Sashe 14
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Na gyada masa ina hawaye, sannan na saki hannunsa na shiga neman tsohuwar butarmu kuma basasshiya cikin duhun asuba, na yi alwala na mikawa Lukman ragowar ruwan shi ma yai alwala, wani masallaci na bi na gabatar da sallah magariba bata, na yi ma Nana addu'ar neman lafiya, sai kuma na rasa wacce za yi ma Doc Asim, bana son nayi masa mummunar addu'a ya zama ba gaskiya ba ne, domin har yanzu zuciyata tana min kwankwanton cewar ba gaskiya ba ne idan ma ya cire wane amfani zai yi da ita wane amfani zata masa? Mi ma zai yi da ita? Wata kila kuma siyarwa zai gi idan ana siya, waya sani ko wani ya ce ya cire? Amman kuma wa Nana ta sani da har zai sa ayimata haka? Ko shiyasa aka Anty Shukura ta ce mu bar asibitin idan ina son mahaifiyata araye? Shiyasa ta rika girgiza min kai a lokacin da zan saka hannu a takardar nan? Gaskiya ne idan har ba cire mata koda yai ba, mi zai sa yai ta taimakonku haka da yawa magani ma kadai ya kashe mata kudi mai yawa, abinci ma shi yake siya mana, anya idan ba wani abun zai mana taimako haka mai yawa? Haka dai zuciyata tai ta min wasiwasin gaskiya da kuma akasinta a lokaci daya.
Fitowa nai na tsinci kwanon mu a inda mugayen mutanen suka harba mana kayan cin abinci da kafa na wanke na bawa Lukman yaje ya karbo mana koko, bayan ya dawo na sake aikensa ya siyo ma Nana waina mai yaji dan nasan ita ce favorite dinta.
Kadan na kur6a kokon shi ma dan ina jin kamar bana da kuzari ne wai ko zan dan samu karin karfi, na mikawa Lukman sauran kokon ya shanye ba ko suga. Sauran ragowar kudin na fito da su ina kargawa da na hada sai na ga ba su kai ma dubu uku ba gaba daya dubu biyu ne da dari hudu da naira talatin, haka na hada kudin guri daya, na kurawa Lukman ido ina ta kallonsa yana shan koko duk da kasancewar hankalina a gurinsa ya ke ba. Bayan ya gama na dauki wainar da ragowar canjin mu doshi asibitin ni da shi ina tafiya ina jin kamar ana turani gabana sai faduwa yake. Lokacin da muka isa asibitin sai masu gadin ward din suka hana mu shiga, wai ba a zuwa ganin marar lafiya sai da yamma haka dokar asibitin ta ke.
“Ba ganinta na zo ba, abinci na kawo mata kuma ni nake jinyar ta”
Na fada cikin muryarta ta gajiyayyu mutane marasa galihu.
“To bari likitoci su fito sai ki shiga”
Na koma gefe na tsaya kamar yadda na tararda wasu mutanen a tsaye, ina nan zaman jiran likitonci su fito wata Nurse ta fito daga dakin tana tambayar mai jinyar Asma'u Ummaru.
“Ga ni nan”
Na fada da dan kuzarina.
“Shigo ciki ana nemanki”
Na bi bayanta kamar yadda ta umarta Lukman kuma ya biyo sai securiting ya rike shi a nan ya fasa masa ihu kamar zai tashi kunnuwansa a dole ya sake shi ya biyo bayana.
Kusan likito ci hudu ne tsaye akanta ta farka har sun tashe ta ya dan jingina da gadon tana kallonsu bakinta ya bushe sosai har fatar bakinta ta fara kankara kamar wace ta shekara ba ta sha ruwa ba.
“Ke kike jinyarta?”
Daya daga cikin likitocin ya tmabaya yana kallona, wata kila gani yake kamar na yi karama ko kuma kyauwo na yake kallo oho.
“Eh ni ce wani abun ne?”
“Babu wani babba sai ke?”
“Bata da kowa sai ni, ni ma kuma ba ni da kowa sai ita”
“Ina hoton da na rubuta miki jiya kin yi?”
Sai da yai maganar na iya gane daya daga cikin likitocin wanda ya karbe mu ne jiya da muka zo.
“Ban yi ba, sai yau zan je na yi”
“To kije ki yi, yana da kyau a kara tabbatarwa, abu na biyu kuma karki kuskura bata komai ta ci drip din da aka saka mata ba zai bari ta ji yunwa ba, ba za ta ci komai ba sai an yi mata hoton an kara tabbatarwa”
“To na gode”
Na fada cike da sanyin murya, sannan dayan ya miko min wata farar takarda.
