Sashe 43
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Karki da ke ta Mama, za ki dauki alhakinta ne kawai, ba ki iya ganin laifin Aliyu sai dai wasu, bayan kuma shi ne mai laifin, kuma Wallahi sai na bashi mamaki”
Ya fada sannan ya juyo ya kalleni.
“Wuce daga nan”
Da saurina na fice daga falon har ina tuntube kamar zan fadi, abun ka da mai shegen tsoro haka nai ta kwara ido a garejin ina ta jiran wani daga cikin yayanta ko kuma ita kanta ta zo ta dake ni amman shiru babu wanda ya zo har dare yai, ban fita karbar abinci a part din Mama Fulani ba, sai na je part din Ammy a can na ci abincin dare na sannan na dawo garejin na kwanta abuna na kwana har safe. Kamar yadda na saba da wuri na farka ina gama sallah na shiga na gyara falon Mama Fulani sannan na je part din Ammy na gyara kamar yadda na saba, bayan na gama Mama Fulani ta ce na dauko gurina aka zuba min abincina, har zan fito sai ya Muhseen ya kirani ya kara min da na shi na fito ina ta murna, a garden na zauna na cinye abuna sannan na dauki plate din naje na wanke na kawo gareji na aje. After like one hour Rukaiyah ta shigo garejin tana rike da makullin mota.
“Ke ta so muje ki riko min kaya”
Da sauri na taso na biyo bayanta a zato daga mota zan riko mata su ko kuma a cikin gida zan dauko na saka mata a mota sai na ji ta ce.
“Ki shiga gidan baya”
Juyawa nai da zimmar komawa gareji na dauko Hijab dina sai ta daka min tsawa.
“Ke ina za ki je?”
“Hijab dina zan dauko”
“Ba Hijab ba ubanki shiga mota muje”
Da sauri na nufi motar na bude na shiga daga ni sai lace dina na jiya da sai dankwali, sai da na rufe motar sannan ta shiga mazaunin direba ta tashi motar muka fice, ni dai ina zaune a baya ina ta kalle-kalle har muka isa wani katafaren shago irin wanda na ke gani a tv nan, wanda komai da komai ana saida a ciki kuma komai bangaren dabam, ni kallo ya hanani rufe motar har sai da naji an dangware ni da karfi.
“Bakauyar banza rufe min mota”
Sai na saka hannu biyu na rufe. Na bi bayanta muna ta taka dan karamin matakalin har muka isa gaban babbar kofar wacce wasu masu uniform suke budewa mutum idan zai shiga, wani dan kwando taja ta mika min shi.
“Ja wannan mu tafi duk abunda na nuna miki ki dauka”
Na saka hannu na karba ina turawa, wai ita ala dole sai ta nuna ni din yar aikin gidansu ce ta sha wani bakin gilashi a fuska tana sanye da yadi babu mayafi a jikinta, ni kuwa duk sai naji na takura da rashin mayafin duk kuwa da na lura kusan rabin matan da suke shigowa shopping din basa da mayafi kuma kowa be kula ba, duk inda muka bi kallona ake nasan wannan baya rasa nasaba da gashin kaina da nai masa tsoro daya na ya sauko har gurin mazaunaina, da kuma haskena ga kyau kamar wata balaraba. Turin kwandon be dame ni ba dan ji nake kamar ina tuka mota duk inda na ga dama juyashi na ke ina jindadi. Dauko wannan dauko wancan haka take bani umarni ina bi kamar bawa da uban gidansa, muna isa sashen kayan dadi ta umarce ni na dauko madara ina kai hannuna sai na ji an rike hannun, da sauri na kalli gafena.
“Na kama ki”
Kamal ne sanye da kananan kaya fuskarsa da murmushi kamar kullum ni ma Murmushin nai sai kuma nai saurin kallon Rukaiya wacce ita ma murmushin take sakar masa.
“Rukaiya shopping kuka zo”
“Eh Wallahi har ma mun kare daman ba da yawa zan yi ba ya aikin?”
“Lafiya kalau, sai ki ba ni aron Mamanar tawa ta raka ni shopping tun da kun kare, kadan na gama sai mu koma gida tare”
Sakin baki tai kamar zata ce masa ba mu kare ba, sai kuma ta ga kamar be dace tai karya ba, dan haka tai murmushin yake.
