Sashe 33
Zaki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“No no no, haba Rahma yaushe kik fara munanamin zato? Ko zan yi soyayya da wata ai ba wannan kazamar ba, yar talakawa taya ma? Wallahi ba son ta na ke ba, kawai yarinyar tana bala'in ba ni tausayi ne, kuma kin ga sanadin mu an zalince ta be kamata mu kyaleta ba”
“Ba mu muka zalince ba Aliyu miyasa ka kasa ganewa? Shi kansa Doc Asim ba zai zalince ba, ai ya fada maka ya bata kudi ita ce take son masa sheri wata kila ma hadin kai ne da ita dan ta bata mishi suna”
Ya san duk yadda zai yi kokarin fahimtar da ita a yanzu ba zata fahimta ba, domin ranta ya bace sosai and ya san wani abu makamancin wannan be taba shiga tsakaninsu ba, ba lallai ne ta karbi abun a zuciyarta ba, musamman a yadda tai masa fahimta baibai,rumgume ta yai ya saka yatsunsa cikin nata. Ita kanta bata taba jin abu ya daki kirjinta ya ratsa zuciyarta yana neman numfashinta ba irin yau, ashe haka kishi yake, ashe haka ko wacce mace take ji idan mijinta na son wata? Bata taba samun kanta a cikin wannan yanayin ba sai yanzu, fashewa tai da wani irin kuka kamar an mata mutuwa shi kuma ya kara matseta a kirjinsa yana shafa bayanta, one of abunda ya tsana is kuka, kukan kuma ya zama shine silar musamman Rahma da baya son abunda ya taba ta. Sakinsa tai tana saka hannunta ta share hawayenta, sai ya mika dukan karfinsa ya rika ta a tare suka rika taka stairs din har ya shiga da ita dakinta bakin gadon suka zauna ita da shi, ta saka duka hannayenta ta rike masa riga hawayen na bin idonta.
“Wallahi Aliyu idan ka so wata zan iya mutuwa, ba zan iya sharing dinka da kowa ba, ba zan so wata ma ta so ka ba balle har ka so ta i just can't”
Tausayinta ne ya kama shi sai ya kara natsowa kusa da ita ya kai hannunsa ya rika fuskarta.
“Babu kowa a zuciyata sai ke ke kedai, ba zan taba son wata dabam ba, ko da ba ki da rai ballantana kina raye, kina jin kin kyauta min idan kika kawo ma kanki cewar zan iya son wata yarinya kamar wacan yarinyar? Karamar yarinya kuma yar talakawa yarinyar da ta zo aiki a gidana? Haba Rahma ki rika tunani kamin ki yi abu mana you should trust your husband”
“Tana da kyau amman”
Ta fada tana yawo da idonta a fuskarsa.
“Yes she's pretty amman ba hakan zai saka na so ta ba, taya wai zan so wannan yarinyar ai abunda ba zai taba yiyuwa ba ne, ki ma daina wannan tunanin kar mu samu matsala da ke”
Ya fada yana tuna masa bacin ransa karara, dan har ga Allah da ba matarsa ce Rahma tai masa wannan zargin ba da ba zai dauka ba, shi be ga dalilin daya da zai saka shi son Ataa ba, daga kawai ya nuna tausayinsa sai Rahma ta kasa fahimtarsa, tausayinma da ba a zalince dalilinsu ba da be ga abunda zai saka shi jin tausayin nata ba. Cewar da yai yes tana she's pretty yasa Rahma jin kamar ya ce yes sai na aureta, at least ya yara kyauta ai abunda be taba ba, ko a tv suke kallo be taba kallon wata a gaban idonta ya ce tana da kyau ba, idan ya kama dole ya fada sai dai ita Rahma ya ce tana da kyau, domin kullum cikin yaba kyauta yake, amman a yau yace yes wata bayan ita tana da kyau and ita kanta da take mace ta san Ataa na da masifar kyau balle kuma Aliyu da yake namiji, bata jin nadamar sanin wani a rayuwarta kamar yadda ta ji na sanin Ataa ba, daman tana yawan jin cewar ba a son daukar an aiki kwace miji suke amman bata taba yarda ba sai yau, da tun farko Ataa bata zo aiki gidan ba, da Aliyu be ganta ba, har ta ga Doc Asim ta masa wannan kazafin da zai saka Aliyu ya tausaya mata.
