Sashe 109
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
“Kurciyarki na burge ni, dan kin yi hakan sai na ji haushi? Ko na miki fada? Ai ko ba amarya kike ba bana da irin wannan rayuwar balle kina Amarya ai ba kyan laifi ko kin kashe dan masu gida”
Nan ma ban ce masa komai ba, yana rikw da hannuna yana watsa da yatsuna har muka isa gaban wani mai siyarda kilishin ya siya mana sannan muka nufi gida.
Kamar yadda ya fada after three days muka koma gida dan yin bankwana da Momy da kuma Nana akan tafiyar da zamu yi Los Vegas, ya bada dama na zabi kasar da na ke son muje amman ban xaba ba saboda ban san komai akan wasu kasashen ba ni dai burina kawai na hau jirgi na san na taba hawa jirgi ko da sau daya ne a rayuwata. Rabar a gida na wuni a nan Nana take labarta min cewar ai kullum a falon Momy take wuni su yi fira saboda kadaici wani lokacin kuma idan zata kwanta Momy na turo mata Amina ko Husna su kwana tare, wani lokaci kuma ita kadai take bachinta.
Na jidadin yadda Momy take kula da mahaifiyata sosai, ita kanta tana jindadin haka. Washe garin ranar muka wuce Abuja daga sokoto, Nasir ne ya hada mana komai a yadda na lura Aliyu be fada min ba, amman na lura da yawan kiransa da yake ya tambaye ni ko shi abu har tafiyar ta hadu. Ya fada min bankwana zai yi ma Mama Fulani sannan mu wuce Lagos domin daga can ne jirginmu zai tashi, be takura ni kan cewar sai yaje da ni na ga Mama Fulani ba ko kuma yi mata bakwana, ni kuma hakan ya fi min sauki da dadi, ko ba komai bana son ganinta ita da Muhseen duk kuwa da ba ni da tabbacin ko zamu tarar da shi a gidan, kwananmu daya a Abuja sannan muka wuce lagos. Daga lagos jirginmu ya tashi da ina ta jin tsoro kamar yadda nai a lokacin da zamu taso daga sokoto zuwa Abuja da kuma zuwa lagos din, domin yadda na ke tsammani da marmarin jirgi sai na tarar ya fi karfin tunani da kuma hankalina, a lokacin da zai daga kana jin motsinsa sosai idan kuma zai sauka kana jin motsin dirarsa a kasa, sai dai idan kana sama baka ma gane tafiya ake sai idan kana kusa da windows, Aliyu a gurin windows ni kuma ina gefensa ya jingina na ni da jikinsa yana ta nuna min kasashe ta cikin wata yar karamar kwanfuta dake lake bayan kujerar da ke gabanmu, da map din yake fada min yanzu muna guri kaza, wani dan biscuit ne aka kawo mana da tea shi kuma ya ce coffee yake so, bayan mun gama sha wata mai uniform ta zo ta dauke sai Aliyu ya sake maida ni jikinsa yana ba ni ragowar biscuit din da ya dauka a plate din a baki ina ci a hankali kamar wata jaririya har bachi yai gaba da ni.
*Khadeeja Candy*
Mun sauka a gajeye domin tafiyar jirgin ta dauke mu awanin masu yawa, na yi zaton idan mun sauka can dare zan gani ko yamma amman sai muka samu safiya ce da alama akwai banbanci yanayi da kuma lokaci.
Muna fitowa daga cikin jirgin Aliyu ya cire jacket din jikinsa ya saka min saboda yanayin sanyin garin, daman doguwar riga ce a jikina sai dan karamin mayadi daya rufe iya kaina ya sauko zuwa wuyana kadan.
