Sashe 13
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
“Ba a mata tiyatar ko da ba likita, maciji ne kawai ya tsareta aka cire dafin”
“Ba ama cizon maciji tiyata allura kawai ake, wannan tiyatar koda ce aka cire mata”
Ji nai kamar ba a duniyar nan na ke ba, sama na ke kasa na ke sai na kasa tantancewa yawu suka cika min baki daman can ido suna ta aikinsu na hawaye. Kar dai ace likitan nn ya da taimake mu kodarta ya cire? Kar dai duk taimakon da yai mana na siyen kodarta ne?
“Amman dan kara tabbatarwa ki je ki yi wannan babban hoton”
Ya miko min wata takardar. Da na cira kafar na je na karbo sai na ji kamar an rike ni kafafuwan suka lauye gurin daya suka min majiyar kamar wacce ta shekara a tsaye.
“Wane likita ne yai mata tiyatar yace za a cire dafin maciji?”
“Wa... Ni... ”
Na amsawa likitan maganar na fito min a rarrabe.
“Ya cuce ku ne kawai ko kuma an gada kai da shi an cuce ku, amman dafin maciji ai ba a masa tiyata”
Daker na karasa na karbi takadar ya juyo kamar kazar da kwai ya fashewa na fito daga dakin likitan ina hawayen da ban ta ina ake turo min su ba. Ban san nawa hoton zai ci ba amman tun da ya ce babban hoto nasan sai ya ci fiye da dubu da wani abu da wacan karamin hoton ya ci, gashi sauran kudin da ke hannuna ba su kai ma dubu uku ba. Da wowa nai kusa da ita na zauna a kujerar roba da ke gabanta, ta bude baki tana sheda da nan da alama numfashin da ke fita daga hancinta baya isarta. Wani irin tausayinta ne ya lullube ni ina ta kallon fuskarta kamar yau na fara ganinta, taya zan iya fadawa Nana ya cire mata koda? Taya ma zata rayu ba koda? A tunani idan mutum ya rasa wani abu daga sassan jikinsa mutuwa zai yi.
“Shikenan Nana shikenan”
Na fada ina jan Lukman na rumgume, sai na saka kaina cikin jikakkar rigarsa na fashe da kuka marar sauti, ganin haka ba yasa shi ma ya fashe da kuka yana ta kallonta.
ALIYU POV.
Babbar asibiti ce kuma kwararriyar a duk fadin duniya, tun da aka ce za a mata dashen a can a cire dayar wacce ta fara lalacewa sai ya hankalinsa ya kwanta domin manyan likitocin ne za su mata aiki kuma sun san kan aikinsu. Within week din da suka je London aka yi mata aikin cikin iyawar Allah da ikonsa aka yi nasarar cire wacan kodar aka dasa mata wata. A can aka cigaba da kula da ita har na tsawon wata daya a ciki wata na biyu ne suka sallamota ta dawo gida Nigeria tare da mijinta da kuma mahaifiyarta wacce sukai tafiyar tare.
A nan gidan ma kusan kullum sai Doc Asim da wani likitan Doc Jonah sun zo dubata, sosai ta so su tare a Abuja tun dawowarsu daman a can suke zama, amman Aliyu ya ki saboda yana son ya koma Abuja da zama a halin da matarsa take bukatar lokacinsa, ya san duk yadda ya ke son bata kulawa idan har suka je Abuja dole ne sai ya leka office amma a nan yana tare da ita tun safe har dare.
At early morning ya farka yau kamar yadda ya sabawa kansa tun da suka dawo gida. Da kansa ya shiga kitchen ya saffara mata abunda zata ci idan ta farka sannan ya dawo falo ya zauna yana duba wasu abubuwan a laptop dinsa.
“Aliyu...”
Ta kwala masa kira daga dakin da take kwance duk da tasan ba zai amsa ba amman ta san zai ji ta, daman can baya amsa kira idan aka kira sunansa, sai dai idan yana kusa da kai ya kalleka ko kuma ya taso ya zo idan shine a kasa da kai, idan kuma kai ne a kasa da shi sai dai ka je ka same shi. Laptop din ya aje ya mike tsaye ya nufi upstairs fuskarsa ba yabo ba fallasa.
