Sashe 56
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mama Fulani bata kare gama rufe bakinta ba, Rukaiya ta shigo dakin da sallama tana fadin
“Mama Abbah na kiranki”
Mama Fulani ta mike tsaye ta fice tana nanatawa Aliyu zancenta, har Rukaiya ta juya zata fita Aliyu ya kirata ta juyo.
“Kamal ya kawo Ataa?”
“Eh amman be shigo ba ita kadai ta zo kuma Mama ta bata kudin mota ta maida ta gida”
Mikewa yai tsaye da sauri.
“What? Miyasa?”
“Daman ai Mama ta ce ba zata kwana a gidan nan ba”
Rukaiya ta bashi amsa tana kallon yadda hankalinsa ya tashi. Fita yai daga dakin ya nufi dakin Mama Fulani sai ya same ta ciki tana magana da Momy.
“Mama miyasa kika kori Ataa?”
Tsayawa tai kallonsa kamar yadda Momy ma take kallonsa.
“Why Mama why”
Ya tambaya kamar ya fasa kuka.
“Aliyu wai miye alakarka da yarinyar nan ne? Ina ce a nan gidan ka santa kuka aiki kawai ta zo amman kun bi ku fitini kanku da ita”
Cewar Mama Fulani Momy ta kalleta ta ce
“Yanzu Fulani sai da kika sallami yarinyar nan? Ba asibiti Kamal ya kai ta ba?”
“Ya dawo da ita ai na bawa Zaharadeen kudin motar ta na ce ya dora ta a mota, ni ba zan zauna da ita a gidan nan ba”
“Baki kyauta min ba Mama, ba ki san kudiri akan yarinyar nan ba”
Cewar Aliyu cikin rashin jindadi.
“Kudirinka kamar ya?”
Be bata amsa ba ya aika mata da wata tambayar.
“Wace tashar kika ce ya kai?”
“Ko kaje yanzu ba zaka same ta ba, and bari na fada maka indai na isa da kai karka bi bayan yarinyar nan”
Mama Fulani ta fada tana nuna shi da yatsa. Sa ya zauna a saman kujerar dakin ya dafe kansa, ji yai babu dadi gaba daya ranar ba tai masa dadi ba, an kori Ataa Mama Fulani ta hana ya bi bayanta and ga abunda Rahma tai masa.
“Daga zuwan yarinya ku dauki wani buri ku dora akanta yar talakawa? Abun kunya ma aiki take a gidan nan fa haba Aliyu ko kowa zai ce ya so ta ai ba da kai ba”
Dagowa yai ya kalli Mama Fulani.
“Ba son ta na ke ba Mama, taimakon zan yi saboda halin da muka saka ta”
“Wane hali? Halin me kuka saka ta? Ina ma kasanta idan ba nan gidan ba? Ko kuwa dan fadan da nai mata da be taka kara ya karya ba shine wani hali”
“Ba shi nake nufi ba, kodar mahaifiyar yarinyar nan aka cire aka sakawa Rahma ba da amincewar su ba, aikin da take a nan saboda ta samawa mahaifiyarta magani take”
Momy ta zaro ido tana rufe baki.
“Daman yarinyar nan ce? Ta ina ka sani?”
“Ta mana aiki ai Momy ko kin manta?”
Ya fada yana kallonta da damuwa a fuskarta.
“Kasan da ita ce ka kyaleta tana ta shan wahala? Ka kasa taimakonta? Anya kana da imani kuwa? Wace irin zuciya ce a kirjinka? Wane irin rayuwa ce wannan?”
“Momy ta ki aminta da ni ne, a duk lokacin da nai mata maganar mahaifiyarta sai ta fada min wata maganar dabam marar dadi, ta kasa yarda cewar taimakonta zan yi, a yanzu ma ina kokarin ganin ta aminta da ni ne kuma Mama ta koreta”
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u amman wannan yarinyar tana ganin rayuwa”
Mama Fulani ta gyara tsayuwarta cikin yanayin da ke nuna bata jidadin boye mata da Aliyu yai ta ce.
