Sashe 95
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Ina fatar mijinki ne na har abada, kuma ina fatar zabin Aliyu ya zame miki alheri a rayuwarki, rayuwar da na ke miki fatan samu ina fatar ita ce a yanzu take rabarki, kuma fatar wannan zabin da kika yi ba zai raba kan iyalan gidan nan ba”
A cikin raina na amsa da amin sannan na kwantar da kaina jikinta. Na kara fashewa da kukan, sai da nai mai isata na samu natsuwar ruhi da zuciya sannan na tashi na shirya na wuce makarantar islamiya, yau a inda na zauna jiya na zauna kusa da wata budurwa mai far'a wacce na zauna da ita jiya, sosai na maida hankalina gurin karatu amman na kasa karanta komai sai tunanin abunda ya faru nake har aka kusa ta shi.
“Yau ba za ki biya ba?”
Na dago daga tunanin da nake na kalleta.
“Zan biya”
“Na ga an kusa tashi ne, ban ma san sunanki ba”
“Sunana Aisha”
“Okay ni kuma sunana Asma'u”
“Kai ashe ke mamana ce”
“Ina da sunan Mama kenan?”
“Eh sunan Mamana ne”
“Eyee daga yau Mama zaki rika ce min”
Na yi murmushi tare da tashi na nufi gurin da malamin yake zaune ana biyawa, na biya harufan da na iya ya kara min wani na taso na dawo inda na ke ma zauna sai yarinyar ta ba ni yasin kanzo wai ko ina so, rai na biya dan haka na karba ina lasawa na ji yaji kamar zan hauka ce da sauri na mika mata ragowar ina fiddo halshena waje ,sai ta saka min dariya ita da wata yarinya da ke gefenta.
“Aisha Aliyu ta so ana kiranki”
Malamin nan da Aliyu ya danka ni hannunsa ranar ne ya shigo yana fadin hakan, ni kuma ban kula ba domin ban dauka da ni yake ba duk kuwa da kasancewar ni yake kallo kuma na san gurin saka sunan form din daya tambayi ni Aisha Umar na fada masa.
“Aisha Aliyu”
Ya maimaita yana kallona sai na nuna kaina.
“Ni...?”
“Eh ta so ana kiranki”
Na tashi ina ta tandar baki saboda yajin na fito na biyo bayan malamin sai ya juyo ya ce min.
“Dauko littafanki?”
Ba musu na juya na je na dauko na biho bayansa, ina ta mamakin dalilin kirana Aisha Aliyu da yai.
“Kije waje ana jiranki”
Na nufi gate din cike da tunanin mai kiran nawa a wannan lokacin da ba a tashi a makaranta ba. Ina fitowa ya hango Aliyu jikin motarsa sanye da kakanan kaya yana kallon inda na ke tsaye da alama daman ni yake jiran na karaso, wani irin tattausan murmushi da ban taba sanin yana tare da shi ba ya rika aiko min yana min wani irin kallo mai wuyar fassara, yayi masifar kyau saboda Murmushin ya kawata fuskarsa har sai da ya saka gaba faduwa, kasa karasawa nai a na tsaya a gurin gate din ina kallonsa sai ya gyara tsayuwarsa ya rumgume hannayensa a kirji yana ta kallona kamar zai cinye ni, daga bisani ya dago daga jikin motar ya daso inda na ke, kamin ya karaso nai kasa da kaina kunyarsa ta rufe kamshin turarensa kuma ya zagaye ni siffar zatinsa ta hana ni sukuni. Hannu ya miko min na san be saba taba ni ba dan haka na mika masa littafan hannuna sai yai gaba ya bar a gurin, sai da ya isa gurun motar ya bude front ya juyo ya kalleni sannan na fara takawa da sauri gudun kar wani ya fito ya hango mu daga dalibai ko malaman makarantar. Ina isa na shiga na zauna sai ya rufe motar ya bude gidan baya ya saka littafan nawa ya zagayo mazaunin direba ya shiga yai mata keys muka hau babban titin unguwar, na yi zaton ko gida zai maida sai na ga mun wuce hanyar gida sai tafiya yake da ni, ni ko sai tandar baki na ke saboda yajin da na ke ji tun ina yi a hankali har sautin ya fara fitowa, da sauri ya maido da hankalinsa gurina kamar ba tukin mota yake ba ko kuma na ce ba a kan titi mike ba.