Yana rungume da matarsa har aka kira sallah magariba, sannan ya sake ta yana kallon fuskarta ya ce.
“Zan je masallaci daga can zan mana takeaway okay”
Ta gyada masa kai tana jin zuciyarta na yi mata yawo da wani abu marar dadi. Goshinta ya sumbata da alama sumbantar goshi yana cikin abunda ya fi kaunar yi a jikin mace, sannan ya tashi tsaye ya nufi kofar fita yana takunsa cikin kasaita kamar yadda ya saba, ita kuma ta bishi da kallo har ya fice, sannan ta tashi ta koma gurin windows ta cigaba da hangensa har ya kunna motar aka bude masa gate ya fice. Sallah ce kawai ta zame mata dole, ita a gaggauce tai yi ta kamar wacce ake jira ta dauki guntun veil dinta ta saka ta dauki makullin motarta ta sauka downstairs tana ta sauri kamar zata tashi sama, tun kan ta shiga motar ta fadawa mai gadi cewar ya bude mata gate, tana shiga ta fisgi motar kamar ba daga cikin gida zata fita ba. Arkilla ta nufa so take taje ta labartawa Momy abunda yake shirin faruwa dan ta san Momy bata san Aliyu yana ganin ya zalinci wata yarinya ba.
Ta isa cikin sa'a domin ta isa a lokacin da duka sisters din Aliyu suke falo Momy kuma tana dakinta zaune bayan gama sallah magariba, su kansu sun yi mamakin ganinta a gidan domin ba karamin abu ke kawo ta gidanba, sai idan za su koma Abuja ta zo bankwana ko kuma idan anyi wani biki ko gaisuwa rasuwa ko wani abun dabam. Cikin mutunci suka gaisa da ita dan haka suke daukarta kamar ba matar yayansu ba ko irin wasan nan na matar yaya da kannen miji bata yi da su, wai kar su rainata daman ta san family miji ba son matar dan'uwansu suke ba.
“Momy na nan?”
“Eh tana dakinta”
Rahila ta amsa mata, sai ta nufi dakin da tana gyara veil dinta wai za a hadu da suruka, iyakar kokarin da tai na tara hawaye a idonta ne yadda Momy zata fahimci akwai damuwa a tare da ita, duk da yake a fuskarta kadai ya nuna tana cikin tashin hankali. Da sallama ta shiga tana maida kofar dakin ta rufe, Momy ta amsa mata tana aje wayar da ke hannunta tare da kallonta. Kusa da Momy ta zube zaune ta fashe da kuka, wanda hakan yasa hankalin Momy ta shi sosai.
“Momy kin san Aliyu yana son wata yarinya yar talakawa wacce ta zo aiki gidanmu?”
Jin hakan yasa hankalin Momy kwantawa daman can farko ta dauko wani abun ne na dabam ba wannan ba.
“Yana son wata? Shi ya ce miki yana son ta?”
“Ya ce ba sonta yake ba, wai tausayinta ya ke, wai sanadin mu aka zalince ta, ina tunanin karya take saboda ta san Aliyu baya son ya zalince kowa ne shiyasa ta ce haka, domin Doc Asim ya ce ya bata kudinta, amman Aliyu duk ya bi ya damu da ita har saka a nemo masa ita, Momy ace ya rasa wacce zai damu da ita sai yar talakawa? Ni shi ya komai bata min rai”
Ta fada cikin kuka, Momy tsayawa kallonta tai, tun da take da ita bata taba tunanin cewar barin yau ta shirya taje ta gaishe da surukarta ba amman ta dauko kafafu ta zo ta kawo mata karar danta.
“To shi dan wajen Fulani ce miki yai ba zai taba kara aure ba?”
“Ba shine damuwar ba Momy yar talakawa fa, kaskantaccin mutane”
“Yar talakawa ai ta miki amfani Rahma ba kodar mahaifiyarta ce a jikinki ba? Ko da siyarwa tai ballantana zalintarta akai aka cireta, talaka shi b mutum ba ne da kike kiranta kaskantacciya? Wannan wace irin magana ce?”