Kasa ce ko kuma na ce gari domin tun a jirgi Aliyu ya fada min cewar ba kasa ce gaba daya ba, gari ne dai kamar yadda kasata take nigeria da gari kala kala. Garin da zan iya kira da kasa, kasa ce yanayi mai kyau mutane kowa hada hadarsa yake babu ruwan kowa da kowa ga bin ka'idodi da dokoki ba kamar kasata nigeria ba, hannu ya daga sai ga texi ta zo ya bude min na shiga sannan aka saka kayanmu a bayan motar shi ma ya zagoyo ya shiga inda na ke, ya jani zuwa jikinsa. Ni kan idona na can jikin windows ina ta kallon tituna da kuma manyan binaye da kwaliyar garin gwanin sha'awa har muka isa wata kyakkyawar hotel mai haske da dagon bene mai kyau da daukar hankali.
Na yi zaton irin kudin kasata zai bawa mutumen a lokacin daya ciro wallet dinsa, sai ga shi na ga wasu kudin ne dabam ba irin namu ba.
Bayan ya gama mika masa kudin ya kama hannu muka shiga cikin hotel din shi kuma yana janye da luggage. Da yalshen nasara yai magana da su ya mika musu wani dan karamin kati da nake zaton na banki ne kamar yadda ya fada a lokacin fa yake nuna min passport din da akai min a gida Nigerian a gurin jami'in immigration da ke sokoto, da kuma na dan kasa da shi ma ya saka aka min, mayar masa da katin sukai su ka bashi wata yar takardar da makulli sannan ya juyo muka nufi wani bangare na hotel din, wani gurin ya taba sai wani dan daki ya bude mana mai kamar kumbu muka shiga ni da shi sannan ya taba wata number sai abun ya rufe ya fara tafiya da mu sama, shi kuma ya ciro wayarsa yana ta daukata hoto har muka isa abun ya bude muka fita, ni dai ina rike da hannunsa gaba daya tsoro ya gama kamani domin na lura da gurin tsif yake kamar babu kowa ga shi dakuna ne aka jera masu yawa sosai ko wane da number shi, numbobin dakunan ya rika dubuwa har muka isa gurin wanda aka ba shi key sa, budewa yai ya ya fara shiga sannan n shigo, an share dakin fes kamar wani ne a ciki komai a tsara shi gwaninb sha'awa, ac dakin ya fara kunnawa da wuta sannan ya maida kofar ya rufe ya aje kayanmu a gefen gadon. Bandaki ya shiga yai wanka da alwala ya fito sannan ni ma na shiga, bayan na gama wankan na nufo kofa abunda ban sani ba ashe Aliyu yana nan jikinn kofar labe yana jiran fitowata ina budewa sai yai cikina yana bani tsoro ai ko da gudu na koma ciki sai da yai saurin shigowa ya dauko ni ya fito da ni. Kuka na saka masa na buge masa fuska sai ya aaka min dariya wai daman ya lura da ina jin tsoro. Sai da muka lissafa sallah da ba mu yi tsakanin tasowar mu daga can zuwa nan muka rama su sannan muka dora da suba din da muka tarar a garin.
Bayan mun gama ya taba telephone din gefen gadon yai magana, ba bata lokaci sai ga wani mai uniform ya kwankwasa kofar dakinmu ya miko mana abinci, Aliyu ya karbo ya kawo mana komai a cikin kwali yake sai wata yar miya ce a cikin kwankwa mai shegen ja. Ni dai ban iya cin wasu abubuwan saboda ban saba ba ban ma tana ci ba, Aliyu kan cin abunsa yake da alama ma sun fi masa dadi. Pizza na ci da shawarma sai kuma miyar da na lasa kadan sai na ji bata min dadi ba.
Bayan mun gama mu kai hauk gado mukai bachi gajiya ni da shi, yadda na ke kwana a jikin Nana haka na kwana a jikinsa, ko da muka farka lokaci ya ja sosai bayan mun yi sallah ya cire layin wayarsa ya saka wani layin dabam ya kira Momy yace ta kaiwa Nana muka gaisa sai kuma Mama Fulani ita ya kirata ta daga ya fada mata ya isa lafiya.
“Miyasa ka canja liyin?”