“A siyo mata wadannan magungunnan”
“To”
Na fada bayan na karba, sannan na zauna a kujera ina hawaye, su kuma suka nufi wata marar lafiyar dake kusa da mu suna dubata.
“Sannu Nana”
Na fada ina jin kuka kamar zai kubuce min, sai tai murmushin karfin hali ta ce.
“Yauwa, Lukman”
Ta mika masa hannu sai yaje da sauri kusa da gadon ya tsaya yana share hawayen kukan da be gama ba har yanzu na rokewar da wacan securiting yai masa abun ka da mai tsoron mai uniform.
“Mi akai maki? Kin ci abinci”
“Na sha koko, wacan dan sandan ne ya rike ni wa ba zan shigo ba”
Ya fada yana hawan gadon ya zauna, sai ta kalleni.
“Ke kin ci abincin”
Kai kawai na iya gyada mata alamar na ci din, sannan na mike tsaye.
“Ina zaki je Ataa?”
Ta tambaya da yaren buzanci, ni kuma na bata amsa da hausa.
“Zuwa zan yi na tambaya kudin hoton da maganin na ji ko nawa ne”
“Kar ma kije tun da kin san ba kudi da mu ba”
“Ba ki sani ba ko kudin ba shi da yawa, kara dai na tambaya na ji, idan da yawa sosai sai mu hakura”
“To Allah yasa ba bu yawa, akwai ragowar kudi da yawa a hannu hannunki?”
“Eh akwai”
Duk wannan maganar da yaren buzanci mu kai sannan na mike tsaye na fita jiki babu kwari, sai da na tsaya bakin kofar na fadawa security cewar zan dawo kuma ni ce ta dazun mai jinyar marar lafiya gudun kar ya sake hana ni shiga idan na dawo. Wannan karon ban tambayi kowa ba na nufin gurin hoton sai suka rubuta min kudin hoton a jikin takardar dubu takwas da dari biyu wai babban hoto ba ne wanda za a ga duka sassan jikinta a jikin hoton. Sannan na doshi pharmacy na mika musu takardar suka duba suka rubuta min kudin maganin shi ma dubu biyar da yan kai, dukan ya tashi kusan dubu goma sha dubu ba dari uku, ji nai kamar na dora hannuna saman kai na kurma ihu, sai dai idan nai ihun wa zai taimake ni wa zai tausaya min har ya kawo min a gaji, a halin da na ke a yanzu ni kaina tsoron taimakon na ke duk wanda zai yi kare ni da zimmar taimako matukar ba ni na nema ba, na yana da wahala na iya amincewa da shi. Tafiya na ke kaina a kasa idona na zubar da ruwan hawaye, jin na ke kamar fuskata za ta taba kasa saboda maso min da tile din da nake takawa ake ina ganinsa kusa da ni.
Kallon da na ga mutane na min ne yasa na share hawayen na daga kaina sama har na iso ward din na shiga, yadda na bar Nana haka na sameta Lukman na kusa da ita tana ta mata firar mafarkin da yai.
“Kudin na da yawa ko?”
Ta fada tun kan ji ta ji domin yanayin fuskata ya nuna hakan.
“Su na da yawa amman za mu iya samu idan muka yi bara, sai na hada da wandanda suke hannuna”
“Ataa kudin da za muke samu a bara ba su da wani yawan da za mu iya siyen magani”
“Zan yi kokarin na samo su cikin sati biyu, ni da Lukman za mu yi In-Sha-Allah za mu samu kuma za ki samu lafiya Nana”
“Ko dai mu koma asibitin wacan likitan?”
“Aa ba sai mun koma ba, ba kuma za mu koma ba har a bada”
Na fada cike da zafin rai.
“Amman ya taimaka mana ai”
“Eh ya taimaka mana ya ceto ranki daga saran da maciji yai miki, sai dai yanzu tiyatar da yai miki duk ita ce ta ja mana wannan matsalar”
“Cewa sukai wani abu ya samu tiyatar ne?”
“Aa cewa sukao maganin da kika sha ba shi ya kamata koli sha ba wai likitan be kware sosai ba”
A take naga hankalinta ya tashi, har fuskarta ta kara boyewa, nasan da na fada mata gaskiyar cewar kodarta aka cire wata kila zan iya rasata ma a nan take. Matsawa nai kusa da ita ina kokarin kwantar mata da hankali.
“Nana ki kwantar da hankalinki zan samu kudi zan biya a baki magani, kuma za ki warke za ki tashi, domin sun ce idan aka ba ki maganin za ki iya jin sauki a take”
Hawayen idonta ta share tana sauke ajiyar zuciya tare da saka dayan hannunta ta dafe gefen hakarkarinta.
“Nawa ne kudin maganin?”