Zaune ya sameta saman gadon ta dukunkune da bargo ta wani bata fuska kamar karamar yarinya.
“Sanyi na ke ji waya ce ka kunna ac”
Sai ya kai hannu ya kashe ac ya hauro saman gadon ya yaye blanket din da ta lulluba da shi yai kissing fuskarta.
“Ta so muje ki karya kin san sun ce ki rika karyawa ba sai kin ji yunwa ba”
“Me ka dafa min”
“Doya da madara ka san kina so ai”
“Ba ka iya ba fa”
“I try ”
Ya fada, yadda yake amsa maganar sai na rantse da Allah ba a bakinsa take fitowa ba, domin babu wata alama da ke nuna cewar magana yake. Saukowa yai da ita saman gadon ya nufi bandaki da ita da kansa ya wanke mata baki as usual sannan ya fito tare da ita.
“Gidan nan duk yai datti kuma bathroom din ma yai wata ba a wanke ba ni kyamar Shiga ma na ke”
Ta fada masa a daidai saitin kunnensa ba ce da ita komai ba ya ja suka nufi hanyar fita daga bedroom din.
“Ka ji?”
Nan ma be ce komai ba har suka sauko downstairs, daman can haka yake kamar wanda maganar take masa wahala, kujera yaja mata ta zauna akan dinning.
“Ba ka ce komai ba”
“Za mu samu wanda zai rika mana shara da gyara gida”
Ya fada sannan ya zauna ya shiga serving dinta, da kansa yake feeding dinta har ta koshi sannan ya zuba ma kansa ya ci.
“Yaushe za ka samo?”
Haka ta dinga tambayarsa amman be ce mata komai ba, har ya gama cin abincin ya tashi.
“Ni wannan miskilancin na ka damuna ya ke”
A dai-dai lokacin da zai stairs ta fadi haka, sai kawai ya juyo ya sakar mata murmushi gefen fuska ya juya ya haye sama.
________
An ciye kidney din wata an raya wata 😪
https://my.w.tt/PWohUhlPv9.
*Z A K I*
By Khadeeja Candy
9️⃣
A saman kujera na kwana a zaune ina ta kallon Nana tun ina kuka da hawaye har na koma ina ta rare kukan kawai babu hawaye. A kasan gurin Lukman ya kwana. Tun da asubar fari masu sharar asibiti suka tashe Lukman ni kuma suka ce na fita za su gyara gurin. Ba dan babu yadda xan yi ba da ba zan fita ba, domin ina jin kamar idan nai nisa da Nana mutuwa za tai ta barni.
A haka na fito ward din ina jin zuciyata babu dadi, Lukman kuma na ta murja ido alamar bachin be isheshi, kai tsaye gida na nufa kai tsaye domin samawa Nana abunda zata ci da ita da Lukman, wannan karon da kafa na iso kasancewar daga unguwar Clapperto zuwa uduth babu wani tazara sosai ga talaka irina wanda ya saba da tafiyar kasa. Ina janye da hannun Lukman har muka iso kangon gidan. Tsaye nai ina ta tunani ta inda zan fara, rashin lafiyar Nana ta tsaya min a rai har na so min kamar bana da wani sauran kuzari.
“Ataa ya me za mu yi?”
Maganar Lukman ce tasa na dawo daga dogon tunanin da nake rakiyar zuciyata da shi.
“Koko zan siya maka kai da Nana”
“Ni ba zan sha ba”
Ya fada yana mitsintsika ido.
“Saboda me? Ko waina kake so?”
“Aa bana son komai Nana na ke son ta samu lafiya, Ataa ai zata tashi ko? Zata ji sauki ko? Na yi mafarki ta samu sauki tana min magana”
Wani irin tausayinsa da na kaina nd ya lullube ni a lokaci daya, duk yadda na ke shakuwa da Nana nasan Lukman ya fini shakuwa da ita domin shi karamin yaro ne, kuma kusan kullum tare suke zuwa bara tsabanin ni da wani lokacin na ke zuwa wani gurin dabam.
“Zata ji sauki idan kana cin abinci,Nana tana son ta ganka kana cin abinci”
“Haka ta fada miki? Da na yi kwana ta farka?”