“Ai na nigeria baya yi a kira shi a wata kasar ko wace kasa da kayinta, daman na dade da siyen wannan ba yau na fara zuwa kasar”
Nan ma ban ce masa komai ba, yana rikw da hannuna yana watsa da yatsuna har muka isa gaban wani mai siyarda kilishin ya siya mana sannan muka nufi gida.
Kamar yadda ya fada after three days muka koma gida dan yin bankwana da Momy da kuma Nana akan tafiyar da zamu yi Los Vegas, ya bada dama na zabi kasar da na ke son muje amman ban xaba ba saboda ban san komai akan wasu kasashen ba ni dai burina kawai na hau jirgi na san na taba hawa jirgi ko da sau daya ne a rayuwata. Rabar a gida na wuni a nan Nana take labarta min cewar ai kullum a falon Momy take wuni su yi fira saboda kadaici wani lokacin kuma idan zata kwanta Momy na turo mata Amina ko Husna su kwana tare, wani lokaci kuma ita kadai take bachinta.
Na jidadin yadda Momy take kula da mahaifiyata sosai, ita kanta tana jindadin haka. Washe garin ranar muka wuce Abuja daga sokoto, Nasir ne ya hada mana komai a yadda na lura Aliyu be fada min ba, amman na lura da yawan kiransa da yake ya tambaye ni ko shi abu har tafiyar ta hadu. Ya fada min bankwana zai yi ma Mama Fulani sannan mu wuce Lagos domin daga can ne jirginmu zai tashi, be takura ni kan cewar sai yaje da ni na ga Mama Fulani ba ko kuma yi mata bakwana, ni kuma hakan ya fi min sauki da dadi, ko ba komai bana son ganinta ita da Muhseen duk kuwa da ba ni da tabbacin ko zamu tarar da shi a gidan, kwananmu daya a Abuja sannan muka wuce lagos. Daga lagos jirginmu ya tashi da ina ta jin tsoro kamar yadda nai a lokacin da zamu taso daga sokoto zuwa Abuja da kuma zuwa lagos din, domin yadda na ke tsammani da marmarin jirgi sai na tarar ya fi karfin tunani da kuma hankalina, a lokacin da zai daga kana jin motsinsa sosai idan kuma zai sauka kana jin motsin dirarsa a kasa, sai dai idan kana sama baka ma gane tafiya ake sai idan kana kusa da windows, Aliyu a gurin windows ni kuma ina gefensa ya jingina na ni da jikinsa yana ta nuna min kasashe ta cikin wata yar karamar kwanfuta dake lake bayan kujerar da ke gabanmu, da map din yake fada min yanzu muna guri kaza, wani dan biscuit ne aka kawo mana da tea shi kuma ya ce coffee yake so, bayan mun gama sha wata mai uniform ta zo ta dauke sai Aliyu ya sake maida ni jikinsa yana ba ni ragowar biscuit din da ya dauka a plate din a baki ina ci a hankali kamar wata jaririya har bachi yai gaba da ni.
*Khadeeja Candy*
Mun sauka a gajeye domin tafiyar jirgin ta dauke mu awanin masu yawa, na yi zaton idan mun sauka can dare zan gani ko yamma amman sai muka samu safiya ce da alama akwai banbanci yanayi da kuma lokaci.
Muna fitowa daga cikin jirgin Aliyu ya cire jacket din jikinsa ya saka min saboda yanayin sanyin garin, daman doguwar riga ce a jikina sai dan karamin mayadi daya rufe iya kaina ya sauko zuwa wuyana kadan.
Kasa ce ko kuma na ce gari domin tun a jirgi Aliyu ya fada min cewar ba kasa ce gaba daya ba, gari ne dai kamar yadda kasata take nigeria da gari kala kala. Garin da zan iya kira da kasa, kasa ce yanayi mai kyau mutane kowa hada hadarsa yake babu ruwan kowa da kowa ga bin ka'idodi da dokoki ba kamar kasata nigeria ba, hannu ya daga sai ga texi ta zo ya bude min na shiga sannan aka saka kayanmu a bayan motar shi ma ya zagoyo ya shiga inda na ke, ya jani zuwa jikinsa. Ni kan idona na can jikin windows ina ta kallon tituna da kuma manyan binaye da kwaliyar garin gwanin sha'awa har muka isa wata kyakkyawar hotel mai haske da dagon bene mai kyau da daukar hankali.