“Ba matsala”
24
“Thank you, idan kin je gida ki fadawa Mama Fulani ni na areta kuma zan kawo ta nan ba da jimawa ba”
“Okay ayi shopping lafiya”
Taja kwandon daga hannuna tai gaba a abunta kamar tana jin haushi. Sai da ta wuce sannan ya dawo da dubansa gurina ya ce.
“Shiga ciki na turaki”
Ba shiri na bude baki.
“Aa mutane suna kallon mu, kuma mutane ba sa shiga cikin kwadon zuba kaya ai, za su mana fada”
“Ko?”
Ya fada yana murmushin kan na sake cewa wani abu ya dauke ni ya zuba a cikin kwandon yana dariya, ina kokarin fitowa ya girgiza min kai.
“Karki fito basa fada”
“Ni kunya na ke ji”
“Nan Abuja ce ba ruwa kowa da kowa”
Tura ni ya fara yi yana tafiya yana dauko duk abunda yake so yana sakawa a gwandon.
“Fada min abunda kike son na siya miki”
“Bana son komai”
“Kina son abun goge baki? Ko kadar mata ko turare?”
Na yi shiru ban ce komai ba sai yai murmushi ya fiddo wayarsa ya dauki ni hoto.
“Bari na taimaka miki na saka ki a status dina ko wani zai gani ya zo kawata”
“Kawarka? Mace?”
“Eh mana”
Saurin sauka nai daga cikin kwandon duk na san wasu sun gama gani na domin ya zaga wani bangare na shopping din da ni a ciki har wasu na kallona. Da kanshi ya koma yana tura kwadon duk wani abun kwadayi daya gani sai ya dauko guda biyu ya fasa ya ci ya bani rabi sai kuma ya saka rabi a cikin shopping basket din. A haka ya daukar min kadar mata da turare da man goge baki sannan muka zo gurin biya ya ciro kudi mai yawa ya bada sai suka saka masa kayan a leda wani daga cikin yaransu suka zo suka dauka suka kai masa a mota. A tare muka fito daga shopping din yana cin chocolate.
“Na jidadin zuwa shopping din nan kin ga na hadu da ke, jiya na aika kiranki waya hana ki fito?”
Nan ma shiru nai masa ban ce masa komai ba, sai ya bude min gidan gaba yana fadin.
“Shiga muje yau dai sai kin ba ni labarin abunda ya kawo ki garin Abuja”
Sai da na fara taka wani abu dake gefen murfin motar sannan na shiga cikin katuwar motar mai tuli sosai, sai shi ma ya zagoyo ta mazaunin direba ya zauna ya rufe motar yana kunna ac motar tare da kai hannu ya rage karar sautin da ke tashi sannan yaja motar muka hau babban titi yana ta kallona kamar ba driving yake ba.
ZAKI
By Khadeeja Candy
23...
Kamal na tsaye yana lasar wayarsa yana jiran fitowar Ataa sai ga Aliyu ya fito yana wani shan kanshi, bayansa Kamal ya rika kallon a zatonsa ko tana bayansa ne amman sai yaja gate din rufe bata fito ba.
“Kai kake kiran Ataa ne?”
“Eh nine Aliyu ya aiki, ashe ka dawo”
Kamal ya fada yana mika masa hannu.
“Yes, wani abun ta maka ne?”
Da mamaki Kamal ya sake kallon Aliyu sai kuma yai murmushi.
“Mi zata min bata min komai ba”
“Miyasa kake kiranta?”
“Mun saba gaisawa da ita ne kwana biyu, yau kuma ban ganta ba, shiyasa na aika a kira min ita, da wata matsalar ne?”
Aliyu ya tsaya kallonsa kamar ba zai yi magana ba can kuma ya ce.
“Babu, idan gaisuwa ne, ba sai ka kara aikawa nemanta ba aiki take, aikin da aka kawota dan shi”
Aliyu na fada masa haka be tsaya jiran abunda zai kara cewa ba ya juyo ya dawo cikin gidan, cikin wani irin jin haushi da be san dalilinsa, a dayan bangaren kuma yana jin idan har ya kyale rayuwar Ataa zata iya shiga wani hali domin kyanta zai rudi samarin su fara jan ra'ayinta ga wata hanyar da dabam wacce bata dace ba. Cikin falon ya dawo ya zauna sa dai be samu Ataa a falon ba sai Mama Fulani da Maryam da Rukaiya suna wata magana ganinsa sukai shiru.
