Sashe 114
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*AG cera ya zo domin ya temaki garkuwan jiki da kuma lafiyar jiki. Sinadari ne wanda ze magance matsaloli da dama wadanda suke hana garkuwan jiki aiki yadda ya kamata ko kuma yake rusa garkuwan jikin ita kanta.*
*Cututtukan zamani daban daban sun sa mutane gaba kuma magance su yana da wahala; irin ciwon Sugar, hawan jini, ciwon sanyin kashi, ciwon gabobi da sauran su. Haka ma cutukka irin wadanda suka shafi fatar jikin wadanda sun hada da kyasfi, pimples, takurewar fata, rakainuwar fata da kuma haske da kyallin fata duka ana shan AG cera kuma yana temakawa wajen magance illolin nan. Mutane masu fama da rashin karfin jiki wajen kwanciya da iyali da kuma mata masu fama da yawan ciwon mara lokacin al'ada ta karshen wata suma baa bar su a baya ba. A takaice dai AG Cera yana temakawa wajen magance cuttukka daban daban wadan ke damun mutum. Domin karin bayani ku tuntuni mu a wannan number +60167474649 ko kuma ku ziyarci shafin mu http://agnutritioninternational.com.*
Sai da nai aman na gama sannan ya zuba min ruwa na wanke baki ya fito daga bandakin. Inda na aje Hijab din dazun ya nufa ya dauko ya zo kusa da ni yana kokarin saka min.
“Saka muje asibiti”
Na bata fuska domin har ga Allah bana jin komai a yanzu, bana jin wani ciwon kai ko wani jiri da zafi jikin kamar na dazun.
““Wallahi bana jin komai Aliyu, aman ne kawai kuma shi ma saboda miyar ne”
“Wani abu kika gani a ciki?”
“Aa bana son miyar ganye dai?”
Fuskar mamaki yai ni kaina ina mamakin kin shan miyar ganye da na ke bayan tana cikin miyar da na ke so, gudun kar Aliyu ya zargi ko bana son cin abincin gidansu ne yasa na ce.
“Ba komai yanzu ai na daina jinsa, daman warin manja ne kuma ya daina”
Na nufi gurin kular abinci na zauna ya saka hannu ina ci ahankali iyakar dauriya nayi domin har ga Allah yau dai bana son warin manjan nan a kusa da ni wata kila saboda zuwan da mu kai a Las Vegas ne dan sabon da nai a can na wata daya yasa na fara mantawa da abincin naija.
“Aliyu ina son tea”
“Okay”
Ya tashi ya fice rike da wayarsa, yana fita nai saurin nufar bandaki na amayarda da dan abunda na ci na tuwon na wanke bakina na dawo, jinginawa nai da gadon, ina ta tunanin Nana da yadda za tai idan tai arba da mahaifinta.
Ba a wani dade ba sai ga Aliyu ya shigi dauke da mug ya zauna kusa da ni ya kai min tea a baki, kadan na kurba shi ma na ji bana sonsa kuma bana son na nuna masa kar yace dole sai munje asibiti, a dole na daure na hanye rabin myg din sannan na kawar da kai sai ya aje kofin ya janyo ni jikinsa ya kwatar ya ciro wayarsa yana lasawa.
“A kira miki Nana ko?”
Na gyada kai. Be ce min komai ba sai da ya kira Momy suka gaisa ya bani muka gaisa sannan ya sake karba ya ce ta bawa wani a kaiwa Nana wayar ina son magana da ita, yana rike da wayar har aka kai mata ina jin lokacin da suke gaisawa Aliyu har wani kasa yake da kai kamar ba shi, lokacin daya miko min wayar sai ya tashi ya fita daga dakin ya bar ni kadai.
“Nana kina nan lafiya?”
“Lafiya kalau kun dawo lafiya?”
Ina jin yanayin muryarta na san ba kafiya ba, muryarta ya nuna tana cikin damuwa da kuma alamar kamar ta yi kuka ma.
“Lafiya Kalau, Nana mun dawo muna Abuja”
Ta yi shiru bata ce komai ba.
“Nana na hadu da Mai Martaba Sarki Agadaz”
Nan ma bata ce min komai ba.
“Nana”
“Naam”
Ta amsa min cikin kuka.
“Nana kike yi?”