“Kin ji ciwo ne?”
Na kasa magana.
“Ko yaji kika ci?”
Na gyada masa kai alamar eh, sai ya faka motarsa gefen titi ya fita daga motar ya tsallaka titi ya shiga wani shagon be dade ba ya fito rike da leda ya dawo cikin motar, da kansa ya bude ledar ya fiddo gorar ruwan mai sanyi ya bude ta ya miko min.
“Na goge”
Na fada ina kokarin karbar ruwan, sai ya saka min murmushi as respond ya kai ruwan a bakina na sha ka dan na rike sauran.
“Sun ishe ki?”
Ya tambaya yana ta kallona kamar mai kula da yadda na ke shan ruwa, sai na gyada masa kai hannunsa ya kai ya karbi ruwan ya tashi motar da hannunaa daya dayan hannun kuma yana kurba ruwan. Yawo ya rika yi da ni a cikin garin sokoto wasu unguwannin na sansu wasu kuma ban sani ba, ni dai ban tambaye shi inda za muje ba nawa idone kawai. Sai da muka yi nisa sosai sannan ya faka motarsa gefen titi ya kwantar da kujerarsa ya juyo da fuskarsa gafena yana kallona, na yi zaton wani abun zai yi ko ya ce sai na ji shiru be ce min komai sai idonsa da ya tsare da su, mi kuma na kasa daga kaina na kallin gefen da yake ma balle kuma na iya hadu ido da shi.
“Ki yi hakurina da kallona, yau ji na ke kamar na hade ki ji na ke kamar na bude miki zuciyata ki shige na rufe, ji na ke kamar a cikin jinina aka halittoki, komai ya zo min a babin da ban yi zato ba, ban san wace karmar zan fada da zata gamsar da ke irin kaunar ki da na ji a raina ba”
Ji nai kaina yayi mugun girma, ban tana jin kunyar Aliyu kamar na yau ba, ban taba jin wani kalami mai girma daga bakinsa kamar wannan ba, bayan wacan furucin da yai min yau ma ya kara min wani wanda ke dora wacan a babin da zai tabbatar da wacan zancen na farko, a wacan karon na yi zaton yana rokona ne saboda kare Momy da son cika mata burinta, sai dai kalaman da yai min a yanzu da irin shaukin da yake ya sauya tunani na.
“Kar a tashi makaranta.....”
Na fada numfashi na fita daker kamar wacce aka taushewa zuciya.
“Na fadawa Malamin ku gida zan kai ki fita za ku yi da Momy”
“Amman yanzu an kusa tashi ai....”
Na furta still numfashin nawa na gargada, sai ya sake dauko ruwan da ke tsakanin ni da shi ya bude robar ruwan ya miko min.
“Sha”
Na karba da sauri na kai robar ruwan a bakina ina ta sha kamar ba zan daina ba har sai da na soma tsarkewa sai yai saurin rike robar ya ciro tissue ya mikon.
“Sannu”
Na karba na goge ruwan da suka zuba jikin hijab dina sannan ta zuke gulashin motar na wurgar da shi waje, gaba daya na tsawwala ina ta jin motar ta mana kada kuma kunyarsa ta rufe duk na bi na rude. Shi kanshi ya lura da hakan, sai ya gyara kujerar ya soma toka motar muka hau titi. Kadan kadan yake tukin har muka isa gida, a bakin gate din ya faka motarsa, ya bude motar ya fita ya zagoyo gefena ya bude min motar
“Babyna fito ki shiga gida”
Na san ma'anar Baby yana nufin jaririya mace, wato yana nufin ni jaririyarsa ce kenan. Na fito daga motar kaina a kasa sai da ya rufe motar sannan ya bude gidan baya ya dauko min tittafaina ya mika min sai da na mika hannuna an karba sai yaki saki
“Thank you so much Love, kin cece ni na zan tana manta wannan alfarmar ba, kin cancanci komai daga gareni I love you so much”
Har zan sakar masa littafan sai yai saurin sakar min ya tsaya yana kallona har na shige cikin gidan. Ban taba dawowa a irin wannan lokacin ba ana ciran sallah magariba, idan ma Nana ta tambaye ni ban san mi zan ce mata ba. Ina shiga bq din sai na samu Nana bata nan sai dai dakin a bude yake cikina na shiga na cire uniform dina ya shiga bandaki nai alwala, ina cikin Sallah Nana ga shigo dakin ita ma ta wuce bandakin tai alwala ko da ta fito na sallame ina tasbihi da hannuna.