“Dubu takwas ne kuma akwai ragowar dubu biyar a hannuna, kin ga dubu uku kawai za mu samo”
Na mata karya saboda hankalinta ya kwanta. sai ta lumshe ido hawaye suka sauko mata, ashe zubar hawayen mahaifiya yana da zafi da daraja a idon 'ya'yanta, domin a take na ji duk wani kuka nawa da na ke kokarin tarewa ya tafi sai na nemi rashin kuzarin na rasa, wani karfi da shaukin neman mafitar inda zan tsayarda da zubar hawayenta ya cika ni. Mikewa nai tsaye na juya da zimmar tafiya sai na ji Lukman ya kira ni.
“Ataa zan biki ni ma zan yi baran”
Fitowa nai na tsinci kwanon mu a inda mugayen mutanen suka harba mana kayan cin abinci da kafa na wanke na bawa Lukman yaje ya karbo mana koko, bayan ya dawo na sake aikensa ya siyo ma Nana waina mai yaji dan nasan ita ce favorite dinta.
Kadan na kur6a kokon shi ma dan ina jin kamar bana da kuzari ne wai ko zan dan samu karin karfi, na mikawa Lukman sauran kokon ya shanye ba ko suga. Sauran ragowar kudin na fito da su ina kargawa da na hada sai na ga ba su kai ma dubu uku ba gaba daya dubu biyu ne da dari hudu da naira talatin, haka na hada kudin guri daya, na kurawa Lukman ido ina ta kallonsa yana shan koko duk da kasancewar hankalina a gurinsa ya ke ba. Bayan ya gama na dauki wainar da ragowar canjin mu doshi asibitin ni da shi ina tafiya ina jin kamar ana turani gabana sai faduwa yake. Lokacin da muka isa asibitin sai masu gadin ward din suka hana mu shiga, wai ba a zuwa ganin marar lafiya sai da yamma haka dokar asibitin ta ke.
“Ba ganinta na zo ba, abinci na kawo mata kuma ni nake jinyar ta”
Na fada cikin muryarta ta gajiyayyu mutane marasa galihu.
“To bari likitoci su fito sai ki shiga”
Na koma gefe na tsaya kamar yadda na tararda wasu mutanen a tsaye, ina nan zaman jiran likitonci su fito wata Nurse ta fito daga dakin tana tambayar mai jinyar Asma'u Ummaru.
“Ga ni nan”
Na fada da dan kuzarina.
“Shigo ciki ana nemanki”
Na bi bayanta kamar yadda ta umarta Lukman kuma ya biyo sai securiting ya rike shi a nan ya fasa masa ihu kamar zai tashi kunnuwansa a dole ya sake shi ya biyo bayana.
Kusan likito ci hudu ne tsaye akanta ta farka har sun tashe ta ya dan jingina da gadon tana kallonsu bakinta ya bushe sosai har fatar bakinta ta fara kankara kamar wace ta shekara ba ta sha ruwa ba.
“Ke kike jinyarta?”
Daya daga cikin likitocin ya tmabaya yana kallona, wata kila gani yake kamar na yi karama ko kuma kyauwo na yake kallo oho.
“Eh ni ce wani abun ne?”
“Babu wani babba sai ke?”
“Bata da kowa sai ni, ni ma kuma ba ni da kowa sai ita”
“Ina hoton da na rubuta miki jiya kin yi?”
Sai da yai maganar na iya gane daya daga cikin likitocin wanda ya karbe mu ne jiya da muka zo.
“Ban yi ba, sai yau zan je na yi”
“To kije ki yi, yana da kyau a kara tabbatarwa, abu na biyu kuma karki kuskura bata komai ta ci drip din da aka saka mata ba zai bari ta ji yunwa ba, ba za ta ci komai ba sai an yi mata hoton an kara tabbatarwa”
“To na gode”
Na fada cike da sanyin murya, sannan dayan ya miko min wata farar takarda.
“A siyo mata wadannan magungunnan”
“To”
Na fada bayan na karba, sannan na zauna a kujera ina hawaye, su kuma suka nufi wata marar lafiyar dake kusa da mu suna dubata.
“Sannu Nana”
Na fada ina jin kuka kamar zai kubuce min, sai tai murmushin karfin hali ta ce.
“Yauwa, Lukman”
Ta mika masa hannu sai yaje da sauri kusa da gadon ya tsaya yana share hawayen kukan da be gama ba har yanzu na rokewar da wacan securiting yai masa abun ka da mai tsoron mai uniform.
“Mi akai maki? Kin ci abinci”
“Na sha koko, wacan dan sandan ne ya rike ni wa ba zan shigo ba”
Ya fada yana hawan gadon ya zauna, sai ta kalleni.
