Sashe 97
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Na kwana da tunanin Aliyu mamakin kalamansa har suka saka ni murmushi ni kadai, washe garin ranar da gagan na ki fita ko'ina saboda kar Aliyu ya gan ni ko kuma ni na ganshi abinci mu da komai Momy aiko mana tai kamar yadda ta saba ko da yake wani lokacin ta kan aiko tace na zo na dauka. Ban wani ci abinci sosai ba na kwanta, sai Momy ta aiko tana kiran Nana, ni dai ban san lokacin da ta dawo ba domin bachi yayi gaba da ni, washe gari bayan na yi sallah asuba na zauna sai da rana ta fito sannan na nufi nufi part din Momy, wani abun mamaki sai na samu kaina da kasa shiga ciki, sai kawai na juyo na dawo kamin na karasa motar Aliyu ta shigo harabar gidan yana sauri ya fito daga motar yai min magana ni kuma yai sauri har da hadawa da gudu na shige cikin bq din. Ban fadawa Nana komai ba sai dai tana ganina ta san ban shiga part din ba domin ban isa ace na shiga har na yi sharar na fito ba. Amina ce ta kawo mana abun karyawa a maimakon Siyama wacce ta saba kowa mana, sai da ta gaisa da Nana sannan ta fada min cewar idan na gama karyarwa na shirya zamu je gidan wata Hajiya Ramatu kawar Momy wai a can za mu yuni. Ina ta mamakin fita da safe haka kuma wai mu wuni a can amman kuma ta taimaka min ko ba komai bana son haduwa da Aliyu a yanzu gashi yau friday kamar jiya ba zuwa makaranta ake ba.
Misalin goma da yan mintuna mu kabar gidan a lokacin har na fara ganin bakin fuska a gidan cikin kuwa har da abokinsa Nasir. A gidan Hajiya Ramatu muka wuni ni da Amina wanda ban san dalilin hakan ba, kuma na kasa natsuwa saboda jefi jefi sai Hajiyar ta kira ni Amarya sai murna take da alama itama tana son auren kamar yadda aminiyarta Momy take so.
Bayan gama sallah azahar ina zaune ina kallon arewa24 suna kokarin karkare wani shirin hausa mata da miji Amina da shigo da waina a a plate da miya ta aje min
“Gashi nan ki ci wainar daurin aurenki yau an daura miki aure Ataa igiya uku ta hau kan ki, Kin zama Mrs Aliyu Aliyu......”
Kamar wacce ta fara ji a yau haka na ji maganar wani kallo na ke mata da ke nuna cewar sam ban fahimci inda zancen ta ya dosa ba, sai ta kama kumatuna ra ja.
“Seriously yau friday aka daura aurenk after Jumma'at prayer congratulations you're now our sister-in-law”
Ta fada ta rumgume ni cike da murna. Ni dai daga turanci da bana ji har hausar ban iya gane komai ba domin a rikece na ke.
Sorry two days ina post a night 😑🙏
*Z A K I -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660*
Ba kowa da kowa aka gayyato a gurin daurin auren ba, sai makusantan Aliyu ciki kuwa har da abokansa duk kuwa da wasu ba su samu zuwa ba bikin ba kawai sun samu sakon ne daga Aliyu wasu kuma daga Nasir gashi lokaci ya kure ba su samu zuwa ba. Sun samu addu'a sosai albarka jama'a kasancewar massallacin juma'a kuma babban masallaci wanda mutake ke taruwa sosai bayan daura auren nasa aka daura na wasu mutanen biyu.