“Idan ban yi kuka ba Ataa mi zan yi? Yanzu haka Yayan yayuna suna nan tare da ni gobe tun da safe sun ce za mu wuce Abuja shi ya bukaci a azo da ni”
“Nana har sun iso? Na dauka ma ba ki ji ba”
“Da yamma suka zo, amman har yanzu ina ta ganin kamar ba gaske ba, wata kila sai idan na yi arba da shi zan yarda, wata kila ya yafe min wata kila kuma wani abun ne dabam zai fada min, hakika ina kaunar haduwa da mahaifina ina kaunar saka shi a ido ne ko da kuwa idan na je tsine min zai yi, amman Ataa har yanzu ina jin kunya da nauyin abunda na aikata”
“Wannan na wuce Nana, ba a iya gyara abunda ya riga ya bace sai dai a tari gaba, ni kaina ina fatar kuma ina tunanin yafiyarce domin ya kirani da jikarsa, jininsa diyar diyarsa, Nana na jidadin ganinsa ko da kuwa wulakanta ni yai ya tozarta ni zan yi farincikin ganin Kakana bayan ke da Lukman da Baba yau ba kara ganin wani wanda yake jinina”
“Allahu Akbar”
Shine abunda ta fada sai ta fashe da kuka ni ma kukan na ke, mun dauki tsawon lokaci a haka sannan na sauke wayar jin kamar kukan zai yi ma Nana yawa na aje wayar kasa ba tare da na kashe ba. Bayan sauke sallah isha'i Aliyu ya dawo dakin ganin yadda fuskata da ido na sukai ya san kukan nai daman haka na ke idan nai kuka abun baya boyuwa ga farin daya mutum.
“Idan har Mahafin Nana ne suka hadu da shi kamar yadda kika fada be kamata ace kina ta damun kanki da kuka kamar haka ba, a tunani farinciki ya kamata ki yi”
“Wani farin cikin Aliyu ya yi har sai an koka, taya kake tunanin mace da aka haife ta tun davta tashi bata san kowa na ta ba, rana tsaka ta hadu da kakanta kai tsammanin murna kawai za tai? Mutumen da ganinsa a tare da Nana shine yankewar zubar hawayenta kuma farincikinta, idan har zai yafe mata ya karbe a yadda take yarsa Aliyu ni ma zan koma ya kamar kowa, mai gata ba kuma gata na naira ba gata na yan'uwan uwa da na uba a tare da ni”
Zaunawa yai kusa da ni daman tun da muke maganar a tsaye yake ni kuma ina zaune saman carpet din da nai sallah.
“Kin ce ba ku da kowa a nan, kin ce ba ki san kowa na ki ba tun da aka haife ki, taya kika gane cewar kina da alaka da wannan mutumen? Babyna mi ya raba ku da danginku? Na dade ina son nai miki wannan maganar amman tunanin sakaki a damuwa ko Mama (NaNa) yasa ban cika damunki ba, kuma ina da burin ko da tsawalla miki da sanin hakan sai na aureki saboda kar na ji wani abu da zai iya zama sanadin da wani a familynki ko nawa zai iya hanani aurenki, na aure ki ba tare da sanin kowa na ki ba sai dan nuna miki tsantsar kauna ni da Momy, Wallahi Ayusher ko da daga sama kika fado zan aureki ba tare da damuwa ba, saboda ke na ke kauna ba wani abun daya shafi dangantarki ba ko kuma asalinki”
Kallonsa na ke hawaye taf a idona wata irin kalar kaunarsa da begensa ne ke shiga cikin raina. Hakika Aliyu yayi min abunda ba kowa ne ke yi ba, auren mace da baka san asalinta ba, ko da dan kyauna Aliyu ya aureni yayi min hallacin tun da be taba bayyana hakan ba ya bari a cikin ransa kuma be taba nuna min ba.
“Ko da ka tambaye ni asalina a wacan lokacin ko kuma anan gaba idan har wannan abun be bayyana ba, ba zan iya fada maka ba, saboda bana son bayyana abunda Nana ta fada min a matsayin sirrin wanda na san jinsa a gurin wani zai iya haifa mata da matsala ko kuma damuwa”
Hannunsa ya kai ya riko nawa.