“Tun dazun kika dawo ko? Daman Hajiya ta ce kila ma kin dawo kika zauna a dakin ke kadai kina jin kunyar shigowa bangarenta”
Na yi murmushi cike da jindadi domin na san idan ta san na kai magariba dole ta tambaya abunda ya tsayar da ni kuma ban san abunda zan ce mata ba.
“Hajiya ce ta aiko aka kiranin na je can muka yi hira wai na daina zama ni kadai a nan”
“Allah sarki Momy ai tana da kirki”
“Tana da kirki sosai kam, kin yi dacen suruka indai abun ya bi haka”
Wata kunyar ce ta rufe ni ban taba tsammanin idan na yi wa mutun irin wannan maganar kunya tana rufe ba duk kuwa da kasancewar uwata ce amman na ji kunyarta sosai.
ALIYU POV.
ido ya kura mata yana ta kallon tafiyarta har ta shige ciki, wani irin abun yake ji marar misaltuwa lallai ya yarda kuma ya tabbatar a yanzu kam yana son Ataa so ba na wasa ba.
Motarsa ya shiga ya dauki hanyar gidansa, sai da ya shiga ya faka motarsa sannan ya fito ya doshi masallacin unguwar yai gabatar da sallah magariba da ya fito sai ya tsaya bakin masallacin sai da liman ya fito sannan ya yai saurin taronsa ya mika masa hannu suka gaisa.
“Ah Alh Aliyu ya gida ya aiki”
Haka yake kiransa Alhaji Aliyu ba dan komai sai dan tarin dukiyar dake saka kowa ganin kimarsa da jin kunyar kiran sunansa kai tsaye.
“Al-hamdulillah”
Aliyu ya amsa sannan ya saka hannunsa aljihu ya ciro duka kudin aljihu da na Wallet dinsa ya mikawa liman din.
A cikin raina na amsa da amin sannan na kwantar da kaina jikinta. Na kara fashewa da kukan, sai da nai mai isata na samu natsuwar ruhi da zuciya sannan na tashi na shirya na wuce makarantar islamiya, yau a inda na zauna jiya na zauna kusa da wata budurwa mai far'a wacce na zauna da ita jiya, sosai na maida hankalina gurin karatu amman na kasa karanta komai sai tunanin abunda ya faru nake har aka kusa ta shi.
“Yau ba za ki biya ba?”
Na dago daga tunanin da nake na kalleta.
“Zan biya”
“Na ga an kusa tashi ne, ban ma san sunanki ba”
“Sunana Aisha”
“Okay ni kuma sunana Asma'u”
“Kai ashe ke mamana ce”
“Ina da sunan Mama kenan?”
“Eh sunan Mamana ne”
“Eyee daga yau Mama zaki rika ce min”
Na yi murmushi tare da tashi na nufi gurin da malamin yake zaune ana biyawa, na biya harufan da na iya ya kara min wani na taso na dawo inda na ke ma zauna sai yarinyar ta ba ni yasin kanzo wai ko ina so, rai na biya dan haka na karba ina lasawa na ji yaji kamar zan hauka ce da sauri na mika mata ragowar ina fiddo halshena waje ,sai ta saka min dariya ita da wata yarinya da ke gefenta.
“Aisha Aliyu ta so ana kiranki”
Malamin nan da Aliyu ya danka ni hannunsa ranar ne ya shigo yana fadin hakan, ni kuma ban kula ba domin ban dauka da ni yake ba duk kuwa da kasancewar ni yake kallo kuma na san gurin saka sunan form din daya tambayi ni Aisha Umar na fada masa.
“Aisha Aliyu”
Ya maimaita yana kallona sai na nuna kaina.
“Ni...?”
“Eh ta so ana kiranki”
Na tashi ina ta tandar baki saboda yajin na fito na biyo bayan malamin sai ya juyo ya ce min.