“Lafiya yake nemanta?”
“Lafiya kalau, wai zuwa yai su gaisa”
“Su gaisa?”
Mama Fulani ta tambaya da mugun mamaki.
“Shi Kamal din? Kuma ya tsaya a waje?”
“Ai ba zai shigo ba dan kar mu dauka gurin Maryam ya zo tunda gurinta ya saba zuwa shiyasa ya aiko a kira masa wannan kazamar”
Rukaiya ta fada tana yatsina fuska, Mama Fulani ta ce.
“Ni fa tun ranar na ke ta mamakin ganinsa har cikin falon nan, domin abu ne mai wahala ya shigo cikin gidan nan idan ba Aliyu ya zo nema ba, sai kuma Maryam wani lokacin idan yana son su gaisa”
Aliyu ya kalleta kamar ya ce wani abu sai kuma yai shiru ya maida hankalinsa gurin tv. Rukaiya da Maryam kuma suna ta kallon juna alamar gulma na cikin cikinsu tana cin su. Wayarsa yai jit alamar kira sai ya cirota daga aljihunsa ya duba number Rahma ce, hakan yasa shi picking ba tare da bata lokaci ba.
“Dear karfe tara za mu je mu ga Doc Perry, idan baka gida ka same ni a asibitinsa idan kuma ka dawo da wuri sai ka same ni a can”
“Kun yi magana da shi ne?”
“Eh mun yi karka bata lokaci ka ji?”
“Na ji make sure kin ci abincin dare kamin ki tafi”
“Okay i love you”
Be amsa ta ba ganin cewar yana a gaban Mama Fulani sai kawai ya kashe wayar ya tura mata ta sako. Ko be fada ba Mama Fulani ta san da Rahma yai waya, sai dai abunda bata gane ba ta ci abincin kafin ta tafi.
“Ina zata ta fi?”
“Zamu je mu ga Doc Perry ne”
“Ciwon ya tashi ne?”
“Aa akan matsalar haihuwa ne”
“Hmmm haka za ku yi ta bata lokaci da kudin a banza ba ku samu mafita ba, na sha fada maka idan ba aure ka kara ba ba zaka taba haihuwa ba”
Ya fada sannan ya juyo ya kalleni.
“Wuce daga nan”
Da saurina na fice daga falon har ina tuntube kamar zan fadi, abun ka da mai shegen tsoro haka nai ta kwara ido a garejin ina ta jiran wani daga cikin yayanta ko kuma ita kanta ta zo ta dake ni amman shiru babu wanda ya zo har dare yai, ban fita karbar abinci a part din Mama Fulani ba, sai na je part din Ammy a can na ci abincin dare na sannan na dawo garejin na kwanta abuna na kwana har safe. Kamar yadda na saba da wuri na farka ina gama sallah na shiga na gyara falon Mama Fulani sannan na je part din Ammy na gyara kamar yadda na saba, bayan na gama Mama Fulani ta ce na dauko gurina aka zuba min abincina, har zan fito sai ya Muhseen ya kirani ya kara min da na shi na fito ina ta murna, a garden na zauna na cinye abuna sannan na dauki plate din naje na wanke na kawo gareji na aje. After like one hour Rukaiyah ta shigo garejin tana rike da makullin mota.
“Ke ta so muje ki riko min kaya”
Da sauri na taso na biyo bayanta a zato daga mota zan riko mata su ko kuma a cikin gida zan dauko na saka mata a mota sai na ji ta ce.
“Ki shiga gidan baya”
Juyawa nai da zimmar komawa gareji na dauko Hijab dina sai ta daka min tsawa.
“Ke ina za ki je?”
“Hijab dina zan dauko”
“Ba Hijab ba ubanki shiga mota muje”
Da sauri na nufi motar na bude na shiga daga ni sai lace dina na jiya da sai dankwali, sai da na rufe motar sannan ta shiga mazaunin direba ta tashi motar muka fice, ni dai ina zaune a baya ina ta kalle-kalle har muka isa wani katafaren shago irin wanda na ke gani a tv nan, wanda komai da komai ana saida a ciki kuma komai bangaren dabam, ni kallo ya hanani rufe motar har sai da naji an dangware ni da karfi.