Bude baki Rahma tai tana kallon Momy jin kamar maganar bata dame ta ba, a tuninta Momy irin Mommynta ce da bata son talaka wanda jin hakan zai saka ta hana Aliyu kula Ataa amman ga mamakinta sai ta ji wani abun da ba tai zato ba daga gurin Momy.
“Wallahi Momy idan Aliyu ya ce zai so ta zan iya mutuwa”
“To ki shirya mutuwa tun yanzu, domin Aliyu ba zai zauna da ke ke kadai ba, ko dan shi ma ya samu ganin nasa yayan, ko ba ita dole Aliyu zai kara aure ko dan Allah ya ba shi haihuwa, shekara takwas da aure amman har yanzu be haihu ba, ko ba dan haihuwa ba ai namiji ba zai maka alkawarin cewar ba zai kara aure ba ka yarda”
Rahma ta kalli Momy hawaye na sauko mata zuciyarta cike da jin zafin maganarta.
“Haihuwa na Allah ne Momy idan lokaci yai zan haihu, dan ban samu ciki a yanzu ba ba shi yake nufin ba zan haihu ba, komai na Allah ne”
“Shi kuma talaucin ba na Allah ba ne ko? Yarinyar da kike raina wata rana za ki ga tayi arziki kamar ki ko ma ta fiki, kuma bari kiji na fada miki idan ma dan wajen Fulani na yawan fada miki cewar ba zai kara aure ba daga ke ki daina yarda, dan namiji haka yake anjima zai iya ganin wacce tai masa ya canja ra'ayi”
Rahma ta kalli Momy tana ganin ta wulakanta ta ce wai wata rana Ataa zata fi ta, taya ma zata kai kamarta balle har ta fi ta.
“Momy ko dai dan baki san yarinyar ba ne, wata kazama ce marar daraja, taya za ki hada ni da ita? Ni fa matar dan ki ce”
“Da na hada ki da ita na yi sabo kenan? Ya yanzu kika gama fadin cewar haihuwa na Allah ba ne? Shi talaucin da arzikin ba na Allah ba ne? Ke bari na fada miki idan ma baki sani ba, arziki da talauci duka na Allah ne, wani lokacin talaka ma sai ya fika kima da daraja a gurin Allah, ba kwalliya ki ka yi wa Allah yasa aka haiho ki a gidan masu arzikin ba, ita kuma ba wani laifi tai ma Allah yai ta a haka ba”
“Ba mu muka zalince ba Aliyu miyasa ka kasa ganewa? Shi kansa Doc Asim ba zai zalince ba, ai ya fada maka ya bata kudi ita ce take son masa sheri wata kila ma hadin kai ne da ita dan ta bata mishi suna”
Ya san duk yadda zai yi kokarin fahimtar da ita a yanzu ba zata fahimta ba, domin ranta ya bace sosai and ya san wani abu makamancin wannan be taba shiga tsakaninsu ba, ba lallai ne ta karbi abun a zuciyarta ba, musamman a yadda tai masa fahimta baibai,rumgume ta yai ya saka yatsunsa cikin nata. Ita kanta bata taba jin abu ya daki kirjinta ya ratsa zuciyarta yana neman numfashinta ba irin yau, ashe haka kishi yake, ashe haka ko wacce mace take ji idan mijinta na son wata? Bata taba samun kanta a cikin wannan yanayin ba sai yanzu, fashewa tai da wani irin kuka kamar an mata mutuwa shi kuma ya kara matseta a kirjinsa yana shafa bayanta, one of abunda ya tsana is kuka, kukan kuma ya zama shine silar musamman Rahma da baya son abunda ya taba ta. Sakinsa tai tana saka hannunta ta share hawayenta, sai ya mika dukan karfinsa ya rika ta a tare suka rika taka stairs din har ya shiga da ita dakinta bakin gadon suka zauna ita da shi, ta saka duka hannayenta ta rike masa riga hawayen na bin idonta.
“Wallahi Aliyu idan ka so wata zan iya mutuwa, ba zan iya sharing dinka da kowa ba, ba zan so wata ma ta so ka ba balle har ka so ta i just can't”
Tausayinta ne ya kama shi sai ya kara natsowa kusa da ita ya kai hannunsa ya rika fuskarta.