A cikin mutanen da suka samu halartar daurin auren har da Kamal wanda Nasir ya sanar da shi amadadin Aliyu, baya farinciki da auren Aliyu da Ataa sai dai kuma baya bakinciki, domin ya san daman Aliyu yana son ta kuma tunda aka ce tana gidansu daman yasan tsakanin Muhseen da Aliyu dole sai ta auri daya. He know what he did to Mama Fulani be kyauta ba, Mahaifiyarsa ma ta masa fada akan hakan kasancewar Mama Fulani kawarta ce kuma makociyarsu bugu da kari kuma mahaifiyar Aliyu domin kamar uwa take a gurinsa. Daman yana neman hanyar da zai shirya da abokinsa kuma ya bashi hakuri kan abunda ya faru, sai dai ba zai iya iya kiran Aliyu kai tsaye ba sanin halinsa na wulakanci zai iya neman ya wulakanta shi ganin ya kawo kansa da kansa kamar yadda yake ganin Mama Fulani ma zata iya masa.
But sanar da shi da Nasir yai cewar Aliyu yana gayyatarsa dauren aurensa ya sa bari duk wani aiki da yake da shi a ranar friday din ya halarci daurin auren, yana ga jin kamar ace shi ne ya auri Ataa. After daurin auren aka wuce shukura hotel aka ci abinci mai kyau drinks ma sai wanda ran mutum ke so.
Ango ya sha kyau shaddar jikinaa ai wani haske take yana wani maiko kana gani ka san shaddar masu naira ce, ko masu nairan ba kananan ba, farar shadda ce wacce ta sha aiki, ga wasu expensive shoes da be taba zuba zuba kudi mai yawa ya siye takalmin da suka kai wadanda Nasir ya zo nasa da su daga Abuja tsada ba, hular kansa kadai tana siyen tufafin wani mai kudin kala goma. Zuciyar Aliyu kal ransa fes kamar babu abunda ya taba bata masa rai a duniya, wasu family friends dinsa har mamakin yadda ya sake da mutane yake ta dariya suke domin sun san ba halin Aliyu ba ne. Amman sai dariya yake baki har kunnuwa yadda yai muran da zuwan Kamal sai ka dauka ma wani abu be shiga tsakaninsu ba, farinciki aure ya saka ya manta da komai.
After lunch a hotel wasu suka kama hanyar Abuja wandan suka zo daga can ciki kuwa har da Abbah da wasu aminansa, yan wasu garuruwan ma suka kama hanya, har da yan Yola wato yan uwan Mama Fulani domin sun san Aliyu dan Mama Fulani ne sai dai Abbah ne ya sanar da su ba Mama Fulani ba, har da kanen Ammy biyu da goma suke Kaduna sai da suka zo.
Momy tana gida tana fama da nata Familyn da kuma Familyn Daddy ana ta wasa da dariya sai tsarguwar juna suke ita da tabasanta da kuma tabansan Daddy, abun gwanin burgewa, Husna da Siyama da wasu cousins dinsu mata su suke rabawa baki abincin, a gidan an yi jalof din shimkafa da kuskus, fried rice, waina da kuma tuwan shimkafa. And su snacks cake da donuts. Drinks ko tun daga na zobo kunun aya, kunun waken suya, ginger da na waje babu kalar da babu, daga Candy Restaurant Momy tai order komai, sai ka dauka ma wunin biki ake ba wai daurin aure ne kawai ba. Yadda aka taru abun har Mamaki ya bawa Momy domin wasu dai bata san ta fada musu ba, musamman ma matan da suka zo na zaton ko har da wunin bikin ne. Komai na Nana Momy ware mata tai ta aika mata a bangarenta.
Sai kusan magariba Momy ta samu kanta, daman wasu daga familynsa da suka so yan matan sun ce a nan za su kwana, Husna da Siyama sai labari ake yana jindadi an hadu da yan'uwa, Amina ce kawai bata nan kowa sai tambayarta yake sai a fada musu tana can tare da Amarya, sai dai ba a fada musu inda Amarya take saboda Momy ta fadawa su Husna da Siyama cewar bata son a damu Ataa domin bata san da daurin auren yau ba kuma bata saba ba, ba karamin aikinta ne ba ta sakawa mutane kuka.
ALIYU POV.