“Kina da karancin shekaru amman kina da wayo da hikima akan dukan abunda ya shafi mahaifiyarki, hakan na da kyau kaunarki na ta karuwa a raina ta ko'ina”
Dan murmushi nai ina hawayen da suka ji su tsaya min. Sai ya jani jikinsa ya rumgume ni kuma na lafe abuna kamar ba a bangaren Ammy muke ba, domin na fara sabawa da yanayinsa a yanzu.
“Ba ni labari ya kai Mama ta rabu da danginta”
Kamar mai karanta labari haka na jera masa yadda komai ya faru kamar yadda Nana ta fada min. Ya tausaya mata matuka kuma ya nuna min jindadinsa da gwarin guiwar cewar Mai Martaba sarkin Agadaz zai yafe mata ta koma cikin danginta ni kaina na tabbatar da hakan domin na lura da yadda ya nuna damuwarsa da ita.
“Za mu je mu yi ma Mama Fulani sallama sannan mu wuce gida”
Kasa nai da kaina alamar bana son zuwan can. Sai ya mikar da ni tsaye.
“Babyna no matter what Mama Fulani zata miki dole ne ke yi respecting dinta matukar kina respecting din Momy da kuma ni”
Ban ce masa komai ba, domin ba zan iya fadar wata mummunar kalma akan babban mutum kamar mama fulani ba, ba kuma zan iya aibanta dan'uwan Aliyu a gabansa ba, saboda mijina ne kuma ya nuna min kauna be kama na ci zarafin wani dan'uwansa a gabansa ba ko kuma na fadi wata maganar wacce zata sosa masa rai, duk kuwa da kasancewar ban san alakar da ke tsakaninsa da Mama Fulani ba, ba zan taba son Mama Fulani ba har abada saboda irin kiyayyar da ta nuna min da kyama ita da yayanta sai dai hakan ba shi yake nufin na nuna a gaban Aliyu ba, taya zan kauna ci macw da ya kirani da mahaukaciya, mayya, yar talakawa, yar matsiyata, tai min korar kare a gidan nan, ta hanani taba abun gidanta abinci ma sai da na tara dankwalina ta zuba min, daga baya ta ware min komai nawa dabam kamar wata karya, matar da ta mareni na suma saboda kawai ina rokon ta bar ni na yi mata aiki ta biyani na nemawa mahaifiyata magani? Har abada kuma har duniya ta hade ba zan taba manta wannan ba.
*Cututtukan zamani daban daban sun sa mutane gaba kuma magance su yana da wahala; irin ciwon Sugar, hawan jini, ciwon sanyin kashi, ciwon gabobi da sauran su. Haka ma cutukka irin wadanda suka shafi fatar jikin wadanda sun hada da kyasfi, pimples, takurewar fata, rakainuwar fata da kuma haske da kyallin fata duka ana shan AG cera kuma yana temakawa wajen magance illolin nan. Mutane masu fama da rashin karfin jiki wajen kwanciya da iyali da kuma mata masu fama da yawan ciwon mara lokacin al'ada ta karshen wata suma baa bar su a baya ba. A takaice dai AG Cera yana temakawa wajen magance cuttukka daban daban wadan ke damun mutum. Domin karin bayani ku tuntuni mu a wannan number +60167474649 ko kuma ku ziyarci shafin mu http://agnutritioninternational.com.*
Sai da nai aman na gama sannan ya zuba min ruwa na wanke baki ya fito daga bandakin. Inda na aje Hijab din dazun ya nufa ya dauko ya zo kusa da ni yana kokarin saka min.
“Saka muje asibiti”
Na bata fuska domin har ga Allah bana jin komai a yanzu, bana jin wani ciwon kai ko wani jiri da zafi jikin kamar na dazun.
““Wallahi bana jin komai Aliyu, aman ne kawai kuma shi ma saboda miyar ne”
“Wani abu kika gani a ciki?”
“Aa bana son miyar ganye dai?”
Fuskar mamaki yai ni kaina ina mamakin kin shan miyar ganye da na ke bayan tana cikin miyar da na ke so, gudun kar Aliyu ya zargi ko bana son cin abincin gidansu ne yasa na ce.
“Ba komai yanzu ai na daina jinsa, daman warin manja ne kuma ya daina”
Na nufi gurin kular abinci na zauna ya saka hannu ina ci ahankali iyakar dauriya nayi domin har ga Allah yau dai bana son warin manjan nan a kusa da ni wata kila saboda zuwan da mu kai a Las Vegas ne dan sabon da nai a can na wata daya yasa na fara mantawa da abincin naija.