Na yi zaton irin kudin kasata zai bawa mutumen a lokacin daya ciro wallet dinsa, sai ga shi na ga wasu kudin ne dabam ba irin namu ba.
Bayan ya gama mika masa kudin ya kama hannu muka shiga cikin hotel din shi kuma yana janye da luggage. Da yalshen nasara yai magana da su ya mika musu wani dan karamin kati da nake zaton na banki ne kamar yadda ya fada a lokacin fa yake nuna min passport din da akai min a gida Nigerian a gurin jami'in immigration da ke sokoto, da kuma na dan kasa da shi ma ya saka aka min, mayar masa da katin sukai su ka bashi wata yar takardar da makulli sannan ya juyo muka nufi wani bangare na hotel din, wani gurin ya taba sai wani dan daki ya bude mana mai kamar kumbu muka shiga ni da shi sannan ya taba wata number sai abun ya rufe ya fara tafiya da mu sama, shi kuma ya ciro wayarsa yana ta daukata hoto har muka isa abun ya bude muka fita, ni dai ina rike da hannunsa gaba daya tsoro ya gama kamani domin na lura da gurin tsif yake kamar babu kowa ga shi dakuna ne aka jera masu yawa sosai ko wane da number shi, numbobin dakunan ya rika dubuwa har muka isa gurin wanda aka ba shi key sa, budewa yai ya ya fara shiga sannan n shigo, an share dakin fes kamar wani ne a ciki komai a tsara shi gwaninb sha'awa, ac dakin ya fara kunnawa da wuta sannan ya maida kofar ya rufe ya aje kayanmu a gefen gadon. Bandaki ya shiga yai wanka da alwala ya fito sannan ni ma na shiga, bayan na gama wankan na nufo kofa abunda ban sani ba ashe Aliyu yana nan jikinn kofar labe yana jiran fitowata ina budewa sai yai cikina yana bani tsoro ai ko da gudu na koma ciki sai da yai saurin shigowa ya dauko ni ya fito da ni. Kuka na saka masa na buge masa fuska sai ya aaka min dariya wai daman ya lura da ina jin tsoro. Sai da muka lissafa sallah da ba mu yi tsakanin tasowar mu daga can zuwa nan muka rama su sannan muka dora da suba din da muka tarar a garin.
Bayan mun gama ya taba telephone din gefen gadon yai magana, ba bata lokaci sai ga wani mai uniform ya kwankwasa kofar dakinmu ya miko mana abinci, Aliyu ya karbo ya kawo mana komai a cikin kwali yake sai wata yar miya ce a cikin kwankwa mai shegen ja. Ni dai ban iya cin wasu abubuwan saboda ban saba ba ban ma tana ci ba, Aliyu kan cin abunsa yake da alama ma sun fi masa dadi. Pizza na ci da shawarma sai kuma miyar da na lasa kadan sai na ji bata min dadi ba.
Bayan mun gama mu kai hauk gado mukai bachi gajiya ni da shi, yadda na ke kwana a jikin Nana haka na kwana a jikinsa, ko da muka farka lokaci ya ja sosai bayan mun yi sallah ya cire layin wayarsa ya saka wani layin dabam ya kira Momy yace ta kaiwa Nana muka gaisa sai kuma Mama Fulani ita ya kirata ta daga ya fada mata ya isa lafiya.
“Miyasa ka canja liyin?”
“Ai na nigeria baya yi a kira shi a wata kasar ko wace kasa da kayinta, daman na dade da siyen wannan ba yau na fara zuwa kasar”