Da kansa ya raka wasu friends dinsa airport yana ta musu godiya cikinsu kuwa har da Kamal, sai dai ya kasa sakewa yana ta jin kunyar Aliyu har sai da ya ga Aliyun ha wayance kamar ba shi ba, ko kuma ya manta da abunda ya faru sannan shi ma ya saki jikinsa har yai ma Aliyun sallama su kai shaking hands.
A hanyar su ta dawo gida tare da Nasir yake driving yana sokonar Aliyu.
“An daura auren nan dai hankali ya kwanta”
“Wallahi kuwa yanzu hankalina a kwance yake fes ba ni da wata matsala malam”
“Ango ango angon da ba Amarya”
“Inji uban wa?”
Nasir ya kyalkyale da wata mahaukaciyar dariya wacce ta saka Aliyu da kansa shi ma ya dara.
“Ai kasan dai Momy ba zata baka amarya nan yanzu ba ko? Sai ta girma”
“Girma? Ta girma a gidana na yarda dai ba zata tare a yau ba”
“Kuma daidai ne ace yadda ka sha shaddar nan ajima a kai maka amaryar ka”
“Na rantse da Allah kau, Nasir kai mugu ne Wallahi”
Nasir din ya sake saka masa dariya har da buga sitarin motar. Aliyu yai murmushi yana cire hularsa ya shafa kansa, sai a yanzu yake jin cewar lallai yayi dacen auren Ataa daman yana son yan latsu wato karamar yarinya kamarta wance bata iya komai bata san komai ba bata waye ba a komai ba, kuma bata taba soyayya ba, he know littafinsa ne zai bude a kwakwaltar da kuma zuciyata domin ya san duk abunda ya koya mata shi zata haddace ya zauna a kanta.
A harabar gidansu Momy Nasir ya faka motarsa ya riga Aliyu fita ya shiga ciki domin gaisawa da Momy daman tun da ya diro garin be leko nan ba, kai tsaye na nufi gurin abokinsa, daga can suka nufi gurin daurin aure kamin su soma hidimar abokansu.
Aliyu na kokarin fita motar wayarsa tai vibration alamar kira, ciro wayar yai daga aljihunsa sai ya ga bakuwar number yar waje saman screen din wayar na nuna masa ana masa kiran ne daga Dubai. Kai tsaye ya fahimci cewar mai kiran tasa ba kowa ba ce face Rahma. Murmushi yai ya danna picking ya kafa wayar a kunne.
“Hello Dear ya Dubai? Hope hutun yayi miki dadi?”
“Aliyu ka yi aure?”
Ta tambaya a sanyaye gabanta sai faduwa yake tana son ya amsa mata da capital NO.
“Yes Yau din nan aka kara dora min wani nauyi da kuma hakki, daraja ta ta dagu daga mai mata daya zuwa biyu”
“Aliyu?”
“Ana wasa da aure ne Rahma? Ai kin san ko zan miki wasa da komai ban da aure ko?”
Misalin goma da yan mintuna mu kabar gidan a lokacin har na fara ganin bakin fuska a gidan cikin kuwa har da abokinsa Nasir. A gidan Hajiya Ramatu muka wuni ni da Amina wanda ban san dalilin hakan ba, kuma na kasa natsuwa saboda jefi jefi sai Hajiyar ta kira ni Amarya sai murna take da alama itama tana son auren kamar yadda aminiyarta Momy take so.
Bayan gama sallah azahar ina zaune ina kallon arewa24 suna kokarin karkare wani shirin hausa mata da miji Amina da shigo da waina a a plate da miya ta aje min
“Gashi nan ki ci wainar daurin aurenki yau an daura miki aure Ataa igiya uku ta hau kan ki, Kin zama Mrs Aliyu Aliyu......”
Kamar wacce ta fara ji a yau haka na ji maganar wani kallo na ke mata da ke nuna cewar sam ban fahimci inda zancen ta ya dosa ba, sai ta kama kumatuna ra ja.
“Seriously yau friday aka daura aurenk after Jumma'at prayer congratulations you're now our sister-in-law”
Ta fada ta rumgume ni cike da murna. Ni dai daga turanci da bana ji har hausar ban iya gane komai ba domin a rikece na ke.