“Aliyu ina son tea”
“Okay”
Ya tashi ya fice rike da wayarsa, yana fita nai saurin nufar bandaki na amayarda da dan abunda na ci na tuwon na wanke bakina na dawo, jinginawa nai da gadon, ina ta tunanin Nana da yadda za tai idan tai arba da mahaifinta.
Ba a wani dade ba sai ga Aliyu ya shigi dauke da mug ya zauna kusa da ni ya kai min tea a baki, kadan na kurba shi ma na ji bana sonsa kuma bana son na nuna masa kar yace dole sai munje asibiti, a dole na daure na hanye rabin myg din sannan na kawar da kai sai ya aje kofin ya janyo ni jikinsa ya kwatar ya ciro wayarsa yana lasawa.
“A kira miki Nana ko?”
Na gyada kai. Be ce min komai ba sai da ya kira Momy suka gaisa ya bani muka gaisa sannan ya sake karba ya ce ta bawa wani a kaiwa Nana wayar ina son magana da ita, yana rike da wayar har aka kai mata ina jin lokacin da suke gaisawa Aliyu har wani kasa yake da kai kamar ba shi, lokacin daya miko min wayar sai ya tashi ya fita daga dakin ya bar ni kadai.
“Nana kina nan lafiya?”
“Lafiya kalau kun dawo lafiya?”
Ina jin yanayin muryarta na san ba kafiya ba, muryarta ya nuna tana cikin damuwa da kuma alamar kamar ta yi kuka ma.
“Lafiya Kalau, Nana mun dawo muna Abuja”
Ta yi shiru bata ce komai ba.
“Nana na hadu da Mai Martaba Sarki Agadaz”
Nan ma bata ce min komai ba.
“Nana”
“Naam”
Ta amsa min cikin kuka.
“Nana kike yi?”
“Idan ban yi kuka ba Ataa mi zan yi? Yanzu haka Yayan yayuna suna nan tare da ni gobe tun da safe sun ce za mu wuce Abuja shi ya bukaci a azo da ni”
“Nana har sun iso? Na dauka ma ba ki ji ba”
“Da yamma suka zo, amman har yanzu ina ta ganin kamar ba gaske ba, wata kila sai idan na yi arba da shi zan yarda, wata kila ya yafe min wata kila kuma wani abun ne dabam zai fada min, hakika ina kaunar haduwa da mahaifina ina kaunar saka shi a ido ne ko da kuwa idan na je tsine min zai yi, amman Ataa har yanzu ina jin kunya da nauyin abunda na aikata”
“Wannan na wuce Nana, ba a iya gyara abunda ya riga ya bace sai dai a tari gaba, ni kaina ina fatar kuma ina tunanin yafiyarce domin ya kirani da jikarsa, jininsa diyar diyarsa, Nana na jidadin ganinsa ko da kuwa wulakanta ni yai ya tozarta ni zan yi farincikin ganin Kakana bayan ke da Lukman da Baba yau ba kara ganin wani wanda yake jinina”
“Allahu Akbar”
Shine abunda ta fada sai ta fashe da kuka ni ma kukan na ke, mun dauki tsawon lokaci a haka sannan na sauke wayar jin kamar kukan zai yi ma Nana yawa na aje wayar kasa ba tare da na kashe ba. Bayan sauke sallah isha'i Aliyu ya dawo dakin ganin yadda fuskata da ido na sukai ya san kukan nai daman haka na ke idan nai kuka abun baya boyuwa ga farin daya mutum.
“Idan har Mahafin Nana ne suka hadu da shi kamar yadda kika fada be kamata ace kina ta damun kanki da kuka kamar haka ba, a tunani farinciki ya kamata ki yi”
“Wani farin cikin Aliyu ya yi har sai an koka, taya kake tunanin mace da aka haife ta tun davta tashi bata san kowa na ta ba, rana tsaka ta hadu da kakanta kai tsammanin murna kawai za tai? Mutumen da ganinsa a tare da Nana shine yankewar zubar hawayenta kuma farincikinta, idan har zai yafe mata ya karbe a yadda take yarsa Aliyu ni ma zan koma ya kamar kowa, mai gata ba kuma gata na naira ba gata na yan'uwan uwa da na uba a tare da ni”
Zaunawa yai kusa da ni daman tun da muke maganar a tsaye yake ni kuma ina zaune saman carpet din da nai sallah.