“Ba ama cizon maciji tiyata allura kawai ake, wannan tiyatar koda ce aka cire mata”
Ji nai kamar ba a duniyar nan na ke ba, sama na ke kasa na ke sai na kasa tantancewa yawu suka cika min baki daman can ido suna ta aikinsu na hawaye. Kar dai ace likitan nn ya da taimake mu kodarta ya cire? Kar dai duk taimakon da yai mana na siyen kodarta ne?
“Amman dan kara tabbatarwa ki je ki yi wannan babban hoton”
Ya miko min wata takardar. Da na cira kafar na je na karbo sai na ji kamar an rike ni kafafuwan suka lauye gurin daya suka min majiyar kamar wacce ta shekara a tsaye.
“Wane likita ne yai mata tiyatar yace za a cire dafin maciji?”
“Wa... Ni... ”
Na amsawa likitan maganar na fito min a rarrabe.
“Ya cuce ku ne kawai ko kuma an gada kai da shi an cuce ku, amman dafin maciji ai ba a masa tiyata”
Daker na karasa na karbi takadar ya juyo kamar kazar da kwai ya fashewa na fito daga dakin likitan ina hawayen da ban ta ina ake turo min su ba. Ban san nawa hoton zai ci ba amman tun da ya ce babban hoto nasan sai ya ci fiye da dubu da wani abu da wacan karamin hoton ya ci, gashi sauran kudin da ke hannuna ba su kai ma dubu uku ba. Da wowa nai kusa da ita na zauna a kujerar roba da ke gabanta, ta bude baki tana sheda da nan da alama numfashin da ke fita daga hancinta baya isarta. Wani irin tausayinta ne ya lullube ni ina ta kallon fuskarta kamar yau na fara ganinta, taya zan iya fadawa Nana ya cire mata koda? Taya ma zata rayu ba koda? A tunani idan mutum ya rasa wani abu daga sassan jikinsa mutuwa zai yi.
“Shikenan Nana shikenan”
Na fada ina jan Lukman na rumgume, sai na saka kaina cikin jikakkar rigarsa na fashe da kuka marar sauti, ganin haka ba yasa shi ma ya fashe da kuka yana ta kallonta.
ALIYU POV.
Babbar asibiti ce kuma kwararriyar a duk fadin duniya, tun da aka ce za a mata dashen a can a cire dayar wacce ta fara lalacewa sai ya hankalinsa ya kwanta domin manyan likitocin ne za su mata aiki kuma sun san kan aikinsu. Within week din da suka je London aka yi mata aikin cikin iyawar Allah da ikonsa aka yi nasarar cire wacan kodar aka dasa mata wata. A can aka cigaba da kula da ita har na tsawon wata daya a ciki wata na biyu ne suka sallamota ta dawo gida Nigeria tare da mijinta da kuma mahaifiyarta wacce sukai tafiyar tare.
A nan gidan ma kusan kullum sai Doc Asim da wani likitan Doc Jonah sun zo dubata, sosai ta so su tare a Abuja tun dawowarsu daman a can suke zama, amman Aliyu ya ki saboda yana son ya koma Abuja da zama a halin da matarsa take bukatar lokacinsa, ya san duk yadda ya ke son bata kulawa idan har suka je Abuja dole ne sai ya leka office amma a nan yana tare da ita tun safe har dare.
At early morning ya farka yau kamar yadda ya sabawa kansa tun da suka dawo gida. Da kansa ya shiga kitchen ya saffara mata abunda zata ci idan ta farka sannan ya dawo falo ya zauna yana duba wasu abubuwan a laptop dinsa.
“Aliyu...”
Ta kwala masa kira daga dakin da take kwance duk da tasan ba zai amsa ba amman ta san zai ji ta, daman can baya amsa kira idan aka kira sunansa, sai dai idan yana kusa da kai ya kalleka ko kuma ya taso ya zo idan shine a kasa da kai, idan kuma kai ne a kasa da shi sai dai ka je ka same shi. Laptop din ya aje ya mike tsaye ya nufi upstairs fuskarsa ba yabo ba fallasa.