“Baka taba fada min wannan maganar ba, baka taba labarta min komai ba, taimakonta da kake son da ma gaskiyar abunda ya faru duk baka fada min ba”
“Ba abu ne mai dadi da zan rika labartawa kowa ba Mama”
“Haka ne”
Ta fada sannan ya juya ta fice daga dakin. Saukowa tai downstairs ta nufi kitchen cikin wani yanayi marar misaltuwa, ko Muhseen da ke zaune a falon bata kula da shi ba har taje ta hada ma Abbah abinci ta fito ta fice ta kofar gaba zuwa part din Abbah, abincin ta kai masa ta zuba masa da kanta kamar yadda ta saba.
“Lafiya dai Hajiya Fulani?”
Abbah ya tambaya ganin yanayinta.
“Lafiya Kalau”
Bata fada masa komai ba duk kuwa da kasancewar fuskarta ta nuna hakan. Sai ya gama cin abinci ya tashi a uzurce ta rako shi har gurin mota ya shiga sannan ta nufo part dinta. Lokacin da ta shigo sai ta zauna a falo tana ta kallon su Rukaiya da Husnat dake gardama kan wani film, kallonsu kawai take amman hankalinta baya gurinsu, Aliyu ne ya sauko yana rike da wayarsa ya nufo inda Mama Fulani take zaune, sai da ya karaso daf da ita ya dan risina sannan ya ce.
“Mama ina ne unguwar su yarinyar nan, kuma daga ina aka akawo miki ita?”
“Ban san kowa nata ba, balle na san unguwarsu”
“Amman baya kawo miki ita?”
“Wacce ta kawo min ita ma ban san inda take ba”
Tana fadar hakan ta mike tsaye ta nufi upstairs ta barshi a gurin risine Muhseen da sauran yan'uwnas suna kallonsa domin sun ji abunda yake tambayar Mama Fulani sun kuma fahimci wacce yake tambayar, ban da Muhseen da be san abunda yake faruwa ba. Mikewa Aliyu yai tsaye ya fice daga falon, motarsa ya nufa ya shiga ya dauki hanyar gidansa cikin damuwa. A masallacin hanya ya tsaya yai sallah magariba da isha'i sannan ya shiga gida. A falo ya fara zaunawa ya dafe kansa yana ta yawo da idonsa, har ga Allah be jidadin korar da Mama Fulani tai ma Ataa ba, all his plan yanzu na taimakonta ne and yanzu be san ma inda zai sake samunta ba, tana kadunar kamar yadda wacan ta fada masa ko kuwa tana cikin sokoto? The way da yake ganin yanayin Mama Fulani ba lallai ta fada masa inda zai ga Ataa ba.
“Ban zata maganar zata haifar da wata matsala ba”
Cewar Rahma tana sauko daga stairs. Kamim ta karaso Aliyu ya mike tsaye ya wuce zuwa upstairs yana fadin.
“Ba shi ya dame ni ba yanzu”
Juyowa tai tana kallonsa.
“To me ya dame ka? Wata matsalar ce?”
Be ce mata komai ba ya shige dakinsa bakin gadonsa ya zauna yana kallon dakin kamar wani bakonsa. Rahma ce ta shigo tana tafiya a hankali ta zauna kusa da shi.
“Aliyu akwai wata matsalar ne?”
“Yarinyar da tai mana aiki wacce aka kirewa mahaifiyarta koda aka saka miki, ta zo nan Abuja tana aiki gidan Mama Fulani and yau Mama Fulani ta koreta”
Da Mamaki Rahma ta kalleshi tasan ba mutum ne mai yawan magana ba lallai ya fada mata cewar yarinyar tana aiki a gidan Mama Fulani ba, amman bata ga abun damuwa a cikin lamarin ba, akan mi zai damu da an koreta? A take zuciyarta ta soma raya mata son ta Aliyu yake.
“Miye abun damuwa dan Mama fulani ta koreta? Wata kila ta mata ba daidai ba ne shiyasa ta koreta”
“Ba lallai sai ta mata wani abu ba, and ba ni da wani plan a yanzu daya wuce taimakon yarinyar saboda halin da muka saka ta”
“Ba mu saka ta cikin ko wane hali ba Aliyu, ba laifin mu ba ne, da muka ce a nemo siya mukai kuma ka biya kudi ba a hanya ka kareta ka cire mata kodar ba, ban ga dalilin damuwa ba sai idan son ta kake!”