Sorry two days ina post a night 😑🙏
*Z A K I -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660*
Ba kowa da kowa aka gayyato a gurin daurin auren ba, sai makusantan Aliyu ciki kuwa har da abokansa duk kuwa da wasu ba su samu zuwa ba bikin ba kawai sun samu sakon ne daga Aliyu wasu kuma daga Nasir gashi lokaci ya kure ba su samu zuwa ba. Sun samu addu'a sosai albarka jama'a kasancewar massallacin juma'a kuma babban masallaci wanda mutake ke taruwa sosai bayan daura auren nasa aka daura na wasu mutanen biyu.
A cikin mutanen da suka samu halartar daurin auren har da Kamal wanda Nasir ya sanar da shi amadadin Aliyu, baya farinciki da auren Aliyu da Ataa sai dai kuma baya bakinciki, domin ya san daman Aliyu yana son ta kuma tunda aka ce tana gidansu daman yasan tsakanin Muhseen da Aliyu dole sai ta auri daya. He know what he did to Mama Fulani be kyauta ba, Mahaifiyarsa ma ta masa fada akan hakan kasancewar Mama Fulani kawarta ce kuma makociyarsu bugu da kari kuma mahaifiyar Aliyu domin kamar uwa take a gurinsa. Daman yana neman hanyar da zai shirya da abokinsa kuma ya bashi hakuri kan abunda ya faru, sai dai ba zai iya iya kiran Aliyu kai tsaye ba sanin halinsa na wulakanci zai iya neman ya wulakanta shi ganin ya kawo kansa da kansa kamar yadda yake ganin Mama Fulani ma zata iya masa.
But sanar da shi da Nasir yai cewar Aliyu yana gayyatarsa dauren aurensa ya sa bari duk wani aiki da yake da shi a ranar friday din ya halarci daurin auren, yana ga jin kamar ace shi ne ya auri Ataa. After daurin auren aka wuce shukura hotel aka ci abinci mai kyau drinks ma sai wanda ran mutum ke so.
Ango ya sha kyau shaddar jikinaa ai wani haske take yana wani maiko kana gani ka san shaddar masu naira ce, ko masu nairan ba kananan ba, farar shadda ce wacce ta sha aiki, ga wasu expensive shoes da be taba zuba zuba kudi mai yawa ya siye takalmin da suka kai wadanda Nasir ya zo nasa da su daga Abuja tsada ba, hular kansa kadai tana siyen tufafin wani mai kudin kala goma. Zuciyar Aliyu kal ransa fes kamar babu abunda ya taba bata masa rai a duniya, wasu family friends dinsa har mamakin yadda ya sake da mutane yake ta dariya suke domin sun san ba halin Aliyu ba ne. Amman sai dariya yake baki har kunnuwa yadda yai muran da zuwan Kamal sai ka dauka ma wani abu be shiga tsakaninsu ba, farinciki aure ya saka ya manta da komai.
After lunch a hotel wasu suka kama hanyar Abuja wandan suka zo daga can ciki kuwa har da Abbah da wasu aminansa, yan wasu garuruwan ma suka kama hanya, har da yan Yola wato yan uwan Mama Fulani domin sun san Aliyu dan Mama Fulani ne sai dai Abbah ne ya sanar da su ba Mama Fulani ba, har da kanen Ammy biyu da goma suke Kaduna sai da suka zo.
Momy tana gida tana fama da nata Familyn da kuma Familyn Daddy ana ta wasa da dariya sai tsarguwar juna suke ita da tabasanta da kuma tabansan Daddy, abun gwanin burgewa, Husna da Siyama da wasu cousins dinsu mata su suke rabawa baki abincin, a gidan an yi jalof din shimkafa da kuskus, fried rice, waina da kuma tuwan shimkafa. And su snacks cake da donuts. Drinks ko tun daga na zobo kunun aya, kunun waken suya, ginger da na waje babu kalar da babu, daga Candy Restaurant Momy tai order komai, sai ka dauka ma wunin biki ake ba wai daurin aure ne kawai ba. Yadda aka taru abun har Mamaki ya bawa Momy domin wasu dai bata san ta fada musu ba, musamman ma matan da suka zo na zaton ko har da wunin bikin ne. Komai na Nana Momy ware mata tai ta aika mata a bangarenta.