Zaune ya sameta saman gadon ta dukunkune da bargo ta wani bata fuska kamar karamar yarinya.
“Sanyi na ke ji waya ce ka kunna ac”
Sai ya kai hannu ya kashe ac ya hauro saman gadon ya yaye blanket din da ta lulluba da shi yai kissing fuskarta.
“Ta so muje ki karya kin san sun ce ki rika karyawa ba sai kin ji yunwa ba”
“Me ka dafa min”
“Doya da madara ka san kina so ai”
“Ba ka iya ba fa”
“I try ”
Ya fada, yadda yake amsa maganar sai na rantse da Allah ba a bakinsa take fitowa ba, domin babu wata alama da ke nuna cewar magana yake. Saukowa yai da ita saman gadon ya nufi bandaki da ita da kansa ya wanke mata baki as usual sannan ya fito tare da ita.
“Gidan nan duk yai datti kuma bathroom din ma yai wata ba a wanke ba ni kyamar Shiga ma na ke”
Ta fada masa a daidai saitin kunnensa ba ce da ita komai ba ya ja suka nufi hanyar fita daga bedroom din.
“Ka ji?”
Nan ma be ce komai ba har suka sauko downstairs, daman can haka yake kamar wanda maganar take masa wahala, kujera yaja mata ta zauna akan dinning.
“Ba ka ce komai ba”
“Za mu samu wanda zai rika mana shara da gyara gida”
Ya fada sannan ya zauna ya shiga serving dinta, da kansa yake feeding dinta har ta koshi sannan ya zuba ma kansa ya ci.
“Yaushe za ka samo?”
Haka ta dinga tambayarsa amman be ce mata komai ba, har ya gama cin abincin ya tashi.
“Ni wannan miskilancin na ka damuna ya ke”
A dai-dai lokacin da zai stairs ta fadi haka, sai kawai ya juyo ya sakar mata murmushi gefen fuska ya juya ya haye sama.
________
An ciye kidney din wata an raya wata 😪
https://my.w.tt/PWohUhlPv9.
*Z A K I*
By Khadeeja Candy
9️⃣
A saman kujera na kwana a zaune ina ta kallon Nana tun ina kuka da hawaye har na koma ina ta rare kukan kawai babu hawaye. A kasan gurin Lukman ya kwana. Tun da asubar fari masu sharar asibiti suka tashe Lukman ni kuma suka ce na fita za su gyara gurin. Ba dan babu yadda xan yi ba da ba zan fita ba, domin ina jin kamar idan nai nisa da Nana mutuwa za tai ta barni.
A haka na fito ward din ina jin zuciyata babu dadi, Lukman kuma na ta murja ido alamar bachin be isheshi, kai tsaye gida na nufa kai tsaye domin samawa Nana abunda zata ci da ita da Lukman, wannan karon da kafa na iso kasancewar daga unguwar Clapperto zuwa uduth babu wani tazara sosai ga talaka irina wanda ya saba da tafiyar kasa. Ina janye da hannun Lukman har muka iso kangon gidan. Tsaye nai ina ta tunani ta inda zan fara, rashin lafiyar Nana ta tsaya min a rai har na so min kamar bana da wani sauran kuzari.
“Ataa ya me za mu yi?”
Maganar Lukman ce tasa na dawo daga dogon tunanin da nake rakiyar zuciyata da shi.
“Koko zan siya maka kai da Nana”
“Ni ba zan sha ba”
Ya fada yana mitsintsika ido.
“Saboda me? Ko waina kake so?”
“Aa bana son komai Nana na ke son ta samu lafiya, Ataa ai zata tashi ko? Zata ji sauki ko? Na yi mafarki ta samu sauki tana min magana”
Wani irin tausayinsa da na kaina nd ya lullube ni a lokaci daya, duk yadda na ke shakuwa da Nana nasan Lukman ya fini shakuwa da ita domin shi karamin yaro ne, kuma kusan kullum tare suke zuwa bara tsabanin ni da wani lokacin na ke zuwa wani gurin dabam.
“Zata ji sauki idan kana cin abinci,Nana tana son ta ganka kana cin abinci”
“Haka ta fada miki? Da na yi kwana ta farka?”