Ta fada da kamar fada idonta na cika da kwalla. Aliyu ya kalleta da kyau
“So ne abunda ranki ya kawo miki? Ba ki yi tunanin ya kamata mu taimake ta ba? Ba ki duba irin zalincin da akai mata da irin rayuwar da ta shiga?”
“Ba mu muka saka ta a cikin wata rayuwa ba Aliyu, idan ma zalinci ne b mu muka zalince ba”
“Amman sanadin wa? Tun farkon da aka samu kodar nan ya kamata na bincika daga gurin wa ta fito ban yi ba, gashi abunda ya faru, yanzu kuma na gane gaskiya sai na ce zan hau gado na kwanta nai rayuwata na kyaleta? Abunda ya faru da ke Rahma ishara ce, wata kila da ba a zalinci yarinyar nan ba da yanzu kodar da aka saka miki bata kone ba”
Hawaye ne ya sauko mata tana kallonsa.
“Mommy ta yi gaskiya, tun ba mutu ba ka fara gajiya da ni, da ada ne baka iya yin maganar wata mace a gabana Aliyu kuma ba za fada min wata magana da zata bata min rai ba, gaskiya ne maza ba su da tabbas, korar da akai wa wata ita ce damuwarka ba lafiyata ba? Saboda ni ina daf da mutuwa ka auro wata ko?”
Mikewa tai tsaye ta fice daga dakin Aliyu ya bita da ido yana jin kansa kamar zai rabe biyu, gaba daya yau komai na duniyar nan ya hade masa, rumtse ido yai gam kamin ya bude ya mike tsaye ya bi bayan Rahma, yayi zaton zai same ta tana kuka sai ya same tana hada wasu tufafin nata cikin akwati tana hawaye. Kusa da ita ya zauna yana kallon yanayinta ya kai hannu ya rika hannunta ya soma magana a hankali.
“Lafiyarki ta dame ni Rahma, amman hankali ya fi karkarta akan yarinyar ina zan same ta har na taimaka mata wata kila idan na taimaka mata Allah zai dube mu ya ba mu haihuwa kuma ya baki lafiya”
Mikewa tai tsaye ta nufi wardrobe ta rufe sannan ta juyo tana share hawayenta ta kalleta.
“Mommy ta fada min gobe da misalin Goma na safe za mu wuce, ina son na kwanta da wuri saboda na samu bachi”
“Mama Abbah na kiranki”
Mama Fulani ta mike tsaye ta fice tana nanatawa Aliyu zancenta, har Rukaiya ta juya zata fita Aliyu ya kirata ta juyo.
“Kamal ya kawo Ataa?”
“Eh amman be shigo ba ita kadai ta zo kuma Mama ta bata kudin mota ta maida ta gida”
Mikewa yai tsaye da sauri.
“What? Miyasa?”
“Daman ai Mama ta ce ba zata kwana a gidan nan ba”
Rukaiya ta bashi amsa tana kallon yadda hankalinsa ya tashi. Fita yai daga dakin ya nufi dakin Mama Fulani sai ya same ta ciki tana magana da Momy.
“Mama miyasa kika kori Ataa?”
Tsayawa tai kallonsa kamar yadda Momy ma take kallonsa.
“Why Mama why”
Ya tambaya kamar ya fasa kuka.
“Aliyu wai miye alakarka da yarinyar nan ne? Ina ce a nan gidan ka santa kuka aiki kawai ta zo amman kun bi ku fitini kanku da ita”
Cewar Mama Fulani Momy ta kalleta ta ce
“Yanzu Fulani sai da kika sallami yarinyar nan? Ba asibiti Kamal ya kai ta ba?”
“Ya dawo da ita ai na bawa Zaharadeen kudin motar ta na ce ya dora ta a mota, ni ba zan zauna da ita a gidan nan ba”
“Baki kyauta min ba Mama, ba ki san kudiri akan yarinyar nan ba”
Cewar Aliyu cikin rashin jindadi.
“Kudirinka kamar ya?”
Be bata amsa ba ya aika mata da wata tambayar.
“Wace tashar kika ce ya kai?”
“Ko kaje yanzu ba zaka same ta ba, and bari na fada maka indai na isa da kai karka bi bayan yarinyar nan”
Mama Fulani ta fada tana nuna shi da yatsa. Sa ya zauna a saman kujerar dakin ya dafe kansa, ji yai babu dadi gaba daya ranar ba tai masa dadi ba, an kori Ataa Mama Fulani ta hana ya bi bayanta and ga abunda Rahma tai masa.