“Ke kin ci abincin”
Kai kawai na iya gyada mata alamar na ci din, sannan na mike tsaye.
“Ina zaki je Ataa?”
Ta tambaya da yaren buzanci, ni kuma na bata amsa da hausa.
“Zuwa zan yi na tambaya kudin hoton da maganin na ji ko nawa ne”
“Kar ma kije tun da kin san ba kudi da mu ba”
“Ba ki sani ba ko kudin ba shi da yawa, kara dai na tambaya na ji, idan da yawa sosai sai mu hakura”
“To Allah yasa ba bu yawa, akwai ragowar kudi da yawa a hannu hannunki?”
“Eh akwai”
Duk wannan maganar da yaren buzanci mu kai sannan na mike tsaye na fita jiki babu kwari, sai da na tsaya bakin kofar na fadawa security cewar zan dawo kuma ni ce ta dazun mai jinyar marar lafiya gudun kar ya sake hana ni shiga idan na dawo. Wannan karon ban tambayi kowa ba na nufin gurin hoton sai suka rubuta min kudin hoton a jikin takardar dubu takwas da dari biyu wai babban hoto ba ne wanda za a ga duka sassan jikinta a jikin hoton. Sannan na doshi pharmacy na mika musu takardar suka duba suka rubuta min kudin maganin shi ma dubu biyar da yan kai, dukan ya tashi kusan dubu goma sha dubu ba dari uku, ji nai kamar na dora hannuna saman kai na kurma ihu, sai dai idan nai ihun wa zai taimake ni wa zai tausaya min har ya kawo min a gaji, a halin da na ke a yanzu ni kaina tsoron taimakon na ke duk wanda zai yi kare ni da zimmar taimako matukar ba ni na nema ba, na yana da wahala na iya amincewa da shi. Tafiya na ke kaina a kasa idona na zubar da ruwan hawaye, jin na ke kamar fuskata za ta taba kasa saboda maso min da tile din da nake takawa ake ina ganinsa kusa da ni.
Kallon da na ga mutane na min ne yasa na share hawayen na daga kaina sama har na iso ward din na shiga, yadda na bar Nana haka na sameta Lukman na kusa da ita tana ta mata firar mafarkin da yai.
“Kudin na da yawa ko?”
Ta fada tun kan ji ta ji domin yanayin fuskata ya nuna hakan.
“Su na da yawa amman za mu iya samu idan muka yi bara, sai na hada da wandanda suke hannuna”
“Ataa kudin da za muke samu a bara ba su da wani yawan da za mu iya siyen magani”
“Zan yi kokarin na samo su cikin sati biyu, ni da Lukman za mu yi In-Sha-Allah za mu samu kuma za ki samu lafiya Nana”
“Ko dai mu koma asibitin wacan likitan?”
“Aa ba sai mun koma ba, ba kuma za mu koma ba har a bada”
Na fada cike da zafin rai.
“Amman ya taimaka mana ai”
“Eh ya taimaka mana ya ceto ranki daga saran da maciji yai miki, sai dai yanzu tiyatar da yai miki duk ita ce ta ja mana wannan matsalar”
“Cewa sukai wani abu ya samu tiyatar ne?”
“Aa cewa sukao maganin da kika sha ba shi ya kamata koli sha ba wai likitan be kware sosai ba”
A take naga hankalinta ya tashi, har fuskarta ta kara boyewa, nasan da na fada mata gaskiyar cewar kodarta aka cire wata kila zan iya rasata ma a nan take. Matsawa nai kusa da ita ina kokarin kwantar mata da hankali.
“Nana ki kwantar da hankalinki zan samu kudi zan biya a baki magani, kuma za ki warke za ki tashi, domin sun ce idan aka ba ki maganin za ki iya jin sauki a take”
Hawayen idonta ta share tana sauke ajiyar zuciya tare da saka dayan hannunta ta dafe gefen hakarkarinta.
“Nawa ne kudin maganin?”
“Dubu takwas ne kuma akwai ragowar dubu biyar a hannuna, kin ga dubu uku kawai za mu samo”
Na mata karya saboda hankalinta ya kwanta. sai ta lumshe ido hawaye suka sauko mata, ashe zubar hawayen mahaifiya yana da zafi da daraja a idon 'ya'yanta, domin a take na ji duk wani kuka nawa da na ke kokarin tarewa ya tafi sai na nemi rashin kuzarin na rasa, wani karfi da shaukin neman mafitar inda zan tsayarda da zubar hawayenta ya cika ni. Mikewa nai tsaye na juya da zimmar tafiya sai na ji Lukman ya kira ni.
“Ataa zan biki ni ma zan yi baran”