“Kin ce ba ku da kowa a nan, kin ce ba ki san kowa na ki ba tun da aka haife ki, taya kika gane cewar kina da alaka da wannan mutumen? Babyna mi ya raba ku da danginku? Na dade ina son nai miki wannan maganar amman tunanin sakaki a damuwa ko Mama (NaNa) yasa ban cika damunki ba, kuma ina da burin ko da tsawalla miki da sanin hakan sai na aureki saboda kar na ji wani abu da zai iya zama sanadin da wani a familynki ko nawa zai iya hanani aurenki, na aure ki ba tare da sanin kowa na ki ba sai dan nuna miki tsantsar kauna ni da Momy, Wallahi Ayusher ko da daga sama kika fado zan aureki ba tare da damuwa ba, saboda ke na ke kauna ba wani abun daya shafi dangantarki ba ko kuma asalinki”
Kallonsa na ke hawaye taf a idona wata irin kalar kaunarsa da begensa ne ke shiga cikin raina. Hakika Aliyu yayi min abunda ba kowa ne ke yi ba, auren mace da baka san asalinta ba, ko da dan kyauna Aliyu ya aureni yayi min hallacin tun da be taba bayyana hakan ba ya bari a cikin ransa kuma be taba nuna min ba.
“Ko da ka tambaye ni asalina a wacan lokacin ko kuma anan gaba idan har wannan abun be bayyana ba, ba zan iya fada maka ba, saboda bana son bayyana abunda Nana ta fada min a matsayin sirrin wanda na san jinsa a gurin wani zai iya haifa mata da matsala ko kuma damuwa”
Hannunsa ya kai ya riko nawa.
“Kina da karancin shekaru amman kina da wayo da hikima akan dukan abunda ya shafi mahaifiyarki, hakan na da kyau kaunarki na ta karuwa a raina ta ko'ina”
Dan murmushi nai ina hawayen da suka ji su tsaya min. Sai ya jani jikinsa ya rumgume ni kuma na lafe abuna kamar ba a bangaren Ammy muke ba, domin na fara sabawa da yanayinsa a yanzu.
“Ba ni labari ya kai Mama ta rabu da danginta”
Kamar mai karanta labari haka na jera masa yadda komai ya faru kamar yadda Nana ta fada min. Ya tausaya mata matuka kuma ya nuna min jindadinsa da gwarin guiwar cewar Mai Martaba sarkin Agadaz zai yafe mata ta koma cikin danginta ni kaina na tabbatar da hakan domin na lura da yadda ya nuna damuwarsa da ita.
“Za mu je mu yi ma Mama Fulani sallama sannan mu wuce gida”
Kasa nai da kaina alamar bana son zuwan can. Sai ya mikar da ni tsaye.
“Babyna no matter what Mama Fulani zata miki dole ne ke yi respecting dinta matukar kina respecting din Momy da kuma ni”
Ban ce masa komai ba, domin ba zan iya fadar wata mummunar kalma akan babban mutum kamar mama fulani ba, ba kuma zan iya aibanta dan'uwan Aliyu a gabansa ba, saboda mijina ne kuma ya nuna min kauna be kama na ci zarafin wani dan'uwansa a gabansa ba ko kuma na fadi wata maganar wacce zata sosa masa rai, duk kuwa da kasancewar ban san alakar da ke tsakaninsa da Mama Fulani ba, ba zan taba son Mama Fulani ba har abada saboda irin kiyayyar da ta nuna min da kyama ita da yayanta sai dai hakan ba shi yake nufin na nuna a gaban Aliyu ba, taya zan kauna ci macw da ya kirani da mahaukaciya, mayya, yar talakawa, yar matsiyata, tai min korar kare a gidan nan, ta hanani taba abun gidanta abinci ma sai da na tara dankwalina ta zuba min, daga baya ta ware min komai nawa dabam kamar wata karya, matar da ta mareni na suma saboda kawai ina rokon ta bar ni na yi mata aiki ta biyani na nemawa mahaifiyata magani? Har abada kuma har duniya ta hade ba zan taba manta wannan ba.