“Daga zuwan yarinya ku dauki wani buri ku dora akanta yar talakawa? Abun kunya ma aiki take a gidan nan fa haba Aliyu ko kowa zai ce ya so ta ai ba da kai ba”
Dagowa yai ya kalli Mama Fulani.
“Ba son ta na ke ba Mama, taimakon zan yi saboda halin da muka saka ta”
“Wane hali? Halin me kuka saka ta? Ina ma kasanta idan ba nan gidan ba? Ko kuwa dan fadan da nai mata da be taka kara ya karya ba shine wani hali”
“Ba shi nake nufi ba, kodar mahaifiyar yarinyar nan aka cire aka sakawa Rahma ba da amincewar su ba, aikin da take a nan saboda ta samawa mahaifiyarta magani take”
Momy ta zaro ido tana rufe baki.
“Daman yarinyar nan ce? Ta ina ka sani?”
“Ta mana aiki ai Momy ko kin manta?”
Ya fada yana kallonta da damuwa a fuskarta.
“Kasan da ita ce ka kyaleta tana ta shan wahala? Ka kasa taimakonta? Anya kana da imani kuwa? Wace irin zuciya ce a kirjinka? Wane irin rayuwa ce wannan?”
“Momy ta ki aminta da ni ne, a duk lokacin da nai mata maganar mahaifiyarta sai ta fada min wata maganar dabam marar dadi, ta kasa yarda cewar taimakonta zan yi, a yanzu ma ina kokarin ganin ta aminta da ni ne kuma Mama ta koreta”
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u amman wannan yarinyar tana ganin rayuwa”
Mama Fulani ta gyara tsayuwarta cikin yanayin da ke nuna bata jidadin boye mata da Aliyu yai ta ce.
“Baka taba fada min wannan maganar ba, baka taba labarta min komai ba, taimakonta da kake son da ma gaskiyar abunda ya faru duk baka fada min ba”
“Ba abu ne mai dadi da zan rika labartawa kowa ba Mama”
“Haka ne”
Ta fada sannan ya juya ta fice daga dakin. Saukowa tai downstairs ta nufi kitchen cikin wani yanayi marar misaltuwa, ko Muhseen da ke zaune a falon bata kula da shi ba har taje ta hada ma Abbah abinci ta fito ta fice ta kofar gaba zuwa part din Abbah, abincin ta kai masa ta zuba masa da kanta kamar yadda ta saba.
“Lafiya dai Hajiya Fulani?”
Abbah ya tambaya ganin yanayinta.
“Lafiya Kalau”
Bata fada masa komai ba duk kuwa da kasancewar fuskarta ta nuna hakan. Sai ya gama cin abinci ya tashi a uzurce ta rako shi har gurin mota ya shiga sannan ta nufo part dinta. Lokacin da ta shigo sai ta zauna a falo tana ta kallon su Rukaiya da Husnat dake gardama kan wani film, kallonsu kawai take amman hankalinta baya gurinsu, Aliyu ne ya sauko yana rike da wayarsa ya nufo inda Mama Fulani take zaune, sai da ya karaso daf da ita ya dan risina sannan ya ce.
“Mama ina ne unguwar su yarinyar nan, kuma daga ina aka akawo miki ita?”
“Ban san kowa nata ba, balle na san unguwarsu”
“Amman baya kawo miki ita?”
“Wacce ta kawo min ita ma ban san inda take ba”
Tana fadar hakan ta mike tsaye ta nufi upstairs ta barshi a gurin risine Muhseen da sauran yan'uwnas suna kallonsa domin sun ji abunda yake tambayar Mama Fulani sun kuma fahimci wacce yake tambayar, ban da Muhseen da be san abunda yake faruwa ba. Mikewa Aliyu yai tsaye ya fice daga falon, motarsa ya nufa ya shiga ya dauki hanyar gidansa cikin damuwa. A masallacin hanya ya tsaya yai sallah magariba da isha'i sannan ya shiga gida. A falo ya fara zaunawa ya dafe kansa yana ta yawo da idonsa, har ga Allah be jidadin korar da Mama Fulani tai ma Ataa ba, all his plan yanzu na taimakonta ne and yanzu be san ma inda zai sake samunta ba, tana kadunar kamar yadda wacan ta fada masa ko kuwa tana cikin sokoto? The way da yake ganin yanayin Mama Fulani ba lallai ta fada masa inda zai ga Ataa ba.