“Babu kowa a zuciyata sai ke ke kedai, ba zan taba son wata dabam ba, ko da ba ki da rai ballantana kina raye, kina jin kin kyauta min idan kika kawo ma kanki cewar zan iya son wata yarinya kamar wacan yarinyar? Karamar yarinya kuma yar talakawa yarinyar da ta zo aiki a gidana? Haba Rahma ki rika tunani kamin ki yi abu mana you should trust your husband”
“Tana da kyau amman”
Ta fada tana yawo da idonta a fuskarsa.
“Yes she's pretty amman ba hakan zai saka na so ta ba, taya wai zan so wannan yarinyar ai abunda ba zai taba yiyuwa ba ne, ki ma daina wannan tunanin kar mu samu matsala da ke”
Ya fada yana tuna masa bacin ransa karara, dan har ga Allah da ba matarsa ce Rahma tai masa wannan zargin ba da ba zai dauka ba, shi be ga dalilin daya da zai saka shi son Ataa ba, daga kawai ya nuna tausayinsa sai Rahma ta kasa fahimtarsa, tausayinma da ba a zalince dalilinsu ba da be ga abunda zai saka shi jin tausayin nata ba. Cewar da yai yes tana she's pretty yasa Rahma jin kamar ya ce yes sai na aureta, at least ya yara kyauta ai abunda be taba ba, ko a tv suke kallo be taba kallon wata a gaban idonta ya ce tana da kyau ba, idan ya kama dole ya fada sai dai ita Rahma ya ce tana da kyau, domin kullum cikin yaba kyauta yake, amman a yau yace yes wata bayan ita tana da kyau and ita kanta da take mace ta san Ataa na da masifar kyau balle kuma Aliyu da yake namiji, bata jin nadamar sanin wani a rayuwarta kamar yadda ta ji na sanin Ataa ba, daman tana yawan jin cewar ba a son daukar an aiki kwace miji suke amman bata taba yarda ba sai yau, da tun farko Ataa bata zo aiki gidan ba, da Aliyu be ganta ba, har ta ga Doc Asim ta masa wannan kazafin da zai saka Aliyu ya tausaya mata.
Yana rungume da matarsa har aka kira sallah magariba, sannan ya sake ta yana kallon fuskarta ya ce.
“Zan je masallaci daga can zan mana takeaway okay”
Ta gyada masa kai tana jin zuciyarta na yi mata yawo da wani abu marar dadi. Goshinta ya sumbata da alama sumbantar goshi yana cikin abunda ya fi kaunar yi a jikin mace, sannan ya tashi tsaye ya nufi kofar fita yana takunsa cikin kasaita kamar yadda ya saba, ita kuma ta bishi da kallo har ya fice, sannan ta tashi ta koma gurin windows ta cigaba da hangensa har ya kunna motar aka bude masa gate ya fice. Sallah ce kawai ta zame mata dole, ita a gaggauce tai yi ta kamar wacce ake jira ta dauki guntun veil dinta ta saka ta dauki makullin motarta ta sauka downstairs tana ta sauri kamar zata tashi sama, tun kan ta shiga motar ta fadawa mai gadi cewar ya bude mata gate, tana shiga ta fisgi motar kamar ba daga cikin gida zata fita ba. Arkilla ta nufa so take taje ta labartawa Momy abunda yake shirin faruwa dan ta san Momy bata san Aliyu yana ganin ya zalinci wata yarinya ba.
Ta isa cikin sa'a domin ta isa a lokacin da duka sisters din Aliyu suke falo Momy kuma tana dakinta zaune bayan gama sallah magariba, su kansu sun yi mamakin ganinta a gidan domin ba karamin abu ke kawo ta gidanba, sai idan za su koma Abuja ta zo bankwana ko kuma idan anyi wani biki ko gaisuwa rasuwa ko wani abun dabam. Cikin mutunci suka gaisa da ita dan haka suke daukarta kamar ba matar yayansu ba ko irin wasan nan na matar yaya da kannen miji bata yi da su, wai kar su rainata daman ta san family miji ba son matar dan'uwansu suke ba.
“Momy na nan?”