“Dauko littafanki?”
Ba musu na juya na je na dauko na biho bayansa, ina ta mamakin dalilin kirana Aisha Aliyu da yai.
“Kije waje ana jiranki”
Na nufi gate din cike da tunanin mai kiran nawa a wannan lokacin da ba a tashi a makaranta ba. Ina fitowa ya hango Aliyu jikin motarsa sanye da kakanan kaya yana kallon inda na ke tsaye da alama daman ni yake jiran na karaso, wani irin tattausan murmushi da ban taba sanin yana tare da shi ba ya rika aiko min yana min wani irin kallo mai wuyar fassara, yayi masifar kyau saboda Murmushin ya kawata fuskarsa har sai da ya saka gaba faduwa, kasa karasawa nai a na tsaya a gurin gate din ina kallonsa sai ya gyara tsayuwarsa ya rumgume hannayensa a kirji yana ta kallona kamar zai cinye ni, daga bisani ya dago daga jikin motar ya daso inda na ke, kamin ya karaso nai kasa da kaina kunyarsa ta rufe kamshin turarensa kuma ya zagaye ni siffar zatinsa ta hana ni sukuni. Hannu ya miko min na san be saba taba ni ba dan haka na mika masa littafan hannuna sai yai gaba ya bar a gurin, sai da ya isa gurun motar ya bude front ya juyo ya kalleni sannan na fara takawa da sauri gudun kar wani ya fito ya hango mu daga dalibai ko malaman makarantar. Ina isa na shiga na zauna sai ya rufe motar ya bude gidan baya ya saka littafan nawa ya zagayo mazaunin direba ya shiga yai mata keys muka hau babban titin unguwar, na yi zaton ko gida zai maida sai na ga mun wuce hanyar gida sai tafiya yake da ni, ni ko sai tandar baki na ke saboda yajin da na ke ji tun ina yi a hankali har sautin ya fara fitowa, da sauri ya maido da hankalinsa gurina kamar ba tukin mota yake ba ko kuma na ce ba a kan titi mike ba.
“Kin ji ciwo ne?”
Na kasa magana.
“Ko yaji kika ci?”
Na gyada masa kai alamar eh, sai ya faka motarsa gefen titi ya fita daga motar ya tsallaka titi ya shiga wani shagon be dade ba ya fito rike da leda ya dawo cikin motar, da kansa ya bude ledar ya fiddo gorar ruwan mai sanyi ya bude ta ya miko min.
“Na goge”
Na fada ina kokarin karbar ruwan, sai ya saka min murmushi as respond ya kai ruwan a bakina na sha ka dan na rike sauran.
“Sun ishe ki?”
Ya tambaya yana ta kallona kamar mai kula da yadda na ke shan ruwa, sai na gyada masa kai hannunsa ya kai ya karbi ruwan ya tashi motar da hannunaa daya dayan hannun kuma yana kurba ruwan. Yawo ya rika yi da ni a cikin garin sokoto wasu unguwannin na sansu wasu kuma ban sani ba, ni dai ban tambaye shi inda za muje ba nawa idone kawai. Sai da muka yi nisa sosai sannan ya faka motarsa gefen titi ya kwantar da kujerarsa ya juyo da fuskarsa gafena yana kallona, na yi zaton wani abun zai yi ko ya ce sai na ji shiru be ce min komai sai idonsa da ya tsare da su, mi kuma na kasa daga kaina na kallin gefen da yake ma balle kuma na iya hadu ido da shi.
“Ki yi hakurina da kallona, yau ji na ke kamar na hade ki ji na ke kamar na bude miki zuciyata ki shige na rufe, ji na ke kamar a cikin jinina aka halittoki, komai ya zo min a babin da ban yi zato ba, ban san wace karmar zan fada da zata gamsar da ke irin kaunar ki da na ji a raina ba”
Ji nai kaina yayi mugun girma, ban tana jin kunyar Aliyu kamar na yau ba, ban taba jin wani kalami mai girma daga bakinsa kamar wannan ba, bayan wacan furucin da yai min yau ma ya kara min wani wanda ke dora wacan a babin da zai tabbatar da wacan zancen na farko, a wacan karon na yi zaton yana rokona ne saboda kare Momy da son cika mata burinta, sai dai kalaman da yai min a yanzu da irin shaukin da yake ya sauya tunani na.