“Ban zata maganar zata haifar da wata matsala ba”
Cewar Rahma tana sauko daga stairs. Kamim ta karaso Aliyu ya mike tsaye ya wuce zuwa upstairs yana fadin.
“Ba shi ya dame ni ba yanzu”
Juyowa tai tana kallonsa.
“To me ya dame ka? Wata matsalar ce?”
Be ce mata komai ba ya shige dakinsa bakin gadonsa ya zauna yana kallon dakin kamar wani bakonsa. Rahma ce ta shigo tana tafiya a hankali ta zauna kusa da shi.
“Aliyu akwai wata matsalar ne?”
“Yarinyar da tai mana aiki wacce aka kirewa mahaifiyarta koda aka saka miki, ta zo nan Abuja tana aiki gidan Mama Fulani and yau Mama Fulani ta koreta”
Da Mamaki Rahma ta kalleshi tasan ba mutum ne mai yawan magana ba lallai ya fada mata cewar yarinyar tana aiki a gidan Mama Fulani ba, amman bata ga abun damuwa a cikin lamarin ba, akan mi zai damu da an koreta? A take zuciyarta ta soma raya mata son ta Aliyu yake.
“Miye abun damuwa dan Mama fulani ta koreta? Wata kila ta mata ba daidai ba ne shiyasa ta koreta”
“Ba lallai sai ta mata wani abu ba, and ba ni da wani plan a yanzu daya wuce taimakon yarinyar saboda halin da muka saka ta”
“Ba mu saka ta cikin ko wane hali ba Aliyu, ba laifin mu ba ne, da muka ce a nemo siya mukai kuma ka biya kudi ba a hanya ka kareta ka cire mata kodar ba, ban ga dalilin damuwa ba sai idan son ta kake!”
Ta fada da kamar fada idonta na cika da kwalla. Aliyu ya kalleta da kyau
“So ne abunda ranki ya kawo miki? Ba ki yi tunanin ya kamata mu taimake ta ba? Ba ki duba irin zalincin da akai mata da irin rayuwar da ta shiga?”
“Ba mu muka saka ta a cikin wata rayuwa ba Aliyu, idan ma zalinci ne b mu muka zalince ba”
“Amman sanadin wa? Tun farkon da aka samu kodar nan ya kamata na bincika daga gurin wa ta fito ban yi ba, gashi abunda ya faru, yanzu kuma na gane gaskiya sai na ce zan hau gado na kwanta nai rayuwata na kyaleta? Abunda ya faru da ke Rahma ishara ce, wata kila da ba a zalinci yarinyar nan ba da yanzu kodar da aka saka miki bata kone ba”
Hawaye ne ya sauko mata tana kallonsa.
“Mommy ta yi gaskiya, tun ba mutu ba ka fara gajiya da ni, da ada ne baka iya yin maganar wata mace a gabana Aliyu kuma ba za fada min wata magana da zata bata min rai ba, gaskiya ne maza ba su da tabbas, korar da akai wa wata ita ce damuwarka ba lafiyata ba? Saboda ni ina daf da mutuwa ka auro wata ko?”
Mikewa tai tsaye ta fice daga dakin Aliyu ya bita da ido yana jin kansa kamar zai rabe biyu, gaba daya yau komai na duniyar nan ya hade masa, rumtse ido yai gam kamin ya bude ya mike tsaye ya bi bayan Rahma, yayi zaton zai same ta tana kuka sai ya same tana hada wasu tufafin nata cikin akwati tana hawaye. Kusa da ita ya zauna yana kallon yanayinta ya kai hannu ya rika hannunta ya soma magana a hankali.
“Lafiyarki ta dame ni Rahma, amman hankali ya fi karkarta akan yarinyar ina zan same ta har na taimaka mata wata kila idan na taimaka mata Allah zai dube mu ya ba mu haihuwa kuma ya baki lafiya”
Mikewa tai tsaye ta nufi wardrobe ta rufe sannan ta juyo tana share hawayenta ta kalleta.
“Mommy ta fada min gobe da misalin Goma na safe za mu wuce, ina son na kwanta da wuri saboda na samu bachi”