“Eh tana dakinta”
Rahila ta amsa mata, sai ta nufi dakin da tana gyara veil dinta wai za a hadu da suruka, iyakar kokarin da tai na tara hawaye a idonta ne yadda Momy zata fahimci akwai damuwa a tare da ita, duk da yake a fuskarta kadai ya nuna tana cikin tashin hankali. Da sallama ta shiga tana maida kofar dakin ta rufe, Momy ta amsa mata tana aje wayar da ke hannunta tare da kallonta. Kusa da Momy ta zube zaune ta fashe da kuka, wanda hakan yasa hankalin Momy ta shi sosai.
“Momy kin san Aliyu yana son wata yarinya yar talakawa wacce ta zo aiki gidanmu?”
Jin hakan yasa hankalin Momy kwantawa daman can farko ta dauko wani abun ne na dabam ba wannan ba.
“Yana son wata? Shi ya ce miki yana son ta?”
“Ya ce ba sonta yake ba, wai tausayinta ya ke, wai sanadin mu aka zalince ta, ina tunanin karya take saboda ta san Aliyu baya son ya zalince kowa ne shiyasa ta ce haka, domin Doc Asim ya ce ya bata kudinta, amman Aliyu duk ya bi ya damu da ita har saka a nemo masa ita, Momy ace ya rasa wacce zai damu da ita sai yar talakawa? Ni shi ya komai bata min rai”
Ta fada cikin kuka, Momy tsayawa kallonta tai, tun da take da ita bata taba tunanin cewar barin yau ta shirya taje ta gaishe da surukarta ba amman ta dauko kafafu ta zo ta kawo mata karar danta.
“To shi dan wajen Fulani ce miki yai ba zai taba kara aure ba?”
“Ba shine damuwar ba Momy yar talakawa fa, kaskantaccin mutane”
“Yar talakawa ai ta miki amfani Rahma ba kodar mahaifiyarta ce a jikinki ba? Ko da siyarwa tai ballantana zalintarta akai aka cireta, talaka shi b mutum ba ne da kike kiranta kaskantacciya? Wannan wace irin magana ce?”
Bude baki Rahma tai tana kallon Momy jin kamar maganar bata dame ta ba, a tuninta Momy irin Mommynta ce da bata son talaka wanda jin hakan zai saka ta hana Aliyu kula Ataa amman ga mamakinta sai ta ji wani abun da ba tai zato ba daga gurin Momy.
“Wallahi Momy idan Aliyu ya ce zai so ta zan iya mutuwa”
“To ki shirya mutuwa tun yanzu, domin Aliyu ba zai zauna da ke ke kadai ba, ko dan shi ma ya samu ganin nasa yayan, ko ba ita dole Aliyu zai kara aure ko dan Allah ya ba shi haihuwa, shekara takwas da aure amman har yanzu be haihu ba, ko ba dan haihuwa ba ai namiji ba zai maka alkawarin cewar ba zai kara aure ba ka yarda”
Rahma ta kalli Momy hawaye na sauko mata zuciyarta cike da jin zafin maganarta.
“Haihuwa na Allah ne Momy idan lokaci yai zan haihu, dan ban samu ciki a yanzu ba ba shi yake nufin ba zan haihu ba, komai na Allah ne”
“Shi kuma talaucin ba na Allah ba ne ko? Yarinyar da kike raina wata rana za ki ga tayi arziki kamar ki ko ma ta fiki, kuma bari kiji na fada miki idan ma dan wajen Fulani na yawan fada miki cewar ba zai kara aure ba daga ke ki daina yarda, dan namiji haka yake anjima zai iya ganin wacce tai masa ya canja ra'ayi”
Rahma ta kalli Momy tana ganin ta wulakanta ta ce wai wata rana Ataa zata fi ta, taya ma zata kai kamarta balle har ta fi ta.
“Momy ko dai dan baki san yarinyar ba ne, wata kazama ce marar daraja, taya za ki hada ni da ita? Ni fa matar dan ki ce”
“Da na hada ki da ita na yi sabo kenan? Ya yanzu kika gama fadin cewar haihuwa na Allah ba ne? Shi talaucin da arzikin ba na Allah ba ne? Ke bari na fada miki idan ma baki sani ba, arziki da talauci duka na Allah ne, wani lokacin talaka ma sai ya fika kima da daraja a gurin Allah, ba kwalliya ki ka yi wa Allah yasa aka haiho ki a gidan masu arzikin ba, ita kuma ba wani laifi tai ma Allah yai ta a haka ba”