Sai kusan magariba Momy ta samu kanta, daman wasu daga familynsa da suka so yan matan sun ce a nan za su kwana, Husna da Siyama sai labari ake yana jindadi an hadu da yan'uwa, Amina ce kawai bata nan kowa sai tambayarta yake sai a fada musu tana can tare da Amarya, sai dai ba a fada musu inda Amarya take saboda Momy ta fadawa su Husna da Siyama cewar bata son a damu Ataa domin bata san da daurin auren yau ba kuma bata saba ba, ba karamin aikinta ne ba ta sakawa mutane kuka.
ALIYU POV.
Da kansa ya raka wasu friends dinsa airport yana ta musu godiya cikinsu kuwa har da Kamal, sai dai ya kasa sakewa yana ta jin kunyar Aliyu har sai da ya ga Aliyun ha wayance kamar ba shi ba, ko kuma ya manta da abunda ya faru sannan shi ma ya saki jikinsa har yai ma Aliyun sallama su kai shaking hands.
A hanyar su ta dawo gida tare da Nasir yake driving yana sokonar Aliyu.
“An daura auren nan dai hankali ya kwanta”
“Wallahi kuwa yanzu hankalina a kwance yake fes ba ni da wata matsala malam”
“Ango ango angon da ba Amarya”
“Inji uban wa?”
Nasir ya kyalkyale da wata mahaukaciyar dariya wacce ta saka Aliyu da kansa shi ma ya dara.
“Ai kasan dai Momy ba zata baka amarya nan yanzu ba ko? Sai ta girma”
“Girma? Ta girma a gidana na yarda dai ba zata tare a yau ba”
“Kuma daidai ne ace yadda ka sha shaddar nan ajima a kai maka amaryar ka”
“Na rantse da Allah kau, Nasir kai mugu ne Wallahi”
Nasir din ya sake saka masa dariya har da buga sitarin motar. Aliyu yai murmushi yana cire hularsa ya shafa kansa, sai a yanzu yake jin cewar lallai yayi dacen auren Ataa daman yana son yan latsu wato karamar yarinya kamarta wance bata iya komai bata san komai ba bata waye ba a komai ba, kuma bata taba soyayya ba, he know littafinsa ne zai bude a kwakwaltar da kuma zuciyata domin ya san duk abunda ya koya mata shi zata haddace ya zauna a kanta.
A harabar gidansu Momy Nasir ya faka motarsa ya riga Aliyu fita ya shiga ciki domin gaisawa da Momy daman tun da ya diro garin be leko nan ba, kai tsaye na nufi gurin abokinsa, daga can suka nufi gurin daurin aure kamin su soma hidimar abokansu.
Aliyu na kokarin fita motar wayarsa tai vibration alamar kira, ciro wayar yai daga aljihunsa sai ya ga bakuwar number yar waje saman screen din wayar na nuna masa ana masa kiran ne daga Dubai. Kai tsaye ya fahimci cewar mai kiran tasa ba kowa ba ce face Rahma. Murmushi yai ya danna picking ya kafa wayar a kunne.
“Hello Dear ya Dubai? Hope hutun yayi miki dadi?”
“Aliyu ka yi aure?”
Ta tambaya a sanyaye gabanta sai faduwa yake tana son ya amsa mata da capital NO.
“Yes Yau din nan aka kara dora min wani nauyi da kuma hakki, daraja ta ta dagu daga mai mata daya zuwa biyu”
“Aliyu?”
“Ana wasa da aure ne Rahma? Ai kin san ko zan miki wasa da komai ban da aure ko?”