“Bakauyar banza rufe min mota”
Sai na saka hannu biyu na rufe. Na bi bayanta muna ta taka dan karamin matakalin har muka isa gaban babbar kofar wacce wasu masu uniform suke budewa mutum idan zai shiga, wani dan kwando taja ta mika min shi.
“Ja wannan mu tafi duk abunda na nuna miki ki dauka”
Na saka hannu na karba ina turawa, wai ita ala dole sai ta nuna ni din yar aikin gidansu ce ta sha wani bakin gilashi a fuska tana sanye da yadi babu mayafi a jikinta, ni kuwa duk sai naji na takura da rashin mayafin duk kuwa da na lura kusan rabin matan da suke shigowa shopping din basa da mayafi kuma kowa be kula ba, duk inda muka bi kallona ake nasan wannan baya rasa nasaba da gashin kaina da nai masa tsoro daya na ya sauko har gurin mazaunaina, da kuma haskena ga kyau kamar wata balaraba. Turin kwandon be dame ni ba dan ji nake kamar ina tuka mota duk inda na ga dama juyashi na ke ina jindadi. Dauko wannan dauko wancan haka take bani umarni ina bi kamar bawa da uban gidansa, muna isa sashen kayan dadi ta umarce ni na dauko madara ina kai hannuna sai na ji an rike hannun, da sauri na kalli gafena.
“Na kama ki”
Kamal ne sanye da kananan kaya fuskarsa da murmushi kamar kullum ni ma Murmushin nai sai kuma nai saurin kallon Rukaiya wacce ita ma murmushin take sakar masa.
“Rukaiya shopping kuka zo”
“Eh Wallahi har ma mun kare daman ba da yawa zan yi ba ya aikin?”
“Lafiya kalau, sai ki ba ni aron Mamanar tawa ta raka ni shopping tun da kun kare, kadan na gama sai mu koma gida tare”
Sakin baki tai kamar zata ce masa ba mu kare ba, sai kuma ta ga kamar be dace tai karya ba, dan haka tai murmushin yake.
“Ba matsala”
24
“Thank you, idan kin je gida ki fadawa Mama Fulani ni na areta kuma zan kawo ta nan ba da jimawa ba”
“Okay ayi shopping lafiya”
Taja kwandon daga hannuna tai gaba a abunta kamar tana jin haushi. Sai da ta wuce sannan ya dawo da dubansa gurina ya ce.
“Shiga ciki na turaki”
Ba shiri na bude baki.
“Aa mutane suna kallon mu, kuma mutane ba sa shiga cikin kwadon zuba kaya ai, za su mana fada”
“Ko?”
Ya fada yana murmushin kan na sake cewa wani abu ya dauke ni ya zuba a cikin kwandon yana dariya, ina kokarin fitowa ya girgiza min kai.
“Karki fito basa fada”
“Ni kunya na ke ji”
“Nan Abuja ce ba ruwa kowa da kowa”
Tura ni ya fara yi yana tafiya yana dauko duk abunda yake so yana sakawa a gwandon.
“Fada min abunda kike son na siya miki”
“Bana son komai”
“Kina son abun goge baki? Ko kadar mata ko turare?”
Na yi shiru ban ce komai ba sai yai murmushi ya fiddo wayarsa ya dauki ni hoto.
“Bari na taimaka miki na saka ki a status dina ko wani zai gani ya zo kawata”
“Kawarka? Mace?”
“Eh mana”
Saurin sauka nai daga cikin kwandon duk na san wasu sun gama gani na domin ya zaga wani bangare na shopping din da ni a ciki har wasu na kallona. Da kanshi ya koma yana tura kwadon duk wani abun kwadayi daya gani sai ya dauko guda biyu ya fasa ya ci ya bani rabi sai kuma ya saka rabi a cikin shopping basket din. A haka ya daukar min kadar mata da turare da man goge baki sannan muka zo gurin biya ya ciro kudi mai yawa ya bada sai suka saka masa kayan a leda wani daga cikin yaransu suka zo suka dauka suka kai masa a mota. A tare muka fito daga shopping din yana cin chocolate.
“Na jidadin zuwa shopping din nan kin ga na hadu da ke, jiya na aika kiranki waya hana ki fito?”
Nan ma shiru nai masa ban ce masa komai ba, sai ya bude min gidan gaba yana fadin.