“Kar a tashi makaranta.....”
Na fada numfashi na fita daker kamar wacce aka taushewa zuciya.
“Na fadawa Malamin ku gida zan kai ki fita za ku yi da Momy”
“Amman yanzu an kusa tashi ai....”
Na furta still numfashin nawa na gargada, sai ya sake dauko ruwan da ke tsakanin ni da shi ya bude robar ruwan ya miko min.
“Sha”
Na karba da sauri na kai robar ruwan a bakina ina ta sha kamar ba zan daina ba har sai da na soma tsarkewa sai yai saurin rike robar ya ciro tissue ya mikon.
“Sannu”
Na karba na goge ruwan da suka zuba jikin hijab dina sannan ta zuke gulashin motar na wurgar da shi waje, gaba daya na tsawwala ina ta jin motar ta mana kada kuma kunyarsa ta rufe duk na bi na rude. Shi kanshi ya lura da hakan, sai ya gyara kujerar ya soma toka motar muka hau titi. Kadan kadan yake tukin har muka isa gida, a bakin gate din ya faka motarsa, ya bude motar ya fita ya zagoyo gefena ya bude min motar
“Babyna fito ki shiga gida”
Na san ma'anar Baby yana nufin jaririya mace, wato yana nufin ni jaririyarsa ce kenan. Na fito daga motar kaina a kasa sai da ya rufe motar sannan ya bude gidan baya ya dauko min tittafaina ya mika min sai da na mika hannuna an karba sai yaki saki
“Thank you so much Love, kin cece ni na zan tana manta wannan alfarmar ba, kin cancanci komai daga gareni I love you so much”
Har zan sakar masa littafan sai yai saurin sakar min ya tsaya yana kallona har na shige cikin gidan. Ban taba dawowa a irin wannan lokacin ba ana ciran sallah magariba, idan ma Nana ta tambaye ni ban san mi zan ce mata ba. Ina shiga bq din sai na samu Nana bata nan sai dai dakin a bude yake cikina na shiga na cire uniform dina ya shiga bandaki nai alwala, ina cikin Sallah Nana ga shigo dakin ita ma ta wuce bandakin tai alwala ko da ta fito na sallame ina tasbihi da hannuna.
“Tun dazun kika dawo ko? Daman Hajiya ta ce kila ma kin dawo kika zauna a dakin ke kadai kina jin kunyar shigowa bangarenta”
Na yi murmushi cike da jindadi domin na san idan ta san na kai magariba dole ta tambaya abunda ya tsayar da ni kuma ban san abunda zan ce mata ba.
“Hajiya ce ta aiko aka kiranin na je can muka yi hira wai na daina zama ni kadai a nan”
“Allah sarki Momy ai tana da kirki”
“Tana da kirki sosai kam, kin yi dacen suruka indai abun ya bi haka”
Wata kunyar ce ta rufe ni ban taba tsammanin idan na yi wa mutun irin wannan maganar kunya tana rufe ba duk kuwa da kasancewar uwata ce amman na ji kunyarta sosai.
ALIYU POV.
ido ya kura mata yana ta kallon tafiyarta har ta shige ciki, wani irin abun yake ji marar misaltuwa lallai ya yarda kuma ya tabbatar a yanzu kam yana son Ataa so ba na wasa ba.
Motarsa ya shiga ya dauki hanyar gidansa, sai da ya shiga ya faka motarsa sannan ya fito ya doshi masallacin unguwar yai gabatar da sallah magariba da ya fito sai ya tsaya bakin masallacin sai da liman ya fito sannan ya yai saurin taronsa ya mika masa hannu suka gaisa.
“Ah Alh Aliyu ya gida ya aiki”
Haka yake kiransa Alhaji Aliyu ba dan komai sai dan tarin dukiyar dake saka kowa ganin kimarsa da jin kunyar kiran sunansa kai tsaye.
“Al-hamdulillah”
Aliyu ya amsa sannan ya saka hannunsa aljihu ya ciro duka kudin aljihu da na Wallet dinsa ya mikawa liman din.