmajeed yace "shiyasa na tuna Tomato ne first Aid treatment din" Zaid ya kira Idi ya zo kusa dashi, ya rada mai abu a kunne, da sauri ya fita, Aunty Aynarh duk tayi wani iri, gani take laifinta ne, Zaid ya kalle su Daddy da sukayi cirko cirko suna kallonsu yace "Baba Abba ku zauna ku cigaba da cin Abincinku, Ni kifin ne bana so, yanzu zaa kawo min wani Miyan sai in ci" Daddy ya sage yana kallon Zaid, wani abu ke bin zuciyanshi, dunia Zaidun Sada kadai ke ce mishi "Baba Abba" jiki a sake ya zauna, yace da Muhsin su cigaba daci, Daddy ya kallesu yace "sai kuka tuna min da k'anina Marigayi, kunsan shi ko kanshi Kifi ya ji sai ya fara sheshek'a?" Hajjo ta chabe tace "haka ne, ko abinci nayi da Man kifi in ya fara Amai kamar zai zazzago kayan cikinsa" Zaid ya runtse idonsa yana tausar zuciyarsa. Abincinsu su ka cigaba daci banda su 3, Zaid da Najwa da Mummy, su kadai ne basu cin Abincin, gaban Mairo ke dukan uku uku, ta kalli Najwa a kalli Zaid, tunanin da bata son yi ta fara yi, Sada be cin Kifi, Zaid din Sada be cin Kifi, Wannan dan Sada ne. Da sauri ta girgiza kanta ta tashi kamar mahaukaciya ta shige daki, daidai nan Idi yayi Sallama da Cooler a hanayensa, Gaban Oganshi ya Dire, Ziyada ta bude Miyan Kubewa danya ne da yaji Jan Nama, ta bude wani Amalan ta sa mai da miyan Kubewar, ta kalli Najwa tace "in sa miki ko? " kai Najwa ta daga, Ziyada ta zuba mata suka cigaba da ci, Hajia Aynarh ta saukar da Ajiyar zucia ganin basuyi zargin ko tayi poisoning dinsu bane.
I N D I A
Duk wasu Process na tafia sun gama, Jirginsu zai tashi Gobe zuwa Dubai, washegari su tafi Nigeria inda zasu isa Lagos daga nan suyi Kano, Paapa da Maama sunyi Resigning a wuraren Aikinsu, an basu kudin Sallama me tsoka, harta Motocinsu da Gidan da suke zaune sun saida, Paapa ya samu wani Agent dan Kano suna communicating, nan ya tura mishi kudi ya siya mishi dankareren Gida a Tarauni, don shi baya tunanin zai koma Gidanshi na da, yafi karfin ya tada Yayanshi a gidan da yake, ya bar mai Gidan nan har abada, Maama ta dinga shiga Gidajen Neighbors dinsu tana musu sallama, Vijhay Bhaiya yayi kuka sosai, Maama tace "InshaAllah zasu zo wani lokacin" bayan sun mishi Alheri me yawa, ko da ta shiga Gidansu Kaveri nan suka bata lokaci da Maman kaveri suna jimamin rabuwansu, Kaveri kuwa bata fito ba tana daki tana cizgar Kuka.
N I G E R I A.