“Shiga muje yau dai sai kin ba ni labarin abunda ya kawo ki garin Abuja”
Sai da na fara taka wani abu dake gefen murfin motar sannan na shiga cikin katuwar motar mai tuli sosai, sai shi ma ya zagoyo ta mazaunin direba ya zauna ya rufe motar yana kunna ac motar tare da kai hannu ya rage karar sautin da ke tashi sannan yaja motar muka hau babban titi yana ta kallona kamar ba driving yake ba.
ZAKI
By Khadeeja Candy
23...
Kamal na tsaye yana lasar wayarsa yana jiran fitowar Ataa sai ga Aliyu ya fito yana wani shan kanshi, bayansa Kamal ya rika kallon a zatonsa ko tana bayansa ne amman sai yaja gate din rufe bata fito ba.
“Kai kake kiran Ataa ne?”
“Eh nine Aliyu ya aiki, ashe ka dawo”
Kamal ya fada yana mika masa hannu.
“Yes, wani abun ta maka ne?”
Da mamaki Kamal ya sake kallon Aliyu sai kuma yai murmushi.
“Mi zata min bata min komai ba”
“Miyasa kake kiranta?”
“Mun saba gaisawa da ita ne kwana biyu, yau kuma ban ganta ba, shiyasa na aika a kira min ita, da wata matsalar ne?”
Aliyu ya tsaya kallonsa kamar ba zai yi magana ba can kuma ya ce.
“Babu, idan gaisuwa ne, ba sai ka kara aikawa nemanta ba aiki take, aikin da aka kawota dan shi”
Aliyu na fada masa haka be tsaya jiran abunda zai kara cewa ba ya juyo ya dawo cikin gidan, cikin wani irin jin haushi da be san dalilinsa, a dayan bangaren kuma yana jin idan har ya kyale rayuwar Ataa zata iya shiga wani hali domin kyanta zai rudi samarin su fara jan ra'ayinta ga wata hanyar da dabam wacce bata dace ba. Cikin falon ya dawo ya zauna sa dai be samu Ataa a falon ba sai Mama Fulani da Maryam da Rukaiya suna wata magana ganinsa sukai shiru.
“Lafiya yake nemanta?”
“Lafiya kalau, wai zuwa yai su gaisa”
“Su gaisa?”
Mama Fulani ta tambaya da mugun mamaki.
“Shi Kamal din? Kuma ya tsaya a waje?”
“Ai ba zai shigo ba dan kar mu dauka gurin Maryam ya zo tunda gurinta ya saba zuwa shiyasa ya aiko a kira masa wannan kazamar”
Rukaiya ta fada tana yatsina fuska, Mama Fulani ta ce.
“Ni fa tun ranar na ke ta mamakin ganinsa har cikin falon nan, domin abu ne mai wahala ya shigo cikin gidan nan idan ba Aliyu ya zo nema ba, sai kuma Maryam wani lokacin idan yana son su gaisa”
Aliyu ya kalleta kamar ya ce wani abu sai kuma yai shiru ya maida hankalinsa gurin tv. Rukaiya da Maryam kuma suna ta kallon juna alamar gulma na cikin cikinsu tana cin su. Wayarsa yai jit alamar kira sai ya cirota daga aljihunsa ya duba number Rahma ce, hakan yasa shi picking ba tare da bata lokaci ba.
“Dear karfe tara za mu je mu ga Doc Perry, idan baka gida ka same ni a asibitinsa idan kuma ka dawo da wuri sai ka same ni a can”
“Kun yi magana da shi ne?”
“Eh mun yi karka bata lokaci ka ji?”
“Na ji make sure kin ci abincin dare kamin ki tafi”
“Okay i love you”
Be amsa ta ba ganin cewar yana a gaban Mama Fulani sai kawai ya kashe wayar ya tura mata ta sako. Ko be fada ba Mama Fulani ta san da Rahma yai waya, sai dai abunda bata gane ba ta ci abincin kafin ta tafi.
“Ina zata ta fi?”
“Zamu je mu ga Doc Perry ne”
“Ciwon ya tashi ne?”
“Aa akan matsalar haihuwa ne”
“Hmmm haka za ku yi ta bata lokaci da kudin a banza ba ku samu mafita ba, na sha fada maka idan ba aure ka kara ba ba zaka taba